Amsoshi

Hausa Language Academic Website

Sunday, 13 January 2019

Da Wasa Ake Gaya Wa Wawa Gaskiya

22:09 0



Sassan adabinmu na baka ba Æ™aramar rawa suka taka ba wajen daidaita muna akalar rayuwa a kowane Æ™arni muka samu kanmu. Lallai, ba don jiya ba, da yau ta yi masassara. YunÆ™urin kyautata rayuwar yau kuwa, gobe ce ake yi wa shimfiÉ—ar maraba. Sarrafa karin maganar “Sabo Turken Wawa” ya zama akalar jan zaren tunanin wannan littafi ya dace. Abin da aka saba da shi an san shi. Abin da aka sani dole an zaune shi. Abin da aka zauna, ya zama abokin rakiya sai a sake jiki, a miÆ™a wuya gare shi, har ya zama raÆ™umin makaho, kai ka gani ba ni ka gani ba. A ganina, burin littafin shi ne, a riÆ™a

Gurbin Ilmi Ga Had’in Kai Da Cigaban Al’umma

21:58 0



Kowace al’umma da ci gaban magabatanta take bugun gaba. Magabata ba su da abin taÆ™ama face alherin da suka shuka na baya na cin moriyarsa. Idan gaba ta yi kyau, ta gyara wa baya hanya nagartacciya. Rashin samun gabaci na gari ke haddasa wa baya doguwar masassara idan ba ta samu kyakkyawar kulawa ba, bakin wuta ya mutu a hannunta. To! Gudun haka ke sa, a koyaushe magabata suka hango baya na Æ™wazo abin yabawa sukan shirya mata gagarumin buki na yi mata madalla irin wannan da muka hallara a yau. A mahangar addini da zamani, babu ci gaban da ya fi samun nagartaccen ilmi da zai ciyar da mai shi da al’ummarsa gaba. NaÆ™alin kafe ilmi a zuciya ya zauna daram! Shi ne ladabi da biyaya ga kogin da aka shawo shi, da masu…..

Hausa Cikin Hausa Martabar Hausawa Da Mai Karatun Hausa

21:52 0


Barazanar da lokaci ke yi wa al’umma ga ci gaban rayuwarsu musamman idan aka kalli mutuwa a faifan nazari, za a ga ba Æ™arami ba ne. Magabata managarta maÉ—aukaka mafifita mahanga nesa, da Æ™yallaro baya, da suka yi wa Hausa aikin a zo a gani an fara Æ™amfarsu a Æ™arninmu. Idan gaba ta fara ba da baya, baya ba ta da sauran kwanciyar hankali. Kasancewar na gaba idon na baya, idan ya faku, na baya ya rasa idon Æ™yallaro gaba. MatuÆ™ar bagiren da sanuwar gaba ta sha ruwa nan ta baya za ta tsoma bakinta. To! Idan ta Æ™i tsoma bakin za a ce da lauje cikin naÉ—i. DanÆ™wairo ya tabbata mana gaba ta riga ta wuce baya ke da saura. Idan haka ne, gaba sunanta gaba, na baya na….

Noma: Igiya Mad’ura Kaya In An Yi Ba Da Kai Ba Su Watse

21:40 0
Halittun da suka mamaye duniyar matane guda biyar ne: Mutane da dabbobi da tsutsaye da kwari da tsirrai. Mutane tsuntsaye da dabbobi da Æ™wari da tsirrai ne abincinsu. Tsuntsaye a kan su suke shawagin biÉ—an abinci su. Dabbobi da Æ™wari da tsuntsaye da tsirrai suke kalaci. Tsuntsaye a kan su suke shawagin biÉ—an abincinsu. Tsirrai da toroson Mutane da dabbobi da tsuntsaye da Æ™wari (da nasu) ke rayar da su. Wanda ya jahilci wannan ya yi wa duniya zuwan kare ga aboki. Wanda ya haÆ™iÆ™ance su bai zuwan sunge duniya ba. Sarrafa rayuwar waÉ—annan gabaÉ—ayansu, su amfani mazauna duniya, yana ga hannun manoma. Ashe idan aka ce ga Æ™ungiyar manoma kowa na cikin ko….

Usama Bn Laden: Gwarzo ko É—an YaÆ™i? (Laluben Ma’aunin Gwarzo a Hangen makaÉ—an Hausa)

16:28 0


MaÆ™asudin wannan bincike shi ne, tantance yadda Bahaushe ke kallon jaruntaka da yadda Bature ke fassara ta’addanci. Takardar ta yi garkuwa da Usama bn Laden ta fuskar yadda duniyar Turai ke kallonsa. An yi Æ™oÆ™arin É—ora gutsattsarin maganganun Turai kan Usama ta fuskar zarginsa, da farautarsa, da cewa da suka yi, sun kashe shi, a ma’aunin awon jaruntaka a Bahaushen hankali. Na yi Æ™oÆ™arin laÉ“ewa ga zantukan mawaÆ™an baka domin su mutane suka fi sauraro, kuma su maganganunsu suka fi naso a zuciyar Bahaushe. Don haka, na gayyato mawaÆ™a fitattu shahararru goma sha É—aya su raka ni a fahinta. An tsinto É—iyan waÆ™a ashirin da huÉ—u daga cikin waÆ™oÆ™insu domin yi wa bayanai nagartaccen turke. An zaÉ“o mawaÆ™an daga rukunin mawaÆ™an sarauta da mawaÆ™an maza da mawaÆ™an sana’a da….

Tubalan Iskoki a Ginin Littafin Ruwan Bagaja

16:13 0



Nazarin hikimomin al’adun Hausawa da harshensu kullum sai Æ™ara bunÆ™asa yake yi saboda irin Æ™oÆ™arin da masana da É—aliban Hausa ke yi na rayar da su. Adabi kuwa, rumbu ne da ake hango rayuwar kowace irin al’umma da iri-iren abubuwan da take cuÉ—anya da su a rayuwarta. Saboda haka, dangantaka tsakanin al’ada da adabi, aba ce mai Æ™arfin gaske, tamkar harshe ne da haÆ™ori. Masana sun tabbatar da cewa al’ummar Hausawa sun daÉ—e suna hulÉ—a da iskoki, kuma hulÉ—ar, ta samo asali ne tun lokacin da suke cikin addininsu na gargajiya. MaÆ™asudin wannan muÆ™ala shi ne hango wani babban gurbi a cikin al’adar Bahaushe, wato yadda iskoki suka mamaye tunanin Bahaushe, har aka wayi gari, da wuya ya faÉ—i, ko ya rubuta, wata fasaha ko hikima, ba tare da ya saka iskoki a ciki ba. Hasali ma, saka iskokin shi ke haskaka fasahar da ya rubuta, kamar yadda littafin Ruwan Bagaja zai tabbatar.