Ticker

6/recent/ticker-posts

Zamani Zo Mu Tafi: Al’adun Hausawa a Duniyar Intanet (Babi Na Biyar)

Citation: Sani, A-U. (2021). Zamani zo mu tafi: Al’adun Hausawa a duniyar intanet. [Kundin digiri na biyu da ba a wallafa ba]. Jami'ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, Nijeriya.

ZAMANI ZO MU TAFI: AL’ADUN HAUSAWA A DUNIYAR INTANET

NA

ABU-UBAIDA SANI
Email: abuubaidasani5@gmail.com ko official@amsoshi.com
Site: www.abu-ubaida.com
WhatsApp: +2348133529736

Zamani Zo Mu Tafi: Al’adun Hausawa a Duniyar Intanet

BABI NA BIYAR
KAMMALAWA

5.0 Taƙaitawa

Samuwar kafafen intanet ya zo da wani juyin-juya-hali a kusan dukkanin al’amuran duniya. Tuni duniya ta karkata kan amfani da intanet domin gudanar da al’amuran yau da kullum. Daga ciki har da abubuwan da suka shafi:

i. Ilimi

ii. Kiwon lafiya

iii. Tattalin arziki

iv. Kasuwanci

v. Shugabanci

vi. Siyasa

Tafiya ta yi tafiya inda duniyar intanet ta kasance wata duniya ta daban da ke buƙatar wakilci. Maganar haka take musamman yayin da aka yi la’akari da Pulatoriyya inda ya nuna gaskiya iri biyu (bayyananniya da ɓoyayyiya). Dole ne a yi hoɓɓasa domin samar da ingantaccen wakilcin al’adun Hausawa a duniyar intanet. Da ma dai Bahaushe na da karin maganar da ke cewa: “Zamani riga,” inda Yunusa, (1989: 40) ya yi nuni cikin tambaya da cewa: “Wato ke nan idan ya zo sai kowa ya ɗauka ya sa a jikinsa?”

Manufar wannan bincike ba ta fita a kadadar nazartar al’adun Hausa a duniyar intanet ba domin gane inda aka fito da wurin da ake yanzu da kuma ƙoƙarin gyaran gobe. Domin cimma manufar ne aka duƙufa kan maƙasudai da suka haɗa da nazartar tsurar al’adun Hausawan cikin duniyar intanet. Bayan nan an nazarci ci gaba da ƙalubalen da kafafen intanet ke fuskanta. Wannan shi zai ba da damar gane tangarɗar da ake samu wajen samar da wakilci na ƙwarai na aladun Hausawa a kafafen. A ƙarƙashin shawarwari kuwa, an mayar da hankali kan zayyano hanyoyi da matakan da ka iya taimakawa wajen bunƙasawa da yayata al’adun Hausa a duniyar intanet.

An yi amfani da hanyar ɗora aiki da kuma ra’i domin cimma manufar wannan bincike. Ko da ma Ojua, (2019: 1) ya nuna cewa ba a faye samun ra’i guda ya wadatar ga binciken da ake gudanarwa a kimiyyar zamantakewa da na mu’amala ba. Karin maganar nan ta “zamani riga” ita ke taimaka wa wannan bincike wajen nuna cewa ya kamata a yi hoɓɓasar samar da wakilcin al’adun Hausawa da bunƙasa su a zamanance. Domin tabbatar da intanet a matsayin duniya mai buƙatar wakilcin aladu kuwa, an yi amfani da ra’in Pulatoriyya.

Masana da manazarta da dama sun gudanar da bincike a ɓangarorin ilimi da suke da dangantaka da wannan bincike. Daga ciki akwai bincike kan  (i) zamani da (ii) al’adun Hausawa da (iii) intanet. Duk da haka, ba a ci karo da wani bincike da ya nazarci al’adun Hausawa a duniyar intanet ba. Lura da haka, an samu hujjar ci gaba da wannan bincike. Idan binciken ya samu cimma nasara, zai kasance mai muhimmanci a ɓangarori daban daban. Zai amfani mahukunta da masana da manazarta da ɗalibai. Baya ga haka, zai kasance mai amfani ga masu gudanar da kafafen intanet na Hausa.

Binciken ya nazarci al’adun Hausawa a farfajiyar duniyar intanet. Al’adun Hausawa da aka ci karo da su sun haɗa da bayyanannu da kuma ɓoyayyu. Cikin bayyanannun al’adu akwai gine-gine da tufafi da wasanni da makamantansu. Ɓoyayyu kuwa sun haɗa da tarihi da halayya da ɗabi’u. Yayin da aka nazarci tasirin intanet kan al’ummar Hausawa da al’adunsu, sai aka tarar da cewa sun kasance hanjin jimina “akwai na ci akwai na zubarwa.” Intanet na da matuƙar amfani. Daga cikin amfaninsa akwai ba da damar sada zumunta da haɓaka Hausa da yayata ta. Yana kuma taimakawa wajen adana al’adun Hausawan. Aibin kafafen intanet ga al’ummar Hausawa sun haɗa da ɓata tarbiyya da ɓata lokaci da samar da kafar damfara da makamantansu.

Wannan bincike ya nazarci ƙalubalen da ke tattare da gudanar da kafafen intanet na Hausa musamman ta ɓangaren bunƙasa aladun Hausawa. Bayan haka, binciken ya nazarci amsoshin da aka tattara yayin hirarraki da masu gudanar da kafafen intanet na Hausa. Bayan duk waɗannan, ya nazarci hanyoyi da matakan da za a iya ɗauka domin bunƙasa aladun Hausawa a duniyar intanet.

5.1 Sakamakon Bincike

Bayan kammala wannan nazari, binciken ya gano abubuwan da suka shafi al’adun Hausawa a duniyar intanet. Abubuwan da wannan bincike ya gano su ne kamar haka:

1. Wannan bincike ya tabbatar da cewa, babu wani ɓangaren rayuwa a yau da zai iya ci gaba ba tare da an haɗa da intanet ba. Ko da addini da ake kallon an fara shi shekaru aru-aru kafin ɓullowar fasahar intanet, a yau ba ya ci gaba yadda ya kamata har sai an haɗa da intanet. Misali, wa’azuzzukan malaman addini na zagayawa matuƙa yayin da aka yi amfani da intanet. Wannan dalili ne ma ya sa Clement, (2020: 1) yake da raayin cewa, a yau ba za a iya kwatanta duniya ba tare da intanet ba. Maana dai, ba a san ma yaya duniya za ta kasance ba idan aka ce babu intanet a yau.

2. Idan har ana son ci gaban al’adun Hausawa da dauwamarsu cikin inganci, dole a auri duniyar intanet. Hakan ne zai ba da damar samar da wakilci mai inganci. Wannan ya yi daidai da faɗin Bahaushe na “zamani riga.” Bahaushe ya ƙarfafa wannan batu inda yake cewa zamani abokin tafiya. Masana da manazarta da ɗaliban Hausa suna mazaunin jakadun Hausa ne a duniyar zahiri. A tunani irin na Pulatoriyya, wannan wakilci ba zai cika yadda ya kamata ba har sai an samu kwatankacinsa a duniyar intanet.

3. Kafafen intanet na da matuƙar tasiri kan alumma da aladunsu. Masu ziyartar kafafen intanet na tasirantuwa daga rubuce-rubuce da bidiyoyi da odiyoyi da ake ɗorawa. A haka al’umma ke iya tasirantuwa da ɗaukar halaye da ɗabi’u baƙi.

4. Al’adun Hausawa tuni suka fara mamaye duniyar intanet. Kafafen intanet na Hausa ƙalilan ne yayin da aka kwatanta su da adadin ɗaukacin kafafen intanet da ake da su a duniya. Duk da haka, da zarar an bincika wani abu ta Hausa (ta amfani da injunan nema), sakamakon da ke bayyana na Hausa ne. Bugu da ƙari, kafafen intanet da za a ci karo da su na Hausa ne. A bisa haka, idan aka inganta kafafen intanet na Hausa ta ɓangaren ɗora ingantattun bayanai, lallai kwalliya za ta biya kuɗin sabulu. A babi na huɗu ƙarƙashin 4.1 an bayyana cewa kafafen intanet na Hausa sun mamaye kusan dukkanin ɓangarorin rayuwa. Akwai kafafe da suka shafi kimiyya da fasaha da waɗanda suka shafi ilimi da koyarwa da kasuwanci da al’ada da zamantakewa makamantansu.

5. Ɗumbin amfanin da intanet yake da shi, bai hana shi samun aibi ba. A ƙarƙashin 3.3 da ke babi na uku an bayyana wasu alfanun intanet. An bayyana aibinsa kuma a ƙarƙashin 3.4 da ke babi na uku.

6. Binciken ya gano cewa, akwai kafafen intanet na Hausa da ke barazana ga al’adun Hausawa. Hakan na faruwa ne kasancewar kafafen na ɗauke da kura-kurai barkatai tare da saɓa wa al’ada da addinin Bahaushe. Daga cikin koma bayan da kafafen intanet na Hausa suke ɗauke da shi akwai:

i. Suna cin karo da al’adun Hausawa

ii. Suna ɗauke da kurakurai barkatai

iii. Sukan ƙunshi bayanai marasa inganci

7. Daga ƙarshe, binciken ya fahimci cewa kafafen intanet na Hausa suna fuskantar ƙalubale matuƙa. A taƙaice, ƙalubalen sun shafi:

a. Muhallin ƙasar Hausa da ke ɗauke da ƙalubalen wutar lantarki da sabis na intanet

b. Ƙarancin tallafi da ƙarfafa guiwa daga ɓangaren masana da hukumomi

c. Yanayin tsauri da wuyar koyo da harkar intanet ke da shi

d. Ƙin karɓar sauye-sauyen rayuwa ga waɗanda abin ya shafa

e. Rashin injunan gyaran rubutun Hausa wanda hakan ke mazaunin ƙalubale ga rubuta ingantacciyar Hausa bisa tsarin ƙaidojin rubutu

f. Rashin takamaimai hanyar rubuta baƙaƙe masu ƙugiya cikin sauƙi

g. Ƙarancin ilimin da Hausawa ke da shi kan tsarin intanet da amfani da shi

5.2 Shawarwari

A ƙarƙashin 5.2 an bayyana sakamakon wannan bincike. An zayyano sakamakon da aka tattara daga alƙaluman wannan bincike. A wannan bagire kuma (5.3) za a mayar da hankali wajen ba da shawarwari. Sun kasance shawarwari ga matsaloli da ƙalubale da binciken ya gano waɗanda ke dabaibaye da al’amuran al’adun Hausawa a duniyar intanet.

1. Ya kamata a samu wata haɗaka tsakanin masana harkar kwamfuta da cibiyoyi da sasukan nazarin Hausa domin tanadi mai kyau na tunkarar zamani ta fuskar intanet. Wannan zai ba da damar buɗe ingantattun kafafen intanet na Hausa waɗanda za su yi wakilcin ƙwarai ga aladun Hausawa. Kowa a cikin tafiyar zai ba da gudummuwa irin tasa. Masana intanet za su duƙufa wajen gina nagartattun kafafen intanet na Hausa. Masana da manazarta da ɗaliban ilimi za su ci gaba da gudanar da bincike da za a riƙa sabunta bayanan kafafen a-kai-a-kai. Cibiyoyi da sasukan nazarin Hausa kuwa za su tallafa ta ɓangaren samar da abubuwan buƙata da suka shafi kuɗin gudanar da kafafen.

2. Ya kamata kowace cibiya da sashen nazarin Hausa ta mallaki kafar intanet na kanta. A cikin kafar, ta riƙa gudanar da alamuranta tare da ɗora nau’ukan bincike da mambobinta ke gudanarwa. Abubuwan da cibiyoyi da sasukan za su riƙa ɗorawa na iya haɗawa da:

i. Sunaye da adireshin mambobi: Hakan zai ba wa masu ziyartar shafin damar tura tambayoyi ga waɗanda suka dace. Har ila yau zai ba da dama ga masu ziyartar shafin na kusa da na nesa tuntuɓar masu gudanar da cibiyoyin yayin da suke buƙatar haɗin guiwa kan wani bincike da za su gabatar.

ii. Bayani a kan cibiya ko sashe: Wannan zai taimaka wa masu ziyartar kafafen na kusa da na nesa. Yayin da suke neman waɗanda za su haɗa guiwa da su wurin bincike, kai tsaye za su tuntuɓi masu kafar. Bayan haka, zai iya sanya sha’awa ga masu ziyarar kafafen na kusa da na nesa. Bayan karanta bayanai dangane da sashe, suna iya zuwa domin karatu a sashen.

iii. Sanya bincike ko wani ɓangare na bincike da aka gudanar: Wannan zai taimaka wajen haɓaka Hausawa da yayata ta.

3. Ba za a iya hana matasa da yaran Hausawa ta’ammuli da duniyar intanet ba. Haka kuma, ba za a iya hana su tasirantuwa da abubuwan da suke cin karo da su a intanet ɗin ba. A bisa wannan dalili, mafita guda ta rage ga Hausawa. Mafitar ita ce buɗe kafafen intanet na Hausa tare da inganta su. Yayin da ya kasance ‘ya’yan Hausawa na da zaɓi, a ƙalla za a samu rangwame.

4. Kasancewar an samu kafafen intanet na Hausa masu ƙarfin tasiri a duniyar intanet, abin da ya saura shi ne ba wa masu gudanar da su ƙarfin guiwa. Bayan haka, yana da kyau a ci gaba da buɗe kafafen domin a samu inganci a ɓangaren kowace al’ada. A ƙarƙashin 4.1 da ke babi na huɗu, an kawo tsokacin Seibert, (2017: 1) da ke kan kafar intanet ɗinsa ta Hausa. Ya bayyana cewa, ya dena sabunta bayanan kafar ne samboda an samu yawaitar kafafen intanet na Hausa. Wannan na nuna cewa, idan aka samu wadatar kafafen intanet na Hausa masu inganci, za su nashe taron yu-yu-yun da ake da su, har a daina jin ɗuriyarsu baki ɗaya.

5. La’akari da amfani da kuma aibin kafafen sada zumunta, dabara ta rage ga mai shiga rijiya. Mahukunta da iyaye da masana da manazartar ya kamata su yi aikin haɗin guiwa a wannan ɓangare. Kowa ya yi bakin ƙoƙarinsa wajen tabbatar da yara masu tasowa suna amfana da alfanun intanet tare da guje wa aibinsa.

6. Kamar yadda aka bayyana a ƙarƙashin lamba ta 4 da ke 5.3, samar da ingantattun kafafen intanet ne kawai zai ba da damar kawo gyara a duniyar intanet. Ta wannan hanyar ne za a samu kyakkyawan wakilcin aladun Hausawa.

7. Haƙiƙa ƙalubalen da kafafen intanet na Hausa ke fuskanta abin dubawa ne. Domin samun sassauci dangane da waɗannan ƙalubale, wannan bincike ya ba da shawarwari kamar haka:

a. A samar da muhalli na musamman ga masu gudanar da kafafen intanet na Hausa. Misali, a samar da zaɓin da za a iya amfani da shi yayin da babu wuta (janareto). Haka kuma, a samar musu sabis ɗin intanet mai nagarta. Wannan na iya kasance tsare-tsaren da cibiyoyi da sasukan nazarin harsunan Nijeriya za su gudanar.

b. Kamar yadda aka bayyana a lamba ta 1 a ƙarƙashin 5.3, a samu haɗin guiwa tsakanin cibiyoyi da sasukan nazarin Hausa domin tallafa wa harkar intanet. Ta haka ne za a bunƙasa lamarin aladun Husawa a duniyar intanet.

c. A riƙa samar da darrusa da horarwa da tarukan ƙarawa juna sani na musamman (ƙarƙashin kulawar mahukunta da aka zayyana a lamba ta 1 ƙarƙashin 5.3). Taruka da darrusa da horarwar su kasance na musamman kuma keɓaɓɓu ga waɗanda suke da rigayayyen sani kan harkar kwamfuta tare da waɗanda suka da sha’awar shiga harkar domin ba da gudummuwa.

d. Ya kamata a samu wani yunƙuri da ya shafi rubuce-rubuce da tarukan ƙarawa juna sani da za su faɗakar dangane da amfanin intanet a yau. Dole ne al’umma (musamman malamai da ɗaliban Hausa) su koyi ta’ammuli da intanet. Amfani da intanet ya kasance dole a yau. Idan Hausawa ba su yi ba, to za a musu. Yayin da wasu suka yi kuwa, gurɓatar haƙiƙanin wakilci tabbas ne. Bahaushe ya yi gaskiya da ya ce: Sai bango ya tsage kadangare ke samun mafaka. Sai a hana bangon tsagewa sannan a liƙe tsagon da ya soma aukuwa. Maana, a samar da kafafen intanet na Hausa tare da toshe komaɗar da kafafen yanzu suka fara samarwa dangane da illoli da koma-bayansu ga al’adun Hausawa.

e. Muhammad Bello (Mai Kafar Makarantar Hausa) shi ne sanannen mutum guda da ya yi hoɓɓasar samar da injin gyaran rubutu na Hausa. Farfesa Abdalla Uba Adamu kuwa shi ne ya samar da tsarin rubuta baƙaƙe masu ƙugiya na Rabiat da Abdalla. Yana da kyau a ƙarfafa wa ire-irensu guiwa domin samun ingantattun injunan gyaran rubutu.

f. A yanzu an kawo ƙarshen matsalar baƙaƙe masu ƙugiya tun bayan da kamfanin Microsoft ya samar da baƙaƙe masu ƙugiya na gama gari (kamar yadda aka bayyana a ƙarƙashin 3.3.7 da ke babi na uku). Abin da ya rage yansu shi ne a yaya waɗannan baƙaƙe tare da bayani game da yadda ake amfani da su.

g. Ya kamata a bi hanyoyin da suka dace na faɗakar da Hausawa game da amfani da intanet. Waɗannan hanyoyin sun haɗa da shirye-shirye a gidajen rediyo da waƙoƙi da kuma tarukan ƙara wa juna sani.

MANAZARTA

Abdullahi, I. S. S. (2008). “Jiya ba Yau ba: Waiwaye a Kan Al’adun Matakan Rayuwar Maguzawa na Aure da Haihuwa da Mutuwa.” Kundin digiri na uku wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Abraham, R. C. (1962). Dictionary of the Hausa Language. London: Hodder Sydney.

Abu, M. (1985). “Al’adun Aure da Canje-canjensu a Katsina.” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Abubakar, A. S. (2007). “Dangantakar Intanet da Harkokin Rayuwa”. Takardar da aka buga a cikin jaridar Aminiya ta ɗaya (1) ga watan Maris.

Abubakar, H. S. (2020). “Ba’amurkiya Daga California ta Biyo Saurayinta Zuwa Kano.” An ɗauko ranar 20 ga watar Fabarairu na shekarar 2020 daga: https://freedomradionig.com/?p=17928.

Abubakar, S. da Ladan, H. (2019). “Dusashewar Wasannin Gargajiya A Kasar Yabo (2).” An ɗauko ranar 19 ga watan Afirilu, shekarar 2020 daga: https://www.amsoshi.com/2018/01/dusashewar-wasannin-gargajiya-kasar_31.html.

Abubakar, S. Y. (1997). "Bori A Zariya." Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijiriya, Jami'ar Ahmadu Bello, Zariya.

Adamu, A. U. (2000). “Hausa Language and Culture on the Internet.” An article published in the Weekly Trust of 20th November.

Adamu, A. U. (2004). “Hausa Information and Communication (ICTs).” A paper presented at the 6th International Conference on Studies in Hausa Language, Literature and Culture at Beyero University, Kano.

Adamu, J.S. (2013). Gudummuwar Shirye-Shiryen Gidan Radiyon Muryar Jama’a, Kano Wajen Kare Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa: Nazari a Kan ‘Aiki Da Hankali’ Da ‘Tamburan Kano.’ In Bunza, A.M. et al (eds). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 645-660. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Adamu, M.T. (1998). Asalin Magungunan Hausawa da Ire-Irensu. Kano: Ɗansarkin Kura Publishers Ltd.

Adamu, S. (2020). “Talla Cikin Siddabaru.” An ɗauko ranar 20 ga watan Afirilu, shekarar 2020 daga: https://www.amsoshi.com/2019/12/talla-cikin-siddabaru.html.

Ado, A. (2017). Ra’o’in Bincike Kan Al’adun Hausawa. Katsina: Kanki Classical Media Enterprises.

Ahmad, A.A. (2013). Tasirin Wayar Salula a Kan Tarbiyyar ‘Ya’yan Hausawa. In Bunza, A.M. da wasu (editoci). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 743-758. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Ahmed, I. A. (2020). “Comrade AAT ya yi Tattaki Daga Katsina Domin ta ya Kwankwasiyya Alhinin Faɗuwa Zaɓe.” An ɗauko ranar 21 ga watan Afirilu, shekarar 2020 daga: https://qalubale.news.blog/2020/02/09/comrade-aat-yayi-tattaki-daga-katsina-domin-ta-ya-kwankwasiyya-alhinin-faduwa-zabe/.

Aƙibu, G. (2001). “Fassarar  Kalmomi Ɗari (100) na Na’ura Mai Ƙwaƙwalwa Tare da Bayaninsu.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Akindele, F. & Adegbite, W. (1999). The Sociology and Politics of English in Nigeria: An Introduction. Ife: O.A.U. Press Limited.

Akodu, A. (1985). “A Comparative Study of the Traditional and the Contemporary Arts of the Maguzawa of Kaduna and Kano States. Unpublished Ph. D. Thesis, Zaria: Ahmadu Bello University.

Almajir, T. S. (2008). “Hausa da Sadarwar Intanet.” A cikin Harsunan Nijeriya, Vol. XXI. Kano: Northwestern University Press.

Almajir, T. S. (2009). “Tasirin Zamani a Kan Rayuwar Hausawa Matasa a Kano.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Jami’ar Bayero, Kano.

Amfani, A. H. (2010). “Hausa Internet Terms.” A paper presented at School of Oriental and African Studies - University College London/Department of Nigerian Languages, Usmanu Danfodiyo University, Sokoto, Nigeria.

Aminu, N. (2015). “Baƙin Dole: Nason Al’adun Turawa ga Al’adun Hausawa a Lardin Sakkwato da Gwandu da Argungu, 1903-2010.” Kundin digiri na Uku wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Argungu, D. M. (2016). “Language and National Development in Nigeria – The Unfinished Business.” A lead paper presented at the 1st National Conference on the Role of  Language, History and Religion in the Development, Integration and Security in Nigeria, held in Usmanu Danfodiyo University, Sokoto, Nigeria.

Armstrong, M. (2019). “How Many Websites Are There?” Retrieved on 20th February 2020 from: https://www.statista.com/chart/19058/how-many-websites-are-there/.

Ashafa, A. M. (2016). “Language/Ethnicity, Religion and National Security: The Missing Links in National Development and Nation Building.” A lead paper presented at the 1st National Conference on the Role of Language, History and Religion in the Development, Integration and Security in Nigeria, held in Usmanu Danfodiyo University, Sokoto, Nigeria.

Ashiru, H. M. (2012). “Gudummuwar Intanet ga Bunƙasa Adabin Hausa.” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Ummaru Musa ‘Yar’aduwa, Katsina.

Augustyn, A. et al (2020). Platonic Criticism. In Encyclopedia Britannica. Retrieved on 17th March 2020 from: https://www.britannica.com/art/Platonic-criticism.

Ayad, A. (2008). Healing Body and Soul. Saudi Arabia: International Islamic Publishing House.

Babajo, S. A. (2001). “Yaji da Biko a Auren Bahaushe.” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Bamgbose, A. (1991). Language and the Nation: The Language Question in Sub-Saharan Africa. Edinburgh: Edinburgh University Press.

Bargery, G. P. (1933). A Hausa-English Dictionary. London: Oxford University Press.

Bargery, G.P. (1934). Hausa-English Dictionary, English-Hausa Vocabulary. London: Oxford University Press.

Barlow, J. P., S. Birkets, K. Kelly and M. Slouka (1995). “What Are We Doing On-Line?” In Harper's. 291: 35-46.

Baruah, T. D. (2012). “Effectiveness of Social Media as a Tool of Communication and its Potential for Technology Enabled Connections: A Micro-Level Study.” In International Journal of Scientific and Research Publications. Volume 2, Issue 5, Pp. 1-10, ISSN 2250-3153.

Basu, S. (2019). What are the 5 main network Topologies? Explained with Diagram. Retrieved on 9th August, 2021 from: https://www.how2shout.com/what-is/what-are-the-5-main-network-topologies-explained-with-diagram.html.

Bourgeois, S. (2016). 11 Types of Networks Explained: VPN, LAN & More. Retrieved from: https://www.belden.com/blogs/network-types.

Bryson, J. (2019). “The Cambridge Platonists in Henry Fielding’s Christian Platonic History of Tom Jones.” Retrieved on 6th March 2020 from: https://cprg.hypotheses.org/.

Bunza A.M (2006). Gadon Feɗe Al’ada. Lagos: Tiwal Nigerian Limited.

Bunza, A. M. (1990). “Hayaki Fid da na Kogo.” Kundin digri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Bunza, A. M. (2004). “Magana da Iskoki ta Bakin Dokinsu.” Muƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani karo na 6 kan Nazarin Harshe da Adabi da Al’adun Hausawa. Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeria, Jami’ar Bayero Kano.

Bunza, A. M. (2005). “Boruƙiyyah: Tazarar Bori da Ruƙiyya a Idon Manazarta.” Takardar da aka gabatar a taron tattaunawa da ƙara wa juna sani na musamman da Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya Jami'ar Bayaro, Kano ta shirya kan "Bori" da "Ruƙiyya".

Bunza, A. M. (2014). “Matakan Ƙyallaro Asalin Bahaushe: (Ruwa Na Ƙasa Sai Ga Wanda Bai Tona Ba).” Takardar jagora da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa-da-ƙasa na farko a Jami’ar Jihar Kaduna, ƙarƙashin inuwar Hausa Studies Scholars Association, kulawar Department of Nigerian Languages and Linguistics bisa taken The Hausa People, Language and History: Past, Present and Future ranar 15th 17th Disamba 2014 a Arewa House, Kaduna.

Bunza, A. M. (2019). “Hausa da Hausawa a Duniyar Кarni na Ashirin da Ɗaya: (Amsa Kiran Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) Ga Ranar Hausa Ta Duniya Litinin 26 Ogusta, (2019).” Takardar da aka gabatar a bikin Ranar Hausa ta duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya ta keɓe a ranar Litinin 26 ga Ogusta, 2019. An gudanar da taron a Jami’ar Bayero Kano.

Bunza, A. M. (2019). “Ƙwarya a Farfajiyar Adabi da Aladun Bahaushe.” A cikin East African Scholars Journal of Education, Humanities and Literature, Mujallad na 2, Fitowa na 12, Shafi na 720-727.  ISSN  2617-443X.

Bunza, A. M. (2020). “Tsakanin Kabi Da Sakkwato: Kar Ta San Kar Aljani Ya Taki Wuta (Daular Kabi A Ma’aunin Bakandamiyar Buda Ɗantanoma).” An ɗauko ranar 19 ga watan Afirilu, shekarar 2020 daga: https://www.amsoshi.com/2018/12/tsakanin-kabi-da-sakkwato-kar-ta-san.html.

Bunza, A.M. (1995). “Magungunan Hausa a Rubuce.” Kundin digiri na uku wanda aka gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Bunza, D. B. (2013). “Zama da Maɗaukin Kanwa Ke Sa Farin Kai: Nason Baƙin Al’adu Cikin Al’adun Auren Hausawa.” Muƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa a Sashen Harusnan Nijeriya, Jami’ar Ummaru Musa ‘Yar’aduwa.

 

Bunza, U. A. (2008). “Jaridu da Mujallun Hasua: Samuwarsu da Rashin Tabbatuwarsu Daga 1986-2006: Nazari Daga Tarihin Adabin Hausa.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Bunza, U. A. da Atuwo, A. A. (2015). “Adabin Wayo a Tantance Bahaushen Asali (Duba Cikin Adabin Abubakar Imam).” Maƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa da ƙasa na Farko Kan ‘Al’ummar Hausawa, Harshe Da Tarihi: Jiya, Yau Da Kuma Gobe’ da  Ƙungiyar Malamai Manazarta Hausa Kaduna 2014 ta shirya wanda za a yi a Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya da Ilimin Harsunan, Jami’ar Jihar Kaduna, Kaduna.

Clement, J. (2019). Daily active users of WhatsApp Status 2019. Retrieved on 3rd January, 2020 from: https://www.statista.com/statistics/730306/whatsapp-status-dau/.

Climent, J. (2020). “Worldwide digital population as of January 2020.” Retrieved on 20th February 2020 from https://www.statista.com/statistics/ 617136/digital-population-worldwide/.

Dabo, D. (2019). “Shawara a Kan Turanci ga Mawaƙan Hausa HipHop Masu Tasowa – Daga Dabo Daprof.” An ɗauko ranar 21 ga watan Afirilu, shekarar 2020 daga: http://www.hausatop.com/shawara-akan-turanci-ga-mawakan-hausa-hiphop-masu-tasowa-daga-dabo-daprof/.

Dan Zubair, (2017). “Muhimmancin Sunayen Hausawa na Gargajiya a Gargajiyar Bahaushe.” An ɗauko ranar 18 ga watar Afirilu, shekarar 2020 daga: https://gobirmob.com/ha/matsayin-sunayen-hausawa-na-gargajiya-a-gargajiyarsu/.

Danladi, S. S. (2013). “Language Policy: Nigeria and the Role of English Language in the 21st Century.” In European Scientific Journal June 2013 edition vol.9, No.17 ISSN: Pp: 1857 – 7881.

Ɗanyaya, M. B. (2007). Karin Maganar Hausawa. Sokoto: Makarantar Hausa.

Dordal, P.L. (2021). An Introduction to Computer Networks (Release 2.0.4). Retrieved on 12th August 2021 from: http://intronetworks.cs.luc.edu/ current2/ComputerNetworks.pdf.

Faruk, S. I. (2011). “Tasirin Aikin Gwamnati a Kan Matan Auren Hausawa a Jihar Katsina.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Fraenkel, J. R. & Wallen, N. E. (2003). How to Design and Evaluate Research in Education. Fifth ed. New York: McGraw-Hill.

Funtuwa, A. I. da Gusau, S. M. (2010). Al’adun da Ɗabi’un Hausawa da Fulani. Kaduna: El-Abbas Printers and Media Concept.

Furniss, G. (1996). Language, literature and Hausa popular culture. London: Edinburgh.

Gada, N. M. (2014). “Kutsen Baƙin Al’adu Cikin Hidimar Aure a Sakkwato.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Galadanci, M. K. M da wasu (1990). Hausa: Don Ƙananan Makarantun Sakandare 1. Lagos: Longman Nigeria Plc.

Garba, S.A. (2013). Auren Zoben Bahaushe da Rediyo a Goshin Ƙarni na 21: (Gidan Rediyon Rahama 97.3 FM da Ginin Tariyya a Mahangar Alada). In Bunza, A.M. da wasu (editoci). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 707-722. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Gerf, V. G. (2004). On the Evolution of Internet Technologies. In Proceedings of the IEEE, VOL. 92, NO. 9. DOI: 10.1109/JPROC.2004.832974.

Gerson, L. (2013). “Was Plato a Platonist?” In From Plato to Platonism (pp. 3-33). Cornell University Press. Retrieved on 7th March 2020, from: www.jstor.org/stable/10.7591/j.ctt32b4gd.5.

Gerson, L. (ND). “What is Platonism?” Retrieved on 5th March, 2020 from: https://www.researchgate.net/publication/236825147_What_is_Platonism.

Gerson, P. L. (2005). “What is Platonism?” In Journal of the History of Philosophy , Vol. 42, Pp: 253-257. DOI: 10.1353/hph.2005.0136.

 Getso, H.A. (2013). Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa a Wannan Zamni: Rawar Da Kafofin Yaɗa Labarai Suke Takawa Wajen Bunƙasa Ko Ruguza Al’adun Hausawa a Yau. In Bunza, A.M. et al (eds). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 607-618. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Gobir, Y. A. & Sani, A-U. (2017). The Jinn, Women Vulnerabilities and The Act of Healings in The Hausa Communities Of 21st Century. In IOSR Journal of Humanities and Social Science (IOSR-JHSS), Volume 23, Issue 1, ver. 5 (January. 2018) PP 67-73 e-ISSN: 2279-0837, p-ISSN: 2279-0845.

Gobir, Y. A. & Sani, A-U. (2018). Traces of Supernatural in Hausa Oral Songs: A Special Reference to Dr. Mamman Shata. In International Journal of Recent Advances in Multidisciplinary Research, vol. 05, Issue 04, pp 3755-3760. ISSN: 2350-0743.

Gobir, Y. A. & Sani, A-U. (2019). “Witchcraft in the Light of Hausa Culture and Religion.” In Academic Journal of Current Research. Vol. 6, No.12; Pp., 23-30. ISSN (2343–403X); p–ISSN 3244–5621. Available at: http://cird.online/AJCR/wp-content/uploads/2020/01/CIRD-AJCR-19-12033-final.pdf.

Gobir, Y. A. (2002) “Iskoki a Idon ‘Yan bori da Masu Ruƙiyya.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usamu Danfodiyo, Sakkwato.

Gobir, Y. A. (2012). “Tasirin Iskoki ga Cutuka da Magungunan Hausawa.” Kundin digiri na uku wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Gobir, Y. A. (2012). “Tasirin Iskoki ga Cututtuka da Magungunan Hausawa.” Kundin digiri na uku wanda aka gabatar a Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Guiɓi, I. I. (2006). “Modern Information Technology: An Assessment of the Role of Hausa on the Internet.” A masters dissertation submitted to the Department of African Languges and Cultures, Ahmdu Bello Uiversity, Zariya.

Guibi, I.I. da Bakori A.D. (2013). Rawar da Kafafen Yaɗa Labarai Suke Takawa Wajen Ruguza Al’adun Hausawa a Yau. In Bunza, A.M. et al (eds). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 619-628. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Gusau, G. U. (2012). Bukukuwan Hausawa. Gusau: Ol-faith Prints.

Gusau, S. M. (2010). “Al’adun Hausawa a Taƙaice.” A cikin Funtua, A. I. da Gusau, S. M. (editoci) Al’adu da Ɗabi’un Hausawa da Fulani. Kaduna: El-Abbas Printers and Media Concepts.

Gusau, U. G. (2012). Bukukuwan Hauswa. Gusau: Ol-Faith Prints.

Gwarjo, Y. T. da wasu (2005). Aure a Jihar Katsina. London: Oxford University Press.

Hassan, B. Y. (2013). “Nason Baƙin Al’adu Kan Al’adun Aure da Haihuwa da Mutuwa na Hausawa.” Muƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa a Sashen Harusnan Nijeriya, Jami’ar Ummaru Musa ‘Yar’aduwa.

Ibrahim, M. S. (1982). “Dangantakar Al’ada da Addini Tasirin Musulunci kan Rayuwar Hausawa ta Gargajiya.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Ibrahim, M. S. (1985). “Auren Hausawa: Gargajiya Da Musulunci.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Ibrahim, M. S. (1985). Auren Hausawa: Gargajiya da Musulunci. Kano: Shoguna Commercial Press.

Ibrahim, S. M. (1981). Auren Hausawa. Zaria: Ahmadu Bello University Press.

Isah, S. (2013). Gudummuwar Gidan Rediyon Companion FM 104.5 Mhz Katsina Wajen Bunƙasa Aladun Hausawa. In Bunza, A.M. da wasu (editoci). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 699-706. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Jayasekara, A. H. D. (2015). “Facebook Users and Undergraduates (Specially Reference to Selected Universities in Sri Lanka).” In International Journal of Scientific Research and Innovative Technology, Vol.: 2, No. 5 , Pp. 78-85. ISSN: 2313-3759.

John, G. W. (1998). “A Definition of Theory: Research Guidelines for Different Theory-Building Research Methods in Operations Management.” In Journal of Operations Management, Vol.: 16 Pp: 361–385. Retrieved on 22nd February 2020 from: http://citeseerx.ist.psu.edu/viewdoc/download?doi=10.1.1.470.4555&rep=rep1&type=pdf.

Kaina, H.M. (2019). Matar Shugaban Najeriya Ta Maida Martani Akan Jita Jitar Mijinta Zai Sake Aure. An ɗauko ranar 24 ga watan Disamba, shekarar 2021 daga: https://www.voahausa.com/a/matar-shugaban-najeriya-ta-maida-martani-akan-jita-jitar-mijinta-zai-sake-aure/5122106.html.

Keary T. (2021). Network Topology: 6 Network Topologies Explained & Compared. Retrieved on 12 August 2021 from: https://www.comparitech.com/net-admin/network-topologies-advantages-disadvantages/.

Kiyawa, H.A. (2013). Tsokaci a Kan Wasu Matsalolin Finafinan Hausa Wajen Ɓata Tarbiyya. In Bunza, A.M. et al (eds). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 661-668. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Kleinrock, L. (2010). “An Early History of the Internet.” In Schwartz, M. (ed). History of Communications. IEEE Communications Magazine August, Issue: August 2020.

Korkmaz, M., Celebi, N. & Yucel, A. S. (2014). “Practical Review of the Place of Social Networks in our Daily Life and Their Effect on Today’s Youth.” In International Journal of Academic Research Part B; 6(1), Pp. 250-261. DOI: 10.7813/2075-4124.2014/6-1/B.35.

Krejcie, R. V., & Morgan, D. W. (1970). “Determining Sample Size for Research Activities.” In Educational and Psychological Measurement, Vol.: 30, Issue: 3, Pp: 607–610. https://doi.org/10.1177/001316447003000308.

Leiner, B. M. et al (1997). “The Past and Future History of the Internet: The Science of the Future Technology.” In Communcations of the ACM, Vol.: 40, No. 2, Pp. 102-108.

Magaji, F. Y. (2018). “Tasirin Zamananci a Kan Zumuncin Al’ummar Hausawa.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Mahmud, A. M. (1997). Hanyoyin Gane Sihiri da Warware Shi. Kano: Burji Publishers & Co.

Mai’aduwa, A.A. (2013). Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa a Yau: Nazari a Kan Finafinan Hausa. In Bunza, A.M. da wasu (editoci). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 723-730. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Maikwari, H. U. (2020). “Wasu Al’adun Hausawa Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a matakin jarabawa ta cikin gida a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Makuwana, A. A. (2011). “Yaɗuwar Harshen Hausa Cikin Intanet.” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Malumfashi, I. & Nahuce, M. I. (2014). Kamusun Karin Maganar Hausa. Kaduna: Garkuwa Media Services.

McCombes, S. (2020). “How to Write a Literature Review.” Retrieved on 26th March 2020 from: https://www.scribbr.com/dissertation/literature-review/.

Meinwald, C. C. (2020). “Plato (Greek Philosopher).” In Encyclopedia Britannica. Retrieved on 17th March 2020 from: https://www.britannica.com/biography/Plato.

Morakinyo, O. (2015). “Language Policy in Nigeria: Problems, Prospects and Perspectives.” In International Journal of Humanities and Social Science Vol.: 5, No. 9. Retrieved on 17th February 2020 from: www.ijhssnet.com/journals/Vol_5.

Muhammad, Ɗ. (2011). “Hausa a Duniyar Yau: Tasirin Game Duniya Kan Harshen Hausa.” A cikin Yalwa, L. Ɗ. da wasu (editoci). Studies in Hausa Langauge Literature and Culture – Proceedings of the Sixth Hausa International Conference – Center for the Study of Nigerian Languages, Bayero University, Kano, 15th – 17th December 2004. Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.

Muhammad, T. A. (1998). Aure Da Buki a Ƙasar Hausa. Kano: Ɗan Sarkin Kura Publishers Ltd.

Mukoshy, J. I. (2015). “Keɓaɓɓun Kalmomin Intanet da Amfaninsu a Nazarin Hausa.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Mukoshy, J. I. (2016). “Keɓaɓɓun Kalmomin Intanet da Amfaninsu ga Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasa.” Muƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani kan Matsayin Harshe da Tarihi da Addini Wajen Bunƙasa Cigaba da Haɗin Kai da Tsaro a Nijeriya, Tsangayar  Fasaha da Nazarin Addinin Musulunci ta Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Mukoshy, J. I. da Umar, S. (2014). “Jagora ga Amfani da Intanet don Bunƙasa Harshen Hausa.” Muƙalar da aka gabatar a taron ƙasa da ƙasa na farko kan Karatun Hausa a Ƙarni na Ashirin da Ɗaya (Ƙrn. 21) a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jamiar Bayero, Kano.

Musa, M. B. (2019). “Sana'ar Kiwo a Ƙasar Hausa.” An ɗauko ranar 17 ga watan Afirilu, shekarar 2020 daga: https://www.alummarhausa.com.ng/2019/11/sanaar-kiwo-a-kasar-hausa.html.

Mwami, J.A.L. (2013). The Roles of Films in Moral Decadence Among Hausa Youth and the Emergence of Kauraye Miscreant Activities in Katsina. In Bunza, A.M. et al (eds). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 685-698. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Nadama, G. (1977). The Rise and Collapes of a Hausa State: A Social and Political History of Zamfara.” Unpublished Ph.D. Thesis, Zaria: Ahmadu Bello University.

Nasir, I. (2009). “Gabatar da Katun na Hausa a Kan Tatsuniyar Gizo da Ɓaure.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Newman, P. (2007). A Hausa-English Dictionary. United States: Yale University Press.

Nie, N. H. (2001). “Sociability, Interpersonal Relations, and the Internet: Reconciling Conflicting Findings.” In American Behavioral Scientist, 45(3), pp: 426-437.

Nie, N. H., Hillygus, D.S., & Erbring. L. (2002). “Internet Use, Interpersonal Relations and Sociability: A Time Diary Study.” In Wellman, B. & C. Haythornthwaite (eds.), Internet and Everyday Life. pp. 215-243. London: Blackwell.

Ogbonna, N. A. (2013). “Language in National Development: The Nigerian Perspective.” In Ndimele, M. & Yakasai H. M. (ed) Language, Literature and Culture in a Multilingual Society. Port Harcourt: M & J Grand Orbit Communications Ltd.

Ojua, T. (2019). “Can I Use Two or More Theories to Support my Research Model?” Retrived on 22 February, 2020 from: https://www.researchgate.net/post/Can_I_use_Two_or_more_theories_to_support_my_research_model.

Olatuja, O. (2016). “Revisiting the Question of the National Language in Nigeria by Olatuja Oloyede.” Retrieved on 16th February 2020 from: http://oloyede001.yu.tl/revisiting-the-question-of-the-national.xhtml.

Owusu-Acheaw, M. & Larson, A. G. (2015). “Use of Social Media and its Impact on Academic Performance of Tertiary Institution Students: A Study of Students of Koforidua Polytechnic, Ghana.” In Journal of Education and Practice. Vol. 6, No. 6, 2015 ISSN 2222-1735 (Paper), ISSN 2222-288X (Online), Pp.: 94-101.

Pandey, K. K.,  Shukla, P. K. &  Pradhan, N. (2015). “Internet Search Engine: A Comparative and Performance Evaluation of Web Search Engine and Meta Search Engine.” In Proceedings of International Conference on Emerging Research in Computer & Software Engineering. ISSN: 2393-9931. Retrieved on 17th March 2020 from: https://www.researchgate.net/profile/Kamlesh_Pandey2/publication/321 685207_Internet_Search_Engine_A_Comparative_and_Performance_Evaluation_of_Web_Search_Engine_and_Meta_Search_Engine/links/5a2ad8af0f7e9b63e538c79c/Internet-Search-Engine-A-Comparative-and-Performance-Evaluation-of-Web-Search-Engine-and-Meta-Search-Engine.pdf.

Pena, I. G. (2018). “Platonism as a Philosophical Method.” In Athens Journal of Humanities & Arts – Volume: 5, Issue 1 – Pages 45-60. DOI: = 10.30958/ajha.5.1.3.

Philip, J. J. (2001). Hausa. Netherlands: John Benjamins Publishing.

Press, G. (2015). “A Very Short History of the Internet and the Web.” Retrieved on 18th March 2020 from: https://www.forbes.com/sites/gilpress/2015/01/02/ a-very-short-history-of-the-internet-and-the-web-2/#12bc09017a4e. 

Rambo, I. (2007). “Nazari Kan Wasu Keɓaɓɓun Al’adun Auren Hausawa da na Dakarkari.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Rashid, A.R. (2019). Jita-jitan auren Buhari da Sadiya: Masallacin Aso Villa ta cika yau. An ɗauko ranar 24 ga watan Disamba, shekarar 2021 daga: https://hausa.legit.ng/1265641-jita-jitan-auren-buhari-da-sadiya-masallacin-aso-villa-ta-cika-yau.html.

Romualdo, P. & Alessandro, V. (2007). Evolution and Structure of the Internet: A Statistical Physics Approach. New Yourk: Cambridge University Press.

Sa’id, B. da wasu (editoci) (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Zaria: Ahmadu Bello University Press.

Sallau, B.A.S. (ND). HAU 214: Hausa Trades and Crafts. Department of Languages, Faculty of Arts, National Open University of Nigeria, Jabi, Abuja.

Sallau, B.A.S. (2009). Sana’ar Wanzanci da Sauye-Sauyen Zamani Jiya da Yau. Kundin digiri na uku wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Sallau, B.A.S. (2010). Magani A Sha A Yi Wanka A Buwaya. Kaduna: M.A. Najiu Professional Printers.

Sambo, M. M. (2009). “Keɓaɓɓun Kalmomin Kwamfuta.” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsuna da Al’adun Afirka, Jami'ar Ahmadu Bello, Zariya.

Sani, A-U. and Umar, M. M. (2018). “Global Growing Impact of Hausa and the Need for its Documentation.” In Contemporary Journal of Language and Literature, Vol.: 1 No.1, Pp.: 16-34. Available at: http://sgpicanada.com/index.php/CJLL/issue/download/1/Abu-Ubaida%20Sani%20and%20Muhammad%20Mustapha%20Umar.

Sani, A-U., Buba, U. & Mohammad, I. (2019). “Wanda Ya Tuna Bara...: Biɗa da Tanadi a Tsakanin Hausawa Matasa a Yau.” In Global Academic Journal of Humanities and Social Sciences, Vol-1, Iss-2 pp-44-50. 44. ISSN: 2706-901X (Print), 2707- 2576 (Online). Available at: https://gajrc.com/media/articles/GAJHSS_12_44-50.pdf.

Sarkin Gulbi, A. (2014). “Magani a Ma’auin Karin Magana.” Kundin digiri na uku wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakwkato.

Sarkin Gulbi, A. (2014). “Magani a Ma’aunin Karin Magana.” Kundin digiri na uku wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Seibert, U. (2017). “Greetings to the Followers of this Group.” Retrieved on 20th Afril 2020 from: https://hausaonline.wordpress.com.

 

Shehu, I. (2013). Gudummuwar Wasannin Hausa na Rediyo Wajen Bunƙasa Aladun Hausawa: Tsokaci Daga Wasan Kwaikwayo na Duniya Budurwar Wawa da Jamiiyar Jatau Na Albarkawa. In Bunza, A.M. et al (eds). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 629-644. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Shehu, M. da Aliyu, L. (2019). “Tasirin Wayar Salula Wajen Gurɓata Rayuwar Hausawa a Yau.” A cikin East African Scholars Journal of Education, Humanities and Literature, Vol - 2, Issue - 12, Pp 706-711. ISSN:  2617-443X.

Shehu, M. da Rambo, R. A. (2019). “Shafin Zumunta na Was’af (Whatsapp): Tasirinsa ga Lalacewar Tarbiyyar ‘Ya’yan Hausawa.” A cikin EAS Journal of Humanities and Cultural Studies, Vol. 1, Issue 6, Pp 357-362. ISSN: 2663-0958.

Shehu, M. da Sani, A-U. (2020). “Zamantakewar Hausawa Jiya Da Yau.” An ɗauko ranar 17 ga watan Afirulu, shekarar 2020 daga https://www.amsoshi.com/2019/02/zamantakewar-hausawa-jiya-da-yau.html.  

Siddiqui, S. & Singh, T. (2016). “Social Media its Impact with Positive and Negative Aspects.” In International Journal of Computer Applications Technology and Research. Vol. 5, Issue 2, Pp. 71 - 75, ISSN:- 2319–8656.

Strickland, J. (2020). “How did the Internet Start?” Retrieved on 17th March 2020 from: https://computer.howstuffworks.com/internet/basics/internet-start.htm.

Sulaiman, A.I. (2013). Ta’addancin Fyaɗe a Finafinan Hausa: Tsokaci Kan Tasirin Finafinan Hausa ga Taɓarɓarewar Al’adu a Yau. In Bunza, A.M. da wasu (editoci). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 731-742. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Tambuwal, A. Y. (2018). “Manunin Tarbiyya a Karin Maganar Bahaushe.” Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Thein, K. (2018). “Soul and Incorporeality in Plato.” In Eirene Sudia Graeca Et Latina, LIV, 2018, Pp. 53–95. Centre for Classical Studies Institute of Philosophy of the Czech Academy of Sciences, Prague.

Tsaure, M. B. & Sani, A-U. (2016). “The National Question: Language Policy and the Quest for a Common Language in Nigeria.” Being a paper presented at the international conference of the Faculty of Arts and Islamic Studies, on The Role of the Arts on Development held at Musa Abdullahi Auditorium, Bayero University, Kano, Nigeria.

Tukur, A. (1988). “Nazari a Kan Cututtukan da Suka Shafi Fatar Jiki da Magungunansu a Bahaushiyar Al’ada.” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jaimi’ar Bayero, Kano.

Umar, B.U. (2013). Nason Zamananci Wajen Zaɓen Mijin Aure: Tsokaci a Kan Wata Addu’ar ‘Yammata Ta Cikin Wayar Salula. In Bunza, A.M. et al (eds). Excerpts of International Seminar on The Deterioration of Hausa Culture (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa), Pp 669-684. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.

Umar, M. M. (2012). “Nazarin Saƙon GSM a Wayar Salular Hausawa. Kundin digiri na biyu wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jamiar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Usman, B. B. da Bunza, D. B. (2020). “Fina-Finan Hausa a Mahangar Al’umma: Gyara ko Ɓarna?” A cikin East African Scholars Journal of Education, Humanities and Literature, Vol. 3, Issue 3. Shafi 52-61. ISSN: 2617-443X. DOI: 10.36349/EASJEHL.2020.v03i03.010.

Weinstein, S. (2016). History & Technologies of the Internet. A lecture note delivered between 22nd September to 13th October 2016 every on Thursdays 7:30pm – 9:00pm at WEA Community Room, Lincoln Towers University.

Wellman, B. (2001) "Physical Place and Cyber-Place: The Rise of Networked Individualism." In International Journal for Urban and Regional Research, 25: 22752.

Wellman, B. et al (2002). Examining the Internet in Everyday Life. Keynote address (given by Barry Wellman) to the Euricom Conference on e-Democracy, Nijmegen, Netherlands.

Yahaya, S. U. (2020). “Damben Hausawa a Zamanance.” Kundin digiri na biyu da aka gabatar a matakin jarabawar cikin gida (Internal Defense) a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

'Yartsakuwa, U. D. (2017). “Zumunci a Yanar Gizo: Harshen Sadarwa Tsakanin Matasa a Shafin Whatsapp.” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami'ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Yunusa, Y. (1989). Hausa a Dunƙule. Kano: Triuph.

Yusuf, L.M.S. (2017). Tasirin camfe-camfen Hausawa cikin tarbiyyarsu (Na daya). An cirato ranar 20 ga watan Ogusta, shekarar 2021, daga: https://bakandamiya.com/blogs/865/143/tasirin-camfe-camfen-hausawa-cikin-tarbiyyarsu-na-daya.

 

 

MANAZARTAN INTANET

Abincin Hausawa, (2015). “Waina.” An ɗauko ranar 17 ga watan Afirilu, shekarar 2020 daga: https://abinci.com/post/130573384693/waina.

Arewa24, (2018). “Tashe Ep 5. An ɗauko ranar 12 ga watan Afirilu, shekara ta 2020 daga: https://www.youtube.com/watch?v=FcLUsPfbOGE.

BBC (British Broadcasting Company) (2010). “Gagarabadau: Tasirin Intanet kan rayuwar Hausawa.” Retrieved on 19th February 2020 from: https://www.bbc.com/hausa/news/story/2010/03/printable/100318_gallerysuperpower.shtml.

BBC (British Broadcasting Company) (2016). “Yadda Facebook ya Zama Makekiyar Maƙabarta.” An ɗauko ranar 20 ga watan Fabarairu na shekarar 2020 daga: https://www.bbc.com/hausa/mujalla/vert_fut/2016/08/160822_unstoppable_rise_of_facebook_rise.

BBC, (British Broadcasting Company) (2020). “Matan Najeriya ba su Iya Soyayya Kamar Turawa ba.” An ɗauko ranar 20 ga watan Fabrairu na shekarar 2020 daga: https://www.bbc.com/hausa/labarai-51190140.

Hausa Top, (2020). “About Us.” Retrieved on 18th April 2020 from: http://www.hausatop.com/about-us/.

Hutu Dole, (2018). “Game da Hutudole.” An ɗauko ranar 18 ga watan Afirilu, shekarar 2020 daga: https://hutudole.com/dangane-da-hutudole_7/.

Internet Live Stats, (2020). “Home Page”. Retrieved on 20th February 2020 from: https://www.internetlivestats.com/.

Java Point (ND).Computer Network Types. Retrived on 20th August, 2021 from: https://www.javatpoint.com/types-of-computer-network.

Kano Online, (2020). “Fadar Mai Martaba Sarkin Katagum Dake Azare.” An ɗauko ranar 18 ga watar Afirilu, shekarar 2020 daga: http://azareonline.com/Home.

Ohio Department of Taxation, (2004). New Defination of Food. Retrieved on the 20th of August 2021 from: http://tzhcpas.com/wp-content/uploads/2011/01/streamlined_sales_tax_food_BR.pdf

Rumbun Ilimi, (ND). Abinci. An cirato ranar 20 ga watan Ogusta, shekarar 2021, daga: https://www.rumbunilimi.com.ng/Abinci.html#gsc.tab=0.  

UF College of Journalism and Communications, (ND). “What is Theory?” Retrieved on 22nd February, 2020 from: http://faculty.jou.ufl.edu/mleslie/spring96/theory.html.

Wikiwand, (ND). Hausawa. An cirato ranar 20 ga watan Ogusta, shekarar 2021, daga: https://www.wikiwand.com/ha/Hausawa

KAFAFEN INTANET DA AKA ZIYARTA

http://azareonline.com/

http://duniyarso.blogspot.com/

http://hausadictionary.com/

http://kanoonline.com/ 

http://katsinaposthausa.com/

http://tsangayaradabi.blogspot.com/

http://tzhcpas.com

http://www.dandali.com/

http://www.gumel.com/

http://www.haiman.com.ng/

http://www.hausang.com/

http://www.hausatop.com/

http://www.teachyourselfhausa.com/

http://zahramuhammadmahmud.blogspot.com/

https://abinci.com/

https://computer.howstuffworks.com

https://cprg.hypotheses.org/

https://dealdey.com.cutestat.com/

https://gidannovels.guidetricks.com/

https://gobirmob.com/ha/

https://hausa.leadership.ng/

https://hausaonline.wordpress.com/ 

https://hausaweddings.com/

https://hutudole.com/

https://jaridarhausa.com/

https://makarantarhausa.com/

https://managarciya.com/

https://parktelonline.com/

https://qalubale.news.blog/

https://slot.ng/

https://www.6pm.com/

https://www.allsaints.com/

https://www.alummarhausa.com.ng/

https://www.amazon.com/

https://www.amsoshi.com/

https://www.anntaylor.com/

https://www.arewafresh.com.ng/

https://www.arewanishadi.com/

https://www.arewarmu.com.ng/

https://www.arewaswag.com.ng/

https://www.asos.com/

https://www.babansadik.com/

https://www.bakandamiya.com/

https://www.barnesandnoble.com/

https://www.batsapost.com/

https://www.britannica.com/art/Platonic-criticism

https://www.comparitech.com

https://www.forbes.com

https://www.hausagett.com.ng/

https://www.hausaloaded.com/

https://www.hausatrust.com/

https://www.hausawasite.com.ng/

https://www.internetlivestats.com/

https://www.isyaku.com/

https://www.jakadanfasaha.com/

https://www.javatpoint.com

https://www.jumia.com.ng/

https://www.kara.com.ng/

https://www.konga.com/

https://www.madubiya.com/

https://www.muryarhausa24.com.ng/

https://www.muryaryanci.com/

https://www.ray-ban.com/usa

https://www.rumbunilimi.com.ng/ 

https://www.statista.com/

https://www.urbanoutfitters.com/

https://www.wikihausa.com.ng/

https://www.wikiwand.com

https://www.yoox.com/us

WAƊANDA AKA YI HIRA DA SU

Suna

Tsokaci

Prof. Aliyu Muhammad Bunza

Farfesa

Prof. Bashir Aliyu Sallau

Farfesa

Ass. Prof. Abdullahi I. S. S.

Ɗan galadiman farfesa

Ass. Prof. Yakubu Aliyu Gobir

Malami a jami’a

Malam Aliyu Muhammad

Malami a jami’a

Dr. Abdullahi Isah Muhammad

Malami a jami’a

Mr. Uwe Seibert

Mai kafafen Hausa Online da Karin Magana

Sa’idu Umar Yahaya

Kasuwancin Waya

Lawan Ɗalha

Mai kafar Bakandamiya

Bashir Ahmed

Mai kafar Hutu Dole

Abubakar Muhammad Tsangarwa

Mai kafar Rumbun Ilimi

Bello Muhammad

Mai kafar Makarantar Hausa

Shehu Auwal

Mataimakin mai kafar Amsoshi

Mohammed Atabo

Mai kafar Gidan Karatu

Zainab Sani

Mai sana’ar sayar da abinci

Abdulrahman Muhammad Manga

Masanin Intanet

RATAYE

Rataye na 1: Waƙar Soshiyal Midiya Duniyar Matasa ta Ɗaniro Katsina

 

Amshi: Soshiyal midiya duniyar matasa,

Mu yaɗa alkairi kar mu yaɗa zamba.

 

1.  Soshiyal midiya duniyar matasa,

A duniyar catin yanzu ta yi rassa,

Ya sa zukatan wasu sun shagalta wasa,

Ya sa waɗansu a hanset su rinƙa gasa,

Maza da ‘yammata kanku zan yi casa,

Har da matan gidan ma ba sa ƙi ji ba.

 

2. Gudu muke ta faman yi ba muts tsaya ba,

Muna saman wani tsauni ba mus sani ba,

Ɗakin duhu mun fita ba da fittila ba,

Ana ta nisa dawa ba da jin kira ba,

Ana shiga rijiya ba da shawara ba,

 Gun fita ya ake? Ban ji mun sani ba.

 

3. A yaɗa alkairi kar a yaɗa zamba,

A nan ake mai da kaɗan ta zamma babba,

A nan ake haddasa ƙi a rai da gaba,

A nan ake tarbiyyar da ban faɗi ba,

A nan ake wargaza tarbiyyar su baba,

 Duk a nan midiya in ba kus sani ba.

 

4. Waɗansu ko sun zo don su yo zumunta,

Waɗansu na yi domin su yo abota,

Su kare addini ko a gyara bauta,

Su sanya ayoyi har ko ak karanta,

Domin a wanke duka zuciya ƙasanta,

 Wassu na yin hakan midiya ku duba.

 

5. Waɗansu ko lamarin ba ni son tunawa,

Irin abin da idanu suke ganewa,

Waɗansu hoto na tsiraici za su sawa,

A midiya nan ne dandalin gwadawa,

Kowa irin mai halinsa zai kulawa,

 Wa ya ce watta rana ba sa haɗe ba?

 

 

6. Abin takaici ma har da ma amare,

Su samu ƙato catin suke a tare,

Su kama yin soyayya ƙwarai a tare,

Har ma ta ce masa honi su canza yare,

Da iggiyar aure ukku kanta ɗaure,

 Shi miji gwangwani kun ga bai sani ba.

 

7. A dole matarka waya ka ba ta babba,

A kan hakan ka hana sai ku rinƙa gaba,

Da kai bayanin ka cocilan ta karɓa,

Sai ta fake maka kallo ba ta bari ba,

Kewarka in ba ka nan ba ta sake ba,

 Me ya sa Alƙurani ba kya riƙe ba.

 

8. Sannan batun ‘yammata da ‘yan samari,

Babbar waya kadda ta sakan ɓarar da gari,

Su dai kawai catin shi suke ma fari,

Shi ne yake kai su cikin jakar magori,

A kama labari sun ɓarar da gari,

 Duk a nan midiya ban ji kun musa ba.

 

9. Ga ‘yan siyasa ita midiya ku duba,

Nan ne wurin jawo tsokana da zamba,

Nan ne wurin ce ma gwaninka bai iya ba,

Nan ne wurin nuna abin da bai yi kyau ba,

Nan ne wurin haddasa gardama da gaba,

 Dandali ne ake ba na fa’ida ba.

 

10. Batu na alkairi ba a son azawa,

Batu na sharri shi ne abin gwadawa,

‘Yan mintuka ka gani ya yi zagayawa,

Duk duniya kowa za ya yo ganowa,

Sirrin waninka a nan ka yi bayyanawa,

 Babu da-na-sani tun da bai gama ba.

 

11. Idan ina waƙar wassu za su tsargu,

Barai a ce an sanyo kiɗan kalangu,

Ga wanda bai da fahimta ko za ni zagu,

Tuna tunanin rushe musu katangu,

Ina nufin wassu su zam kamar guragu,

 Ni ko Ɗaniya ban yo nufin hakan ba.

 

12. Ɗan Kattsinawa ne wanda yay yi waƙe,

A da ina barci yanzu ga ni farke,

Ku gane noma shi ne ake a duƙe,

Ku san batun tafiya na wurin fatake,

Da an yi nisa yaro ka gan shi ɗauke,

 Don ba zai juriya ne da taffiyar ba.

 

13. Nai godiyata tari a gun masoya,

Ɗan’iro mai waƙa ba ni ƙin masoya,

Ni ɗan Mutan Katsinawa muna da kunya,

Gami da tarbiyya gunsu ne na koya,

Lambar waya in na faɗe ta sai ku juya,

Gaisuwa ni da ku don ba ta katse ba.

Post a Comment

0 Comments