TAMBAYA TA 153
Assalamu alaikum
Mene ne hukuncin Auren Dibar
wuta a Musulunci?
Shin hukuncin Yana da bambanci idan Macce ce ta shirya Auren Dibar wutar ba tare da sanin tsohon Mijinta ba?
Mene ne hukuncin idan matar
da Mijin suka shirya Auren Dibar wutar?
Sannan hukuncin
yana da bambanci idan sabon
mijin da Aka Aura yana da Masaniya akan Auren Dibar wuta ne za a yi da shi?
(daga Barrister Isma'il)
AMSA
Wa alaikumus salam wa
rahmatulLah.
Wannan tambayar mun riga mun
amsa irinta achan baya. Amma saboda muhimmancin Mas'alar, da kuma yawan
faruwarka a cikin al'ummah, sai na ga cewa ya zama wajibi mu sake amsa wannan
dinma.
Imamuz-Zahabiy (rah) ya fada
a cikin shahararren littafinsa mai suna "KITABUL-KABA'IR" akan shafi
na 141, Laifi na 53, yana cewa:
Hadisi ya inganta daga
Sayyiduna Abdullahi bn Mas'ud (ra) yana cewa: "MANZON ALLAH (Sallallahu
Alaihi Wasallam) YA TSINEWA MAI AUREN KISAN WUTA, DA KUMA WANDA AKA YI AUREN
KISAN WUTAN DOMINSA".
Imam Tirmidhy (rah) ya ce:
Aiki a bisa wannan fahimtar
(rashin halarcin auren kisan wuta ta kowacce fuska) ya tabbata agun ma'abota
ilimi. Daga cikinsu akwai
Umar bn Khattab,
Uthman bn Affan
Abdullahi bn Umar (Allah shi
Ƙara yarda dasu).
kuma wannan shi ne fahimtar
FUƘAHA'U daga tabi'ai.
Imamu Ahmad bn Hanbal da
Imamun Nisa'iy su ma sun ruwaito irin wannan hadisin Da isnadai masu inganci.
Wani mutum ya tambayi
Abdullahi bn Umar (ra) cewar:
"YAYA KAKE GANI? Shin
ya halatta in auri matar da wani mutum ya saki domin in halatta ta a gareshi??
Sai ya amsa masa da cewar:
A'a bai halatta ba. sai dai
in za ka aureta, to ka aureta domin kwadayin zama da ita, idan kaga ta yi maka
shikenan ka zauna da ita. Idan kuma ba ta yi maka ba ka sake ta. (Amma auren
kisan wuta haramun ne). Ya ci gaba da cewa: MUN KASANCE MUNA ƘIRGA SHI (irin wannan auren) AMATSAYIN
KWARTANCI AZAMANIN MANZON ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam).
Imamul-Athram da
Ibnul-Munzir sun daga Sayyiduna Umar bn Khattab (ra) yana cewa:
"BA'A TAƁA ZUWA MIN DA MASU AUREN KISAN WUTA BA,
FACHE SAI NA JEFESU (RAJAMUWATO JIFA IRIN NA HADDI).
Wani Mutum ya saki matarsa (Saki
uku) dama kuma 'Yar baffansa ce, Sai daga baya ya dawo yana nadama, sai wani
mutum kuma ya zo yake tambayar Sayyiduna Abdullahi bn Umar (radhiyalLahu anhu)
cewa: Shin ya halatta inje in aureta, (daga baya in sake ta) domin in halasta
masa ita??"
Sai ya ce masa "Zaman
Zina sukeyi ko da sun kai shekara 20 suna tare. In dai an daura auren da wannan
niyyar.
Imam Ibrahim An-Nakha'iy ya
ce IN DAI DAYAN CIKIN MUTUM UKUN NAN (wato mijin farko, ko miji na biyu, ko
kuma ita matar) in dai WANI DAGA CIKINSU ya yi NUFIN AUREN KISAN WUTA, TO AUREN
NA BIYUN DANA FARKON DUK SUN LALACE. (Dama bai halatta ba). KUMA DUK DA HAKA
MATAR BA TA HALATTU GA WANCAN MIJINTA NA FARI BA (Koda ta dawo hannunsa).
Imam Hasanul-Basary ma ya ce:
In dai dayan cikin mutum ukun nan ya yi niyyar auren kisan wutan, to auren ya
'baci.
Daga Cikin wadanda suke kan
wannan fahimtar akwai:
IMAMU MALIK
SUFYANUTH THAURY
IMAMU AHMAD BN HANBAL
IMAM LAYTHU BN SA'AD.
Irin wannan auren bai
halatta ma tun farko adaura shi ba (Mutukar Malamai da waliyyan auren sun
fahimci niyyar masu auren) Kuma ya kamata hukuma ta rika ladabtar da dukkan
wadanda aka samesu da hannu a ciki.
WALLAHU A'ALAM.,
DAGA ZAUREN FIƘHU JUNE 15 2013 (ANYI RUBUTUN NAN TUN
SHEKARU 12 DA SUKA GABATA). YA ALLAH KA SANYA IKHLASI CIKIN DUKKAN AYYUKANMU
AMEEN.
EMAIL ADDRESS: zaurenfiƙhu@gmail.com
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.