Ticker

6/recent/ticker-posts

Nazari Kan Kasuwancin Littattafan Hausa: Gudumawarsu Wajen Haɓaka Tattalin Arzikin Ƙasa

Being A Paper Presented at the National Conference, Theme “Kano: Politics, Economy and Society from the Earliest Times to the Present” Organized by Faculty of Humanities, Yusuf Maitama Sule Uniɓersity, Kano. On Monday 15th – Wednesday 17th April, 2019.

littattafan hausa

Nazari Kan Kasuwancin Littattafan Hausa: Gudumawarsu Wajen Haɓaka Tattalin Arzikin Ƙasa

 

Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya)

Postgraduate Student, Department of Nigerian Languages and Lisguistics, Bauchi State Universiry, Gadau. (Masters in view).

07066366586, 08125351694

Email: ibrahimba182@gmail.com

 

Da

Audu Baba

School of Postgraduate, Department of Nigerian Language, Bayero Uniɓersity Kano. (Masters in view)

08069580413

Email: abdullahibabanguru@gmail.com

 

 

Da

Saminu Sabo

College of Education and Legal Studies Nguru, Yobe State

 

1.0       Gabatarwa

            Rubutu hanya ce sassauƙa ta isar da saƙo ga al’umma, wannan rubutun kuwa ya shafi na zube ne, ko waƙa ko kuma na wasan kwaikwayo. Wannan hanya ta rubutu ta zaburar da ‘yan ƙasa ta fuskoki da dama  tun daga lokacin da suka buɗe idanuwansu a kai. Wannan rubutu ya kasu zuwa gida uku, wato zube (ƙagaggen labari), waƙa da kuma wasan kwaikwayo. Waɗannan kashe – kashen yana ƙunshe da ire – iren mutanen da suka ƙware wajen tsara su da rubuta su. Ɓangare mafi girma cikin waɗannan nau’o’i shi ne ƙagaggen labari.

            Marubuta ƙagaggun laraban Hausa ba ya ga zaburar da ‘yan ƙasa da suke yi ga rubuce – rubuce, sun bayar da muhimmiyar gudumawa wajen haɓaka tattalin arzikin ƙasa. Rubuta ƙagaggun labarai a yau, ɗaya ce daga cikin sana’o’in da suke tsakanin al’umma, musamman mata da matasa maza. Sana’ar, wadda take ta ƙirƙirar labari ce da tsarawa bisa baiwa da hikimar da Allah ya huwace wa bawa. Ta irin wannan hanya ce wasu rukunan al’umma rayuwarsu kacokan ta ɗoru a kan wannan sana’a. Baya ga nau’in mutanen da suke ƙirƙirar labarin, su tsara, akwai wasu nau’o’in mutane da suka yi tarayya a kai wajen yaɗuwar waɗannan littattafai.

            Cikin wannan takarda an yi ƙoƙarin bayyana ire – iren mutanen da rayuwarsu ta jingunu zuwa ga wannan sana’a, wadda jingunuwar rayuwar tasu ya shafi cinsu, shansu da tufafinsu. Sai ya kasance bunƙasa tattalin arzikin ƙasa ne, domin su a karan kansu suna samun biyan buƙatunsu na yau da gobe, sannan kuma suna bayar da haraji ga hukuma, wanda haraji ga hukuma haɓaka tattalin arziki ne ga asusun ƙasa. 

1.1       Ma’anar Ƙagaggun Labarai

            Masana sun tattauna wajen bayyana ma’anar ƙagaggun labarai. Misali: Yahaya (1992:65) ya bayyana shi da cewa, “Na ɗaya daga cikin rukunin adabin Hausawa na zamani da masana adabin Hausa suka bayyana shi da ‘zube’, wanda shi ne na farko a cikin rukunin, kafin waƙa da wasan kwaikwayo.”

            Shi kuwa Mukhtar (2016:2) a wata lakca da ya gabatar, ya ce, “Shi ƙagaggen labari cike yake da zantukan hira da nishaɗi, wanda ba da gaske ya taɓa faruwa ba, saboda ana samar da shi ne kawai don nishaɗantarwa.”

            Duba da waɗannan ma’anoni da suka gabata, ƙagaggun labarai na Hausa, su ne ire – iren labaran da ake samu a rubuce ko da ka, domin samun abokin hira da ɗebe kewa ta hanyar karantawa ko sauraro. Tun bayan da Hausawa ‘yan ƙasa suka koyi karatu da rubutu, sai suka riƙi hanyar rubuta ƙagaggun labarai a matsayin wata hanya ta sana’a, musamman ta la’akari da yadda ake ƙara samun yawaitar masu karantawa, wanda hakan sai ya haifar da yawaitar marubuta waɗannan ƙagaggun labarai, ciki kuwa maza da mata, matasa da manya.

1.2       Tarihin Rubutun Ƙagaggun Labarai Na Hausa

            Yahaya (1988:77) ya bayyana tarihin rubuce-rubuce na ƙagaggun littattafai bai daɗe sosai ba, domin an same su ne bayan shigowar Turawa, musamman masu bincike da yaɗa addinin Kirista irin su J.F. Schon. Schon ya yi rubuce-rubuce duk da kasancewar mafi yawan littattafan na shi sun fi kama da na yaɗa addinin Kirista, face littafinsa na Letafin Magana Hausa (1857) da ya yi kama da zube, sai na ƙarshe wato ‘African Proɓerbs, Tales and History (1886)’ da ya fi kama da ƙagaggun labarai. Yunƙurin haɓakarsu kuwa, ya biyo bayan zuwan Turawa ‘yan mulkin mallaka a waɗannan rubuce-rubucen a cikin zube na Hausa. Misali an samu Frank Edgar, Fletcher, Rattray R.S. da Whitting. Sai kuma lokacin da aka kakkafa makarantun boko a Jihar Arewa. Misali a lardin Sakkwato a 1905 ƙarƙashin shugabancin Mr. Burden, wadda aka rufe ta sakamakon rashin kai yara. Sannan a 1909 Gwamna Lugard ya sa Mr. Harns Ɓischer wato (Ɗan Hausa) ya sake buɗe wata makarantar a Kano.                 

2.0       Kafa Hukumomi da Ƙungiyoyin Rubuta Ƙagaggun Labarai

            Baya ga samar da ɗaiɗaikun waɗancan rubuce – rubuce, an yi ƙoƙarin haɓaka rubutattun ƙagaggun labarai na Hausa ta hanyoyin kafa hukumomi waɗanda za su samar da sabbin littattafan ƙagaggun labarai, da kuma fassara wasu rubuce – rubuce. Waɗannan hukumomi da ƙungiyoyi da aka kafa, sun taka muhimmiyar rawa wajen samar da sabbin littattafan ƙagaggun labarai. Don haka a nan, dole mu kalli haɓakar waɗannan littattafai da fuskoki biyu, wato ta fuskar hukumomi da kuma ƙungiyoyi.

2.1       Gudumawar Hukumomi/Kamfanoni Wajen Samar da Litattafan Ƙagaggun Labarai

            Ko shakka babu, hukumomi/kamfanoni sun taka rawa wajen samar da sabbi da fassarawa na littattafan ƙagaggun labarai na Hausa. Samuwar waɗannan hukumomi sun yawaita littattafan zube waɗanda suke zama tsani na samar da wasu a yau. A taƙaice, ga jerin hukumomi/kamfanoni da kuma wasu cikin littattafan da suka samar.  

2.1.1    Hukumar Gudanarwa ta Makarantar Midil, Katsina

            An kafa wannan Hukuma a shekarar 1927, inda Hukumar ta yi nasarar samar da wasu littattafai waɗanda suka haɗa da:

i.          Hausa Stories na Malam H.B.G. Nuhu

ii.         Littafin Karatu na Hausa na Malam Bello Kagara

iii.       Takobin Gaskiya na Malam Nagwamatse

2.1.2    Hukumar Fassara (Translation Bureau)

            An kafa wannan hukuma a shekarar 1927. Wannan hukuma ita ma ta samar da littattafai da dama, kamar yadda Maƙera (2009) da Lawan (2011) suka bayyana a cikin Abu Sabe (2013: 1 – 5), irin littattafan da aka samar a ƙarƙashin wannan hukuma ta fassara sun haɗa da: 

i.          Dare Dubu da ɗaya (1933) na Mamman Kano da Frank Edger 

ii.         Littafin Hausawa da Maƙwabtansu

iii.       Labaru Na Da da Na Yanzu (1931)

iɓ.        Fassara littafin kiwon lafiya (1931) (Muktar, 2004:18).

            A cikin shekarar 1933 ne aka canja sunan Hukumar Fassara ya koma Hukumar Talifi, wato Literature Bureau a Turance. An yi hakan saboda la’akari da ayyukanta ba sun tsaya a fassara ba ne kawai, har da sanya gasa da samar da ƙagaggun labarai. An naɗa Dr. R.M. East a matsayin Shugaba, sannan an samar da wasu littattafai a yayin gasar farko da Hukumar ta sa, musamman guda biyar da suka yi nasara waɗanda suka haɗa da:

i.          Ruwan Bagaja (1933) na Malam Abubakar Imam.

ii.         Gandoki (1933) na Malam Bello Kagara.

iii.       Shehu Umar (1933) na Malam Abubakar Tafawa Balewa

iɓ.        Idon Matambayi (1933) na Malam Muhammadu Gwarzo.

ɓ.         Jiki Magayi (1933) na John Tafida da R.M. East.

2.1.3    Kamfanin Gaskiya Ta Fi Kwabo

An kafa wannan kamfani a shekarar 1945, musamman la’akari da aka yi da yadda gwamnatin mulkin mallaka ta Arewacin Nijeriya ta zaɓi ‘yan Arewa a shekarar 1939 domin su taimaka a cikin yaƙin duniya na ɗaya, inda buƙatuwar a yawaita labaran yaƙi ta taso. Wannan Hukuma, an naɗa Alhaji Abubakar Imam ya zama Edita; yayin da Mr. Rupert M. East ya zama mataimakinsa. Daga shekarar da aka kafa ta, wato 1945 zuwa ƙarshen 1949 ta samar da littattafai irinsu:

i.          Ikon Allah na Dr. R.M. East da Alhaji Abubakar Imam,

ii.         Kyaftin Makama na Abdulkadir Makama,

iii.       Zamanin Nan Namu na E.M. Rimmer da Ahmadu Ingawa,

iɓ.        Bala Da Babiya na Nuhu Bamalli

ɓ.         Mango Park Mabuɗin Kwara na Alhaji Nuhu Bamalli

ɓi.        Yawon Duniya Hajji Baba na Alhaji Abubakar Tunau Mafara ya fassara (Abu Saber, 2013: 7, Mukhtar, 2010:19). 

2.1.4    Hukumar NORLA (Northern Region Literature Agency)

An kafa wannan hukumar a shekarar 1953, kuma aka damƙa ta ga Alhaji Abubakar Imam; domin ya gudanar da azuzuwan yaƙi da jahilci da kuma samar da littattafai don waɗannan azuzuwan. Wannan Hukuma, ta ci gaba da gudanar da ayyukanta har zuwa shekarar 1959, lokacin da aka rushe ta aka mayar da aikinta zuwa Kamfanin Gaskiya. A tsakanin waɗannan shekaru, wato daga shekarar 1953 zuwa 1959, wannan Hukuma ta samar da littattafai guda shida (6), waɗanda suka haɗa da:

i.          Hali Zanen Dutse na Sarkin Musulmi Alhaji Abubakar na III

ii.         Littafin Addini na Alhaji Halliru Binji

iii.       Tarihin Fulani na Wazirin Sakkwato Alhaji Junaidu

iɓ.        Littafin Mamaki na Abdullahi Maƙarfi

ɓ.         Littafin Mafarki na M.M. Kumasi

ɓi.        Motsi Ya Fi Zama na Malam Aminu Kano, da sauransu. (Mukhtar, 2010:20).   

2.1.5    Hukumar Northern Nigerian Publishing Company NNPC

Wannan Hukuma an kafa ta a shekarar 1960. Ita ma ta yi hoɓɓasa wajen samar da littattafai. Cikin littattafan da ta samar sun haɗa da:

i.          Nagari Na Kowa (1959) na Jabiru Abdullahi.

ii.         Tauraruwa Mai Wutsiya (1969) na Umaru Dembo da sauransu. (Yahaya, 1988:213)

            Bayan haka, wannan Hukumar ta (NNPC) ta sa gasar ƙagaggun littattafai a cikin shekara ta 1981 inda ta buga uku daga cikin waɗanda suka yi nasara. Cikinsu akwai:

i.          So Aljannar Duniya (1980) na Hafsatu Abdulwaheed

ii.         Ahmadi Na Malam Amah (1980) na Magaji Ɗanbatta

iii.       Mallakin Zuciyata (1980) na Sulaiman Ibrahim Katsina.

            Haka kuma baya ga waɗannan kamfanoni da hukumomi an sami wallafe-wallafe da dama a cikin shekarun 1970 misali:

i.          Littafin Abdullahi Ka’oje mai suna ‘Dare Ɗaya’ wanda aka buga a shekarar 1973.

ii.         Littafin Abdulƙadir Ɗangambo mai suna ‘Kitsen Rogo’ wanda aka buga a shekarar 1978 da dai sauransu. (Mukhtar, 2010:20)

2.1.6    Hukumar Al’adu Ta Arewa (Federal Department of Culture)

Wannan Hukuma an kafa ta a shekarar 1982. Ita ma ta yi ƙoƙari wajen samar da littattafan ƙagaggun labarai, cikinsu akwai:

i.          Turmin Danya (1982) na Sulaiman Ibrahim Katsina.

ii.         Tsumagiyar Kan Hanya (1982) na Musa Muhammad Bello.   

iii.       Ƙarshen Alewa Ƙasa (1982) na Bature Gagare.

iɓ.        Zaɓi Naka (1982) na Munir Mamman Katsina. 

            Baya ga waɗannan, a shekarar 1984 wata al’adar rubuce – rubuce na ƙaggagun littattafai ta sake kunno kai wadda aka sa wa suna “Adabin Kasuwar Kano” wadda a Turance ake kira “Kano Market Literature”. An sami wani jigo na soyayya inda ya yi tasiri sosai da sosai a cikin wannan adabin. Daga cikin waɗanda suka share fage akwai irin su littafin:

i.          Rabin Raina (littafi na ɗaya) (1984) na Talatu Wada Ahmed.

ii.         Soyayya Gamon Jini (1986) na Ibrahim Hamza Abdullahi.

iii.       In Da Rai (1987) na Idris Imam.

iɓ.        Budurwar Zuciya (1987) na Balaraba Ramat Yakubu.

ɓ.         Kogin Soyayya (1988) na A.M. Zahraddeen.

ɓi.        Idan So Cuta Ne (1989) na Yusuf M. Adamu (Muktar, 2010: 21).

2.2       Kafa Ƙungiyoyin Marubuta Ƙagaggun Labarai Na Hausa

            Bayan ɓullowar Adabin Kasuwar Kano a 1984, kamar yadda Malumfashi (1984) ya raɗa wa suna, sai ƙagaggun labarai suka fara yawaita, musamman ma waɗanda suke da jigon soyayya. Wannan sai ya haifar da kakkafa ƙungiyoyi na marubuta daban-daban. Mukhtar (2004:27), ya jero ire-iren ƙungiyoyin da aka samar tun a wancan lokaci, cikinsu akwai:

i.          Ƙungiyar Raina Kama

ii.         Ƙungiyar Marubuta ta Himma     

iii.       Ƙungiyar Marubuta ta Mikiya

iɓ.        Ƙungiyar Marubuta ta Ɗan haƙin da ka Raina

ɓ.         Ƙungiyar Marubuta ta Soyayyar Zamani

ɓi.        Ƙungiyar Marubuta ta Kukan Kurciya

ɓii.       Ƙungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) da sauransu.                    

            Kafa waɗannan ƙungiyoyi ya haddasa samuwar tarin marubuta mata da yawan gaske waɗanda littattafansu suka mamaye kasuwannin ƙasar Hausa.

2.3       Wasu Cikin Littattafan Ƙagaggun Labarai Na Hausa da Marubutunsu a Yau

            Baba da Nayaya (2017:6) sun haƙaito ire – iren littattafan ƙagaggun labarai na Hausa a wani aki da suka gabatar. Cikin waɗannan litattafan akwai:

i.          In da Alƙawari (1992) na Bala Anas Babinlata

ii.         Duniya Sai Sannu (1997) na Ado Ahmad Gidan Dabino, MON.

iii.       Mafarkin Khadija (2014) na Maimuna Idriss Sani Beli

iɓ.        Rayuwar Bilkisu (2016) na Ayuba Muhammad Ɗanzaki.

ɓ.         Launin So (2009) na Kabir Yusuf Anka

ɓi.        Jininmu Ɗaya (2012) Abida Muhammad

ɓii.       Amon ‘Yanci (2013) Halima Ahmad Matazu

ɓiii.     Jarrabi (2014) na Abubakar Auyo.

iɗ.        Ɗan Musulmi (2014) na Rahma Abdulmajid

ɗ.         Me Zan Yi Da Ke (2016) na Maryam Rabi’u Ado

ɗi.        Marubuciya (2017) na Jiddah Haulat Nguru

ɗii.       Bulaguron Wawa (2014) na Sa’adatu Baba Ahmad

ɗiii.     Rumaisa (2014) na Fauziyya D. Suleiman.

ɗiɓ.      Adon Dawa (2011) na Jamila Umar Tanko

ɗɓ.       Babban Dare (2014) na Amina Dauda Abubakar.         

            Idan an dubi waɗannan littattafai, za a ga mafi yawan jigonsu ya karkata ne a kan soyayya, wannan shi ya ƙara tabbatar da sauyin jigo da aka samu tsakanin wallafe – wallafen baya, har kawo shekarar 1984, da kuma waɗanda ake haifa a yanzu. Wannan kuwa na da alaƙa da yanayin da aka samu na sauyin zamani da kuma wanzuwar baƙin al’adu a cikin al’adun Hausawa.

 

2.4       Marubuta Ƙagaggun Labaran Hausa        

            Tun lokacin da sana’ar rubuce – rubucen ƙagaggun labarai na Hausa ta fara kankama a tsakanin Hausawa, sai aka samu yawaitar marubutan a dukkanin sassanin ƙasashen Hausawa. Kawo yanzu, ba za a iya ƙayyade adadin marubuta ƙagaggun labarai na Hausa ba.

            Nayaya da Baba (2018: 55) sun jero wasu daga cikin marubutan ƙagaggun labarai na Hausa. Misali;

i.          Bilkisu Ibrahim Nabature

ii.         Zuwaira Isa

iii.       Fauziyya D. Suleiman

iɓ.        Hadiza Nuhu Gudaji

ɓ.         Naja’atu Haruna Saleh

ɓi.        Muhammad Lawal Barista

ɓii.       Maryam Kabir Mashi

ɓiii.     Abubakar Auyo

iɗ.        Nura Sada Nasimat

ɗ.         Zaidu Barmo Katsina da sauransu.   

2.5       Wuraren da Ake Ɗab’in Ƙagaggun Larabci na Hausa

            Da yake marubuta ƙagaggun labarai suna da yawa, kenan wuraren da ake bugawa a kwamfuta ma dole su yawaita. Masu ɗab’i su ne masu fitar da shi a cikin fallayen takardu, a wuraren a kan samu, masu yin bango da sauran dukkanin ayyukan da suka shafi ɗab’i. Kaɗan daga cikin wuraren akwai:

i.          Gidan Dabino Publishers dake kusa da Gidan Ƙanƙara, Sabon Titi Sani Mainagge, Kano.  

ii.         Anka Graphics Fagge, Kano.

iii.       Iya Ruwa Publishers Kano.

iɓ.        Gimbiya Publishers Fagge, Layin Wafa, Fagge D2, Birnin Kano.

ɓ.         Fancy Printing and Publishing Company, Sabuwar Unguwa, Katsina.        

2.6       Wuraren Da Ake Dillancin Ƙagaggun Labarai

            Akwai wurare da dama da ake dillancin littattafan ƙagaggun labarai na Hausa. Daga cikin wuraren akwai:

i.          Sauƙi Bookshop, Ƙofar Maggi, Bayan Banki Layina 2, Kasuwar Muhammad Abubakar Ilimi dake Sabon Gari Kano.

ii.         Alhaji Muhammad Jega Bookshop, Kasuwar Kurmi Kano.

iii.       Nurullah Bookshop, bayan gadar ‘Yan Kura, Kasuwar Sabon Gari Kano.

iɓ.        Mace Mutum Bookshop, Kan Titin Dawaki, daura da Titin Ahmadu Bello, G.R.A., Nasarawa Kano.

ɓ.         Garba Mohammed Bookshop, Kasuwar Sabon Gari Kano.

ɓi.        Nazzy Bookshop, Kasuwar Gama, Brigade daura da Gwagwarwa Police Station, Kano. 

ɓii.       Amintako Bookshop, No. 1 Shamaki Road, Hadejia, Jihar Jigawa. 

 

2.7       Wuraren da Ake Bayar da Hayar Littattafan Ƙagaggun Labarai

            Da yake harkar bayar da hayar littafi, harka ce wadda ta saɓawa duk wasu marubuta, hakan ya sanya ba kowane mamallakin littafi ba ne ke aminta da a bayar da hayar littafinsa. Wannan sai ya sanya galibi a ɓoye ne mata a gidajensu da kuma wasu ɗaiɗaikun shagunan sayar da littattafan ke bayar da wannan haya. Wasu cikin wuraren da ake bayar da wannan haya sun haɗa da: 

i.          Rakiya da ke unguwar Hotoro, Kano

ii.         Hajiya Maryam mai Kunun Aya, Unguwar Hausawa, Kano.

iii.       Aisha mai sayar da takardu dake Tokarawa, Kano

iɓ.        Shagon Gimba mai littattafai, maina huɗu, Ƙaramar Hukumar Nguru, Jihar Yobe.

ɓ.         Isa Mai Kayan Bulawus, kan Titin Ahmadu Bello, Ƙaramar Hukumar Nguru.

 

3.0       Gudumawar Ƙagaggun Labaran Hausa Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasa

            Haƙiƙa yaɗuwar ƙagaggun labaran Hausa waɗanda aka buga a matsayin littafin karantawa; sun bayar da gagarumar gudumawa wajen yaɗa tattalin arzikin ƙasa. Za a yarda da hakan yayin da aka yi la’akari da yadda rayuwar dubban mutane ta dogara ga wannan sana’a, wadda ta nan suke samun ci da sha, da kuma sauran buƙatunsu na rayuwa.

            Kamar yadda aka faɗa, akwai nau’o’in mutane mabambanta waɗanda rayuwarsu kacokan ta dogara a kan wannan sana’a. Don a fahimci bayani na a fili, an kasafta su kamar haka:

3.1       Masu Rubutawa (Marubuta)

            Waɗannan su ne rukuni na farko wajen samar da ƙagaggun labaran Hausa, domin su ne nau’o’’i na mutanen da Allah ya huwacewa basirar tsara labarin da kuma baiwar rubuta shi. Rubuta ƙagaggun labarai baiwa ce ba karantar ta ake ba, domin zurfin ilimin mutum ko matakin karatu ba za su sanya ya zama marubuci ba. Marubuta litattafan Hausa, ta hanyar tsara basirar da Allah Ya fuwace musu ce, suke samar da rubutattun littattafai, wanda daga nan sai a samar da shi, har a kai kasuwa ga masaya. Da wannan abin za su gudanar da al’amuran rayuwarsu na yau da gobe, wato wannan ce sana’arsu. 

3.2       Masu Yin Faifan Littafi

            Su ne waɗanda ke sanya littafin a faifan CD, wato bayan an rubuta shi da keken rubutu ko na’urar rubutu, sai su mayar da shi faifan domin saita shi. Ta wannan hanya ce suke samun abin masarufinsu, bayan sun yi wa littafi wannan faifan na CD.

3.3       Masu Buga Littafi (Masu Ɗab’i)

            Maɗaba’a nan ce wurin da ake buga littattafan ƙagaggun labarai bayan marubuta sun rubuta, sannan an sanya shi a kwamfuta har a yi masa faifai. To daga nan sai a sanya a na’urar ɗab’i wadda za ta fitar da adadin da ake buƙata. Masu aiki a maɗaba’a, suna da ƙaiyadaddan farashi ga dukkanin wani ɗab’i da za su yi wanda ta nan suke samun nasu abin masarufin.   

3.4       Masu Tsara Bango (Coɓer Design)

            Waɗannan rukuni kuwa su ne suke tsara bangon littafi kafin a kai ga buga shi, sawa’un wannan tsarawar suna yi ne da kwamfuta ko kuma da hannu. Irin waɗannan mutane, marubuta kan kawo musu aikin ne sai su bayyana musu tsarin bangon da suke so, kuma su biya su. Ta nan su ma suke samun nasu abin masarufin.

3.5       Masu Yin Faifan Bango (Coɓer Plate)

            Wannan wani muhimmin rukuni ne waɗanda ke dogaro da ƙagaggun labarai wajen tafiyar da rayuwarsu. Aikin wannan jama’a shi ne yin faifan bangon littafi, wato ‘plate’ a Turance. Domin za su ɗauki aikin da aka yi na bangon littafi da kwamfuta sai su mayar da shi cikin faifan. Ta irin wannan hanyar, marubuta ke biyan su kwatankwacin aikin da suka yi musu, to sai su samu ribarsu a ciki bayan sun cire kuɗin kayan aiki.   

3.6       Masu Buga Bango (Coɓer Printers)

            Bayan an tsara bangon littafi, kuma an sanya shi cikin faifai. To abu na gaba shi ne fitarwa, to wannan rukuni su ne masu fitar da bangon littafi. Su kuwa za su yi amfani ne da tsarinas na cikin faifai su fitar da adadin yadda suke so. Ta wannan hanya ce suke samun kuɗaɗen gudanar da al’amuran rayuwarsu nay au da gobe. 

3.7       Masu Sayarwa/Dillalai Ko Diloli           

            Bayan aikin littafi ya kammala, marubuci kan sauƙi littafi domin sayarwa. To marubuci kan ɗauki littafin ne ya kai wa masu samarwa, wato diloli waɗanda a gun su ne ƙananan ‘yan kasuwa za su je su saya domin su ma su sayarwa makaranta. To marubucin littafi yakan bayar da wani ayyanannen farashi na shi, su kuma sai su ɗora ribarsu, wadda da ita suke riƙe wannan kasuwanci nasu.  

 

3.8       Masu Sayar da Ɗai-Ɗai

            Wannan rukuni kuwa, su ne ƙananan ‘yan kasuwar da suke sayowa a wurin manyan diloli sannan su zo su kasa suna sayarwa masu karantawa. Irin wannan nau’i, sukan sayowa a cikin farashi mai rahusa, sai su ƙara wani abu ta la’akari da kuɗin dakon da za su cire da ɗawainiyar da suka yi da kuma abin da zai biyo baya na riba. 

3.9       Masu Dako

            Wannan rukuni kuwa, jingunuwarsu ga wannan sana’a ita ce dako. Wato su ne masu jigilar littattafan ƙagaggun labarai tun daga maɗaba’a zuwa gun marubuci, ko diloli, ko ƙananan ‘yan kasu, ko kuma ma zuwa wani gari makusanci ko mai nisa. A irin wannan jigilar ce suke samun abin masarufinsu wanda suke riƙe rayuwarsu da shi. 

3.10     Masu Bayar da Shi Haya

            Wannan wani nau’i ne na mutanen da ke bayar da hayar littattafan sawa’un a shagunansu ne ko kuma mata ne a gidajensu. Amma mafi yawan masu bayar da wannan haya mata ne. Wato bayan sun bayar kan wani farashi za a karanta a dawo musu da shi cikin ƙidaddigun kwanakin da suke bayarwa.

            Masu bayar da haya, sukan sayo duk duga ɗaya a kan kuɗi N 150, N 200, N 250, ko kuma N 300. Idan sun kawo shagunansu ko gidajensu, sukan bayar da shi haya a kan           N 40 tsawon awa ashirin da huɗu (24 hrs), idan ba a samu matsalar riƙewa daga gurin wasu ba, to a sati guda sukan fitar da kuɗinsu, har ma su samu riba, musamman waɗanda suke ƙasa da ɗari uku (N 300).

3.11     Masu Turawa a Wayoyi

            Su kuwa waɗannan masu samun abin masarufinsu ne ta hanyar tura wa mutane sautin murya na waɗannan littattafai a wayoyinsu ko wani abin saurare kamar radiyo mai amfani da memory. Irin waɗannan ana karance labaran ne tsaf, sannan a rinƙa turawa domin saurare maimakon karantawa daga cikin littattafai. To a yayin da masu buƙata suka je domin a tura musu, sukan bayar da wani kuɗi da aka ƙayyade da wannan suke mayar da kuɗinsu har su ci riba.

3.12     Masu Shagunan Haya

            Waɗannan kuwa su ne irin waɗanda ke gina shaguna domin bayar da su haya, cikin waɗanda ke karɓar hayar kuwa akwai masu ɗab’i, dilolin littattafai, masu sayar da ɗai-ɗai da masu haya, sai kuma sauran waɗanda suka jiɓinci wannan sana’a, kuma suka karɓi hayar wurin sana’ar. Ta irin wannan hanyar ce masu hayar shaguna suke samun kuɗaɗen shiga yayin da suka bai wa masu harkar littafi hayar shaguna.  

 

4.0       Kammalawa

            Kamar yadda ya gabata a wannan takarda an bibiyi ɓangaren ma’ana da kuma taƙaitaccen tarihin samuwar ƙagaggun labarai na Hausa. A cikin takardar, an bayyana kamfanoni/hukumomi da gwamnati ta kafa a matakai daban – daban domin samar da waɗannan littattafai, sannan aka bayyana irin gudumawar da suka bayar wajen samar da littattafan. A cikin takardar dai, an bayyana ƙungiyoyin da aka samar domin wallafa ƙagaggun labarai na Hausa, haka zalika da irin rawar da suka taka. Sannan aka bayyana masu ƙagawa, da masu bugawa da kuma masu dillancinsu. Takardar, ta bayyana nau’o’in mutane guda goma sha biyu da rayuwarsu ta rataya a wannan sana’a, wanda ya kasance su suke cicciɓawa wajen samarwa da yaɗa littattafan ƙagaggun labarai, kamar yadda su ma da wannan sana’a suka dogara wajen gudanar da al’amuran rayuwarsu na yau da gobe. Kenan, a takardar an fahimci lalle ƙaga labari da bugawa sana’a ce da take da muhimmanci a wannan ƙasa, ta fuskar gwamnati/hukumomi da ɗaiɗaikun mutane, domin sana’a ce da ta kewaye wani sashe na rayuwar al’umma, kuma ta zama maɓuɓɓuga ta yaɗa aikin yi da arziki. A shawarce, ya kamata gwamnati ta ƙara inganta wannan sana’a ta hanyar kakkafa masana’antu da horas da masu wannan sana’a ilimummuka da dama domin ƙara inganta wannan sana’a.                 

Manazarta

Tuntuɓi masu takarda.

Post a Comment

1 Comments

ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.