Takarda Wadda Aka Gabatar A Taron Ƙara Wa Juna Sani, Na Jami'ar Jihar Kaduna, Daga Ranar 28th Zuwa 30th Ga Watan Maris, Shekarar 2019.
Kishi Kumullon Mata:
Nazarin Kishi Cikin Fina-Finan Hausa
Ibrahim
Baba (Nayaya)
Ma'aikatar
Ilimi ta Ƙananan Makarantun Sakandare, Ƙaramar Hukumar Nguru,
Jihar Yobe.
Shugaban
Ƙungiyar Nguru Writers' Association of Nigeria
07066366586,
08125351694.
Kibɗau:
ibrahimba182@gmail.com
Hassan
Musa
Sashen
Nazarin Harshen Hausa, Kwalejin Ilimi ta Umar Suleiman dake Gashua, Jihar Yobe.
08064890499
hassanmusa170
@gmail.com
Saminu
Sabo
Sashen
Nazarin Harshen Hausa
Kwalejin
Shari’a da Addinin Musulunci ta Atiku Abubakar, Nguru Jihar Yobe 08062563939
Kibɗau: saminusabo3467@yahoo.com
1.0
Gabatarwa
Fina-finan Hausa wata tsararriyar hanya ce mafi sauƙi wadda ake bayyana
halayya da ɗabi'u na al'umma
cikin fasaha domin isar da saƙo ga wanda ya ji ya gani. Tun lokacin
da fina-finan Hausa suka samu ɓulluwa a tsakanin Hausawa, wato ƙarshen ƙarni na ashirin 20,
masu rubutawa da tsarawa da shiryawa suka ta ƙoƙarin bayyana al'adu
iri daban-daban da halayyar zaman al'umma. Idan muka dubi fina-finan Hausa yan
bana bakwai, za mu iske cike suke da al'adu daban-daban na al'umma, da kuma ɗabi'u na rukunonin
mutane da halayyarsu. Misali, tun lokacin da finan-finan Hausa suka fara
yawaita a tsakanin al'ummar Hausawa, masu tsarawa da shiryawa sun mayar da
hankali ne wajen shirya fina-finan da suka shafi zamantakewar auratayya, tun
daga kan neman aure, har kawo yin sa da kuma irin zaman da ake yi bayan aure,
sawa'un mai daɗi ne ko akasin sa.A
irin wannan shirye-shirye na fina-finai ne, sai ake shirya fina-finan da suka shafi
kishi tsakanin ma'aurata, wato mata suna kishi tsakaninsu da junansu a matsayin
matan mutum guda, ko kuma samari su rinƙa kishi tsakanin waɗanda suke neman
budurwa ɗaya, ko kuma yan mata
masu son saurayi guda.
A
cikin wannan takarda, an tattaro fina-finai guda goma sha biyu waɗanda aka naƙalto abubuwan kishi
na tashe-tashen hankula da suka wakana tsakanin kishiyoyi, munin kuwa, ya afku
ne tsakani kishiyoyin ko kuma tsakaninsu da mazajensu ko da 'yan'uwan miji ko
uwar miji.
1.1
Ma'anar Fim
Gidan
Dabino da wani (2004:332)sun bayyana fim da
cewa, "Tantagayyar kimiyya da fasaha ce kuma rayuwar ɗan'adam ce ake
nunawa. Fim yana ɗauke da tarihi da ɗabi'un jama'a da
muhallinsu da abincinsu da kuma suturarsu musamman bisa harshensu da tsarin su
na rayuwa da hanyoyin tunaninsu da kuma falsafar rayuwar mutanen da ake yin fim
ɗin su. Har ila yau,
fim hanya ce ta sanarwa da ilimantarwa da jan hankali da nishaɗantarwa da faɗakarwa da yaɗa manufa da
tallatawa".
'Yar'aduwa (2007:30)ya yi na shi
ta'arifin da cewa, "Fim wata hikima ce ta hoto mai motsi da take ɗauke da mutane, wato
hotunansu maza da mata, yara ko manya, ko kuma ma wanin mutane, wanda aka ɗauka ta hanyar yin
amfani da na'urar ɗaukar hoto ta
musamman, tare da bai wa mutane (kowannensu)damar tafiyar da wasu
ayyuka ta fuskar kwaikwayo ko wanin sa, a wani ɗan lokaci da aka keɓe wanda shi wasan
kwaikwayon (fim)yake ɗauke da wani saƙo na musamman kan
nishaɗi da gargaɗi da wa'azi da soyayya da tarihi ko wanin
haka, zuwa ga al'ummar duniya".
Idan
muka yi la'akari da waɗannan ma'anoni guda
biyu, za mu iya kallon ma'anar da fim a taƙaice da cewa, wata keɓantacciyar hanya ce
tsararriya ta sarrafa hikima da fasaha a aikace; wanda ake amfani da na'urar ɗaukar hoto mai motsi
da sautuka, domin isar da wani saƙo na musamman ga
al'umma, ta hanyar zayyano matsaloli da hanyoyin magance su ko uƙubar wanda ya munana.
1.2
Asali da Samuwar Fina-finan Hausa
'Yar'aduwa (2007:30) ya bayyana samuwar
fina-finan Hausa, abu ne da ya faru a ƙarshen ƙarni na ashirin (20). Amma farkon abin da
ya ɗora tubalin samuwar
sa shi ne wasan kwaikwayo. Kuma shi kan sa wasan kwaikwayo ya samu ne bayan
Turawa mulkin mallaka sun kafu, kuma har sun yi nisa wajen shimfiɗa tsare-tsare da suka
shafi ilimi da tsarin mulki da sarauta.
Binta (2008:11-16) ta bayyana tarihin samuwar fina-finan Hausa dubi da
nazarce-nazarce daga mawallafe-wallafen masana, misali Bargery (1934), Chamo
(2005:36), Inuwa (2009) da Garba (2009), inda yawancinsu bakunansu sun daidaita
da na juna ta fuskar asalin fina-finan Hausa. Misali, majigi hoton farko da
Hausawa suka fara cin karo da shi kafin sauran hotuna da ake nunawa. An fara
nuna majigi ta hanyar sanya allon kallo a saman mota.
Binta (2008:15 – 16), bayan tattara bayanan masanan da ta yi game da
samuwar fina-finan Hausa, sai ta nuna cewa, a cikin shekarar 1998 ne masu
shirya fina-finai suka yunƙuro suka kafa ƙungiya ta masu wannan
harkar domin su yi magana da murya ɗaya. Tun daga wannan lokaci sana 'ar shirya
fim ta bunƙasa, kuma ga shi ƙofar shiga wannan
sana'ar a buɗe take, sai aka dinga
tururuwa cikin ta maza da mata, saboda amfanin da ake ganin masu wannan sana'a
sun fara samu. Gaskiya ne, wannan sana'a ta samar wa matasa da dama aiki, maza
da mata sun zama 'yan wasa da masu shiryawa da masu ba da umarni da masu ɗaukan nauyi, masu waƙoƙi da masu kwalliya da
masu ɗaukan hoto da 'yan
kasuwa da sauransu. Wannan sana'a ta haɗa mutane iri-iri, kuma kowa yana da tasa
wadda ta shigo da shi wannan sana'a. Da wannan sana'a suka yi mata rajista suka
sa mata suna Kannywood Industry, wato masu shirya fina-finan Hausa. A ƙarƙashin wannan
Industiri akwai kamfanoni da suke shirya fina-finai kuma cibiyar wannan ƙungiya Kano.
Kamfanoni sun haɗa da Kaduna, Abuja,
Sakkwato, Maiduguri da sauran wurare.
2.0
Ma'anar Kishi
Kishi suna ya tara, domin a kan bayyana shi ta hanyoyi daban-daban,
kamar yadda ake masa kallo ta fuskoki da dama, kuma kowa da irin yadda yake
sarrafa na shi/ta a aikace.
Kishi tsakanin kishiyoyi shi ne abu mafi muni kuma wanda ya zama ruwan
dare a yau, wanda kuma a kan sa ne muhallin wannan takarda.
2.1
Ma'anar Kishi
Masana da dama da masu nazari sun bayyana ma'anar kishi a cikin
kundayensu. Misali, Rabi (1998) a cikin Binta (2009:92) ta bayyana cewa
"Kishi wani hali ne da mutum yake tsananin son abu ba tare da tarayya da
wani ba".
Garba (1998:334) ya kawo ma'anar kishi da cewa, "Kishi cikin jikin
mutum yake, sai dai kuma mata sun fi nuna shi da aiwatar da shi. Mata na da
hanyoyin nuna kishi kanar ta magana, da habaici da karin magana da lugude da waƙa, ko ta shanti ko ta
niƙa
ko zungurar wani abu inda kishiya take, yadda za ta farga da ita ake, ko wata
shewa, ko dai wani abu makamancin waɗannan".
Shi
kuwa Abbas (1999:1) cewa ya yi, "Kishi shi ne sosuwar zuciya da ɓacin ran da suke kawo
fushi a dalilin tarayyar da wani ya yi da wani a kan abin da wanin ya keɓanta da son sa, ko
mallakarsa".
A
ta'arifin Bakura (2003:91) ya bayyana kishi da cewa "Wata hanya ce ta
gwagwarmaya dake tattare da zargi da tuhuma da saɓani da rashin jituwa da husuma da
mugun nufi, domin ƙoƙarin kare keɓantacciyar ƙauna ga abin so, ba
tare da yin tarayya da wani ba".
CNHN
(2006:247) kuwa ta bayyana kishi da cewa, "Rashin jituwa ne da nuna ƙyashi irin wanda
matan dake auren mutum ɗaya suke yi wa juna.
Ko kuma nuna gaba ga wani a kan wani abu na kirki da mutum ya sa a gaba don
cimma buri".
Idan
aka dunƙule waɗannan ma'anoni, za a ga kishi ya shafi tarayyar mutum
biyu ne a wurin mutum guda kuma a matsayi guda, ta yadda kowa zai yi ƙoƙarin ganin shi ne a
gaba, ko kuma a sama. Wanda hakan kuwa zai kawo rikice-rikice da hayaniya da
musguna wa juna.
2.2
Abubuwan Dake Kawo Kishi
Kishi ba abu ne da ke zuwa kai tsaye ba, dole ne yana da wasu sabuba
dake janyo shi ƙarshe ya zaunar da shi a zuciyar mai yi. Ta la'akari da
ma'anonin da suka zo a baya, za mu ga kishi na da sabuba kamar haka:
2.2.1
Tsananin So
Wato
ta yadda wani zai sallama zuciyarsa ga wani, har iya kasance ba ya ganin
laifinsa, kuma ba ya buƙatar wani ya kusanci wannan abu ko da da wasa ne.
2.2.2
Tarayya A Kan Abu Guda
A
duk lokacin da wani ya haɗa soyayyar mata biyu
a zuciyarsa, to waɗannan mata za su
kasance cikin kishin juna sakamakon tarayyar da suka yi da juna a zuciya guda.
2.2.3
Rashin Jituwa da Ƙyashi
Wannan
ma na janyo kishi, musamman tsakanin matan mutum guda, domin kowacce za ta rinƙa bibiyar yar'uwarta
sakamakon wannan rashin jituwar, sannan kuma ƙyashi da mugunta ko
mugun nufi zai riƙa biyo baya, saboda wancan rashin jituwar.
2.3
Rabe-raben Kishi
Masana sun bayyana kishi kan iya zama kyakkyawa ko mummuna, kuma
dukkansu ana iya gane su ta irin yanayin da aka bayyanar da su.
Mohammed (2011:105-106) ya bayyana cewa, kyakkyawan kishi ana aiwatar da
shi ne domin amfanin kai ba tare da cutar da abokin kishi ba. A nan ne akan
samu irin kishin da ake kira 'Kishin zuci'. Misali, ta fuskar neman ilimi a
tsakanin masu ƙoƙarin neman sa, kowane daga cikinsu yakan yi ƙoƙarin ya ga ya fi kowa
ƙoƙari, ba tare da cutar
da kowa ba. Haka ko ta fuskar sana'a ne za a ga kamfanoni masu yin abubuwa iri ɗaya, kamar sabulu ko
magi ko katifa ko gadaje da sauransu, za a ga kowane kamfani da irin ingancin
abin da ya samar. Saboda haka sukan yi kishi a tsakanin su ta yadda za su samu
karɓuwa ga jama'a, wanda
duk ya fi kishi to za a ga kullum yana daɗa inganta sana'ar tasa ce ba tare da ya cutar
da abokin hamayyarsa ba.
Sannan akwai irin kishin daga jin sunan; ba abin so ba ne. Kishi ne da
ake bayyana shi ta hanyar cutar da abokin yi, ko a nuna masa ba a ƙaunar sa. Irin wannan
kishi, shi ne aka fi samun sa a tsakanin mata.
Ana
samun kishi a tsakanin mata biyi waɗanda suke mijinsu ɗaya. Sannan ana samun
kishi a tsakanin matar wa da matar ƙani, wato faccala.
Haka ma kuma ana samun kishi tsakanin uwar miji da matar ɗa. Akwai kuma kishin
dake tsakanin yayye ko ƙannen miji da matar ɗan'uwansu.
Binta (2009:94 – 118) ta yi bayani game da rabe-raben kishi, inda ta
kasafta su zuwa gida uku, kuma kowanne ta yi bayanai da buga misalai gwargwadon
iko. A dunƙule, ta kasa kishin kamar haka:
2.3.1 Kishi tsakanin kishiyoyi, wato irin
kishin dake tsakanin matan mutum guda. Irin wannan kishin ya faru a fina-finai
da dama kamar Rikicin Cikin Gida (2018) na kamfanin Ɗan Hajiya Film
Production Kano.
2.3.2 Kishin uwar miji, irin kishin da uwar
miji ke yi ga matar ɗanta. Irin wannan
kishi ya faru a fim ɗin Uwar Miji da
sauransu.
2.3.3 Kishin faccala, wato irin kishin dake
tsakanin matan wa da ƙani a junan su.Irin wannan kishin ya faru a fim ɗin Ƙawayen Amarya (2018)na kamfanin 2 Effect
Empires Kano.
3.0
Yanaye-yanayen Kishi Tsakanin Mata a Cikin Fina-finan Hausa
A
rayuwar zahiri, kishi kan sanya mata aikata abubuwa daban-daban na halaka wanda
a ƙarshe
yake zama sababin jefa rayuwar kishiyoyi ko mazajensu ko kuma su ɗin a karan kansu
cikin mawuyacin hali. Idan aka leƙa ga fina-finan Hausa
ma za a iske cike suke da fina-finai masu ɗauke da irin waɗannan halaye na kishi tsakanin mata. A
nan, za a kawo wasu fina-finai da kishi ya bayyana ƙarara da kuma irin
abin da mace take aikatawa a sakamakon wannan kishi, sawa'un a kan kishiyarta
ce, ko 'ya'yan kishiya, ko maigida ko kuma wani cikin dangin miji, musamman
mahaifiyar miji.
3.1
Kishi kan sa mace ta kashe kishiyarta
A
rayuwar zahiri tsananin kishi kan sanya mace kashe kishiyarta ta hanyar amfani
da makami ko asiri ko kuma duka kawai. Haka abin yake a cikin fina-finan Hausa.
A cikin fim ɗin Akushi (2018) na
kamfanin Oscar International an ga yadda Lami ta hallaka kishiyarta ta hanyar
amfani da magani. Lami wadda suke auren Malam tare da kishiyarta, ta rasa
haihuwa wanda kishi ya hana ta nutsuwa, a ƙarshe kuma ta halaka
ta.
3.2
Kishi kan sa mace ta yi wa kishiyarya asiri, ta shiga duniya
A
cikin fim ɗin Matar Uba (2018)
na kamfanin Halifa Abubakar Inɓestment Nigeria Limited, an ga yadda Asabe ta yi wa
Mariya asiri ta shiga duniya. Malam Nasidi shi ne mijinsu, amma tsananin kishi
ya sanya Asabe ta je wajen Malami domin neman maganin da za ta yi wa Mariya
asiri ta halaka ta. Ga yadda suka yi da Malamin:
Malam: Ai ni ma ba cewa na yi zai rabu da ita ba,
ita za ta rabu da shi, za mu kore ta ta bar gidan ta shiga duniya har abada ba
wanda zai ƙara jin labarin inda take, kuma har abada ba za ta dawo
ba.
Asabe: To ai ni Malam a daidai na, ai in wannan
ita kenan sharaɗin, na amince. Mata
ta shige min rayuwa, haka kawai ta same ni da mijina ta raba ni da shi.
A
nan, mun ji yadda aka yi, kuma ƙarshe hakan ta faru, inda ta yi asirin
da ya sanya Mariya ta shiga duniya, ba a ƙara ganin ta ba sai
labarin mutuwarta aka ji.
3.3
Kishi kan sa mace ta kashe uwar mijinta
Kamar yadda aka sani, kishi kan sanya mace kisan uwar miji. Ya zo a
cikin fim ɗin Dalal (2018) na
kamfanin A. Y. I Uniɓersal Motion Pictures
Kano inda hakan ta faru. Hafsat matar
Jamil ta haɗa kai da mahaifiyarta
da ƙanin
mahaifiyar Jamil, wato Alhaji Bala domin ganin bayan mahaifiyar Jamil ɗin. Mahaifiyar Jamil
ta sanya ya ƙara aure sakamakon rashin mutunci da tsatsube-tsatsuben
da Hafsat da mahaifiyarta Hajiya Mama suke yi don ganin sun mallake shi. Haka
kuwa aka yi, amma bayan ya yi auren sai da suka rinƙa asirai, ƙarshe sai da kishi ya
sanya ta kashe uwar Jamil ɗin da goyon bayan Hajiya Mama da Alhaji Bala.
3.4
Kishi kan sa mace ta kira danginta/ƙawayenta domin dukan
kishiyarta
Daga
cikin abin da zuciyar mace ke raya mata, bayan mijinta ya ƙara aure, akwai dukan
amarya, wannan kuwa ya faru a fim ɗin Dalal (2018) ɗin, bayan Jamil ya ƙara aure, sai da
Hafsat ta kira ƙawayenta/'yan'uwanta domin dukan matar da ya auro. Ga
yadda suka yi:
Ƙawa 1: Ai ni haushinki
nake ji, ya za a yi a ce kina zaune duk kishin kin nan wai har mijinki ya yi
aure ya shigar da amaryar gida kina zaune a falo ba ki ɗauki wani mataki ba,
kin ban kunya wallahi.
Hafsat: To ya zan yi? Ai ba kwa nan ne, ko ba
gaskiya ba?
Ƙawa 1: To ai
yanzu ga mu mun zo.
Ƙawa 2: Ai wannan cin
mutunci ne da cin amana.
Hafsat: Ai dama na sani, daman jira nake ku zo mu
afka musu.........
Ƙawa 3: Ai ga mu mun zo,
sai ki tashi yanzu mu afka musu.
Hafsat: Abin da nake ao, kirawo min su Falmata,
kafin su zo mu je mu afka musu, duk abin da ta tafasa ta ƙone.
Haka
kuwa aka yi, domin daga nan sai suka nufi ɗakin Amaryar inda suka rufe ta da duka bayan
ta fito daga ɗakin.
3.5
Kishi kan sanya mace ta daina yi wa mijinta biyayya da kyautatawa
Mace
idan ta kasance ma'abociyar kyautatawa da ladabi ce ga mijinta, to a sakamakon
kishi zai sanya su samu saɓanin da za ta daina yi masa dukkanin biyayya da ladabi da
kyautatawar da take masa a baya.
Fim ɗin Lubna (2018) na
kamfanin Ƙalarawi Enterprises ya nuna hakan, yayin da Ibrahim ke
zaune lafiya da matarsa, amma sakamakon ya nuna mata zai ƙara aure sai da
kishin ta ya bayyana, har ta canja masa a yanayin mu'amala da kyautatawa.
Ibrahim: Tun lokacin da na ce zan ƙara aure shi kenan
kika bi kika canja.
Mata: Me ka gani? Ni ba komai.
Ibrahim: A'a da komai, walwala ta canja,
clearing ya canja, akwai abubuwa da yawa da kike min a gidan nan kin daina su.
Kai amma kina da zafin kishi!
Mata: Ai kishi dole ne, duk macen da ka ga ba ta
da kishi to wallahi ba ta son mijinta. Amma kishi ya zama dole, abin da kake so
dole ka yi kishi..
A
nan, mun ga yadda kishi ya janyo ta daina kyautata wa mijinta, walwala ta
sauya, ladabi ya sauyu.
Fim ɗin Matar Mijina
(2018) na kamfanin Al-Rahuz Film Production Kano, an ga yadda Jalila ta sauya
mu'amalarta da mijinta a sanadiyyar ya ce zai ƙara aure, inda suna
zaune cikin zaman lafiya da walwala, amma da ya zo da maganar aure sai matsala
ta nemi kunnowa.
Adam: Ya za ki ji idan aka ce miki zan ƙara aure? (Bayan abin
da ya bayyana a fuskarta na damuwa da kiɗimewa). Ya ya na ga duk jikinki ya yi sanyi?
Jalila: Ka ga duk zaman lafiyar da muke, ka ga duk ƙaunar junan dake
tsakan na da kai, da zarar ka ƙara aure za ka neme su ka rasa.
Adam: Ban gane me kike nufi ba!
Jalila: Ina nufin zan buɗe wani sashi na daga
Jahannama! Wallahi da faɗuwar gaba za ka rinƙa shigowa gidanka.
Wannan ya nuna a baya suna zaman lafiya, amma sakamakon maganar ƙarin aure da ya yi
mata, sai ta furta waɗannan kalamai.
3.6
Kishi kan sa kishiyoyi rikici a cikin gidan su, su rinƙa faɗa a junansu
Abu
mafi sauƙi da matan da suke auren mutum guda suke yi shi ne faɗa a koyaushe. Fim ɗin Rikicin Cikin Gida
(2018) na kamfanin Ɗan Hajiya Film Production ya nuna irin wannan kishi, inda
A'isha da Maryam waɗanda matan Sadiƙ ne suke faɗa a junansu a
koyaushe.
Bayan Maryam ta ɗebo ruwa ta watsa wa
A'isha wadda ke kwance a kan doguwar kujera a falo, sai A'ishan ta miƙe tsaye.
A'isha: Ni kika watsa wa ruwa?
Maryam: An watsa miki.
A'isha: Lalle kin yi kuskure, wallahi sai kin yi
nadamar abin da kika aikata a jikinki.
Maryam: Ke da Allah dakata! Wacce take faɗa a baki ba za ta iya
aikatawa ba, ke kin san tsohuwar kuka ta wuci runguma wallahi sai dai sara.
A'isha: Haka kika ce?
Maryam: Ƙwarai kuwa.
Sai
A'isha ta ɗauki kwalba ta kwaɗa wa Maryam a ka, nan
take faɗa ya kaure a
tsakaninsu. A taƙaice dai, kishi kan sanya irin wannan faɗa a kowanne lokaci,
ta yadda ba wani sauran zaman lafiya a gidan.
3.7
Kishi kan sa mace ta rinƙa yi wa mijinta
rashin kunya, ƙarshe ma ta iya lalata auren ta
Sau
da dama idan mace ta san mijinta yana shirin ƙara aure, to fitsara
da rashin kunya ce suke fara biyowa baya, ƙarshe ma auren su ya
lalace sakamakon irin rashin kunyar da take yi masa. Irin wannan al'amari ya
faru a fim ɗin Mubeenah (2017) na
kamfanin Mai Shadda Inɓestment, inda
Mubeenah ta ɗauki aniyar cin
zarafin mijinta a yayin da ya zo mata da maganar ƙarin aure.
Adnan: Bai kamata 'ya'yanmu su gane cewa akwai
wata matsala tsakaninmu ba, ko kaɗan ba ni da niyyar na cutar da ke ko na wulaƙanta ki, ba wai na yi
shi da niyya ba ne.
Mubeenah: Dan Allah ka dakata min! Kana so ka
ce min yarinyar ce ta janyo ka ta ce lalle sai ka aure ta? Kana so ka ce min ba
ka taɓa furta mata kana son
ta ba kenan?
Adnan: Ni fa ban ce haka ba, amma ina so ki
fahimce ni, kuma ina so ki yi min kyakkyawan zato.
Mubeenah: Ka ga dan Allah ka yi haƙuri kar ka min wata
lakca ba abin da za ka faɗa min na fahimta. Don
haka ka je ka yi duk abin da ka ga dama, amma ina so ka sani, ni ban isa na
hana ka abin da ka ga dama ba, amma idan ka yi kuskuren yin aure, wallahi tallahi za ka yi nadama, za
ka ga kuma abin da zai biyo baya.
Haka
al'amarin ya faru, domin bayan auren ta yi ta fitina har sai da ta kai ta
lalata rayuwar auren ta hanyar saki, inda suka rabu.
3.8
Kishi kan sanya kishiya ta kira kishiyarta da karuwa
Bayan faɗa dake afkuwa
tsakanin kishiyoyi, haka akwai faɗar baƙaƙen maganganu masu
muni kamar ambatar kishiya da karuwa. Fim ɗin Rikicin Cikin Gida (2018) na kamfanin Ɗan Hajiya Film
Production ya zo da hakan, wato yayin da Maryam ta gyara falo a ranar girkinta,
sai A'isha ta zo ta kwanta.
Maryam: To tsohuwar kilaki! Sai ki tashi ki fita
daga falon nan saboda yau ba ke kika gyara falon ba, ballantana ki zo ki wani
kwanta ki baje, sai ki bari lokacin da kika yi sai ki zo ki kwanta.
3.9
Kishi kan sanya mace ta rinƙa zargin mijinta
Sau
da dama mace idan mijinta ya yi yunƙurin ƙara aure, to wannan
mat za ta koma sae-sae da zargin mijin nata a kan munanan halaye. Ya zo a cikin
fim ɗin Halin Kishi (2008)
na kamfanin Global Time Moɓies yayin da Abdallah ya yi yunƙurin ƙarin aure, sai kishi
ya sanya matarsa Zainab ta rinƙa zarginsa da fasiƙanci. A gefe guda
kuma ta rinƙa yin barazanar kisa ga Zara'u (Budurwar mijinta) matuƙar ba ta rabu da
mijin nata ba.
3.10
Kishi kan sanya mace ta rinƙa yi wa kishiyarta ƙage da sharri a gaban
mijinsu
A
lokacin da mutum ke auren mace sama da ɗaya, kuma kishi ya sanya su rashin zaman
lafiya, to kowacce za ta rinƙa ɓata kishiyarta a gaban mijinsu. Ya bayyana a
cikin fim ɗin Matar Uba (2018)
na kamfanin Halifa Abubakar Inɓestment Nigeria Limited, inda Malam Nasidi ya zauna yana
jimamain rashin sanin inda Mariya ta shiga, sai Asabe take mata ƙage.
Malam Nasidi: Yau fa kwana uku ba
mu ga Mariya ba, ba mu san halin da take ciki ba har yanzu.
Asabe: Kai kake ta da hankalinka, ni fa ina ganin
Mariya gajiya ta yi da zaman gidan nan, tana so ta ga duniya, duniya ta ganta
ta gogu, ta buɗe ido, idonta ya yi
tar a duniya.
Malam Nasidi: Dakata, Mariya ba
za ta yi haka ba, na san ta sarai.
Asabe: Ba a shaidar mutum, mutum ai shege ne, Malam
mutum shege ne........
A
nan, duk da Mariya ba ta nan, ta ma ɓata, amma sai ga shi kishi ya sanya Asabe
aibantata; ta hanyar yi mata ƙage.
3.11
Kishi kan sanya kishiya ta rinƙa azabtar da 'yar
kishiyarta
Sanin kowa ne, kishi kan haddasa ƙiyayya da gaba da
kuma tsana. Haka zalika, kishi kan sanya mace ta rinƙa azabtar da ‘ya’yan
kishiyarta. A cikin fim ɗin Matar Uba (2018)
na kamfanin Halifa Abubakar Inɓestment, an ga yadda Asabe ta rinƙa azabtar da Amira
'yar gidan Mariya; bayan ta yi wa Mariya ɗin asiri. Ta rinƙa ɗaura mata talla, kuma
idan ba ta sayar ba ta rinƙa jibgar ta, ba isasshen abinci, ba
barci wadatacce, wanda a ƙarshe sai da K.B
saurayinta ya yi sanadiyyar tafiyar ta bariki.
3.12
Kishi kan sanya kishiya ta kashe mijinta
A
duk lokacin da kishi ya tunzura mace, to za ta rinƙa yin saƙe-saƙen hallaka mijin
nasu, domin a nata tunanin shi ya jefa ta cikin wannan halin. Wata kuwa za ta
yunƙuro
domin kisa amma ba da gaske ba, sai dai idan akwai tsautsayi, sai kisan ya
afku. Fim ɗin Mariya (2018) na
kamfanin Mai Shadda Inɓestment Limited an ga
yadda hakan ta faru. Mariya, wadda aka yi mata auren dole da Sarkin Noma Malam
Sada ba tare da tana son sa ba. Shi kuma ya kasance mai auri saki ne, sannan
yana da 'ya'ya. A haka aka yi auren, wanda bayan yin sa Mariya ba ta ba da kai
ga Malam Sada ba.
Wata
rana ta aika a sayo mata maganin ɓera domin ta zuba masa a abinci ya ci ya mutu,
a dalilin ba ta son shi sai bayan ta zuba, tausayi, da imani ya zo mata, sai ta
ɗauka ta je za ta
zubar. Ashe duk abin da yake faruwa a idanun Talatu (uwargidan Malam Sada) ake
yi, inda ita kuma tuni ta faɗa kogon kishi da Mariya. Ganin Mariya za ta zubar da
wannan abinci mai guba, sai ta zo ta karɓe abincin, ta aika masa, saboda kishi, alhali
ta san da guba a ciki. Malam Sada bayan ya ci abinci, cikinsa ya murɗe har ya mutu, sai
Talatu ta koma tana cewa ai Mariya ce ta kashe shi. Bayan Shari’a ta yi zurfi,
gaskiya ta bayyana cewa Talatu ce ta kasha shi saboda kishi.
3.13 Kishi kan sa kishiya ta tayar da
hankalin mijinta, ta haifar da rikici a gidan mijinta, a kasa zaune a kasa
tsaye, kamar yadda hakan ya afku a fim ɗin Ɗakin Amarya (2016),
inda Talatu ta rinƙa tayar da fitintunu wanda har a ƙarshe ta yi yunƙurin ƙona gidan gaba ɗaya. Sannan ta rinƙa ƙirawo ƙaninta tare da 'yan
daba, suka rinƙa hautsina gidan da farfasa kayan kallo da kujerun gidan.
3.14
Kishi kan sanya mace ta rinƙa haukar ƙarya
Mace
takan yi haukar ƙarya da da'awar aljanu sun kama ta yayin da mijinta ya
nemi ƙarin aure. Ya zo a fim ɗin Hawainiya (2014) inda Jamila ta rinƙa haukar ƙarya yayin da mijinta
Shu'aibu ya zo mata da batun ƙarin aure.
3.15
Kishi kan sanya mace ta rinƙa tozarta mijinta da
yi masa gori
Kaɗan daga cikin aikin
mace shi ne tozarta miji yayin da ta ba shi kuɗi ko suka haɗa jari domin yin
kasuwanci ko kuma idan ta yi masa wata alfarma, muddin idan ya zo mata da batun
ƙarin
aure, to za ta rufe idanuwanta ta rinƙa cin zarafinsa da yi
masa gori.
Ya
zo a fim ɗin Mu Zuba Mu Gani
(2018) inda Sakina ta fara goranta wa mijinta Ahmad jarin da ta ba shi a
dalilin ya zo ƙara aure. Bayan ta same shi a falo yana shirye-shiryen
fita ɗaurin aurensa kamar
yadda aka gaya mata, sai ya yi ta ƙoƙarin nuna mata ba
wurin kowa zai je ba, ƙarshe ta nemi mintuna biyu a wurinsa. Bayan ta juya za ta
shiga ɗakin girki, sai ya
ce:
Ahmad: Wayyo uwargidana.....
Sakina: (Ta juyo da mamaki a fuskarta)
Uwargida kuma?
Ahmad: Kuma Amaryata, ki bari na ƙarasa zance, ke an
fara magana ba a ƙarasa ba sai ki shigo.
Bayan ta tafi zuwa kicin, ta dawo hannunta a baya, ta nufo shi, sanna ta
nemi ya rufe idanuwansa, sannan ta watsa matsa manja a babbar rigarsa. Daga
cikin maganganun da suka yi akwai:
Ahmad: Ban gane ba, ya aka yi na yaudare ki? Me
kike nufi da haka?
Sakina: Kar ka yi tsammanin Allah bai yoni asirinka
ba, duk abin da kake Allah ya tona asirinka na sani. Wato an ɗaura auren ka yau
kana sauri za ka tafi wajen dinner. To bari na faɗa maka, wallahi tallahi ba za ka cuce
ni ka ce na ba ka kuɗi mu yi kasuwanci ka
je ka yi aure da shi ba.
Haka
dai rikici ya ɓalle tsakaninsu, har
bayan an yi auren ta ci gaba da goranta masa wannan kuɗi, ta hana amaryar
zuwa wurinsa. Dukkanin tashe-tashen hankulan da suka faru, sun faru ne a
dalilin ƙarin auren da ya yi, wanda kishi ya jagoranci aikata
komai.
4.0
Kammalawa
Bayan tattaro bayanai da aka yi yayin buɗe wannan takarda, waɗanda suka haɗa da ma'anar fim da
samuwarsa, sannan aka yi bayani dangane da kishi da yadda yake auluwa. A cikin
takardar, an bayyana sababin faruwar kishi a tsakanin al'umma, inda aka
karkatar da bayanin kishin dake tsakanin kishiyoyi, wato matan da suke auren
mutum ɗaya. Har wa yau, a
cikin takardar, an ga yadda kishi yake a cikin fina-finan Hausa, ta yadda aka
ciro misalan a cikin fina-finai daban-daban na Hausa wanda yawan su ya kai goma
sha biyu. A ciki an nuna sakamakon dake afkuwa wanda yawancinsa rabuwa ce,
domin a yayin da tashin hankali ya biyo baya, ba lalle a samu bakin zaren da za
a haɗa domin ɗaure wannan matsala
ba. A cikin takardar, an bayyana yadda mata a fina-finan Hausa ke aiwatar da
kishinsu a aikace a yayin da suke kasance matan mutum guda. Hakan sai kishi ya
yi tasirin da zai sanya su illata kishiyar tasu, ko mijin, ko ‘ya’yan kishiya,
ko kuma su illata uwar miji kamar yadda misalai suka gabata a wasu fina-finai.
A mafi yawan waɗannan fina-finai
kuwa, akan ga sakamakon da hakan yake haifarwa wadda ta aikata mugunta, ko dai
ta harkace, ko ta gamu da wata cuta, ko ‘ya’yanta su kasance mutanen banza, ɓarayi, ko kuma ta
rabu da mijinta ta koma rayuwar zawarci cikin ƙasƙanci.
Manazarta
Tuntuɓi masu takarda.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.