Ticker

6/recent/ticker-posts

Ci Gaban Mai Ginar Rijiya: Illolin Dimokuradiyya A Rayuwar Hausawa AYau

Takardar da aka gabatar a taron kara wa juna sani na kasa da kasa na farko a kan nazarin harshen Hausa a k’arni na 21 da Jami’ar Bayero Kano ta shirya a ranar Litinin 10 - Alhamis 13 ga Nuwamba, 2014.

NA

MUSA SHEHU
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu ‘Danfodiyo, Sakkwato
07031319454
msyauri@yahoo.com

1.0  Gabatarwa


          Hausawa na d’aya daga cikin al’ummomin duniya da ke a sahun gaba idan aka yi batun tarbiyya da kyawawan tsarin zamantakewar al’umma. Tsarin zamantakewar Bahaushe ya taimaka wajen samar da kyawawan d’abi’u da al’adu abin alfahari ga mai su. Hausawa sun ci gaba da tafiya bisa wad’annan kyawawan d’abi’u da al’adu wad’anda suka zama musu abin ado a tsakanin mutane.[i] Daga cikin kyawawan d’abi’un Hausawa na zamantakewa akwai gaskiya da rik’on amana, da zumunci, da tarbiyya tagari ga ‘ya’yansu maza da mata, ga ladabi da biyayya, da taimakon juna, da kyautata wa mak’wabci, da makamantansu da dama. Sai dai kuma, dukkan wad’annan kyawawan d’abi’u da halaye na al’ummar Hausawa sun wanzu ne tun kafin tasirin Turawa na samuwar dimokurad’iyya a k’asar Hausa, domin a yau al’amurra sun sassauya, kyawawan d’abi’un da aka sani ga Hausawa sun yi rauni matuk’a. Zama lafiya ya kau, biyayya ga iyaye da magabata ta salwanta, tarbiyya tagari daga iyaye ta sha ruwa, zumunci ya kama gabansa, wai duk da sunan ci gaban dimokurad’iyya, wanda nike ganin cewa, ci gaba ne amma irin na mai ginan rijiya. Kar dai in cika ku da gafara sa ku kasa ganin k’aho. Mak’asudin wannan takarda shi ne, nazarin illolin da dimokurad’iyya ta haifar a rayuwar Hausawa a yau, da dalilan faruwarsu, da kuma hanyoyin magance su ko kuma rage musu k’arfi ta yadda rayuwar Hausawa za ta iya sake ginuwa kamar inda aka fito ko fiya da haka. A sakamakon shigowar dimokurad’iyya a k’asar Hausa a yau, kyakkyawar rayuwar Hausawa ta sukurkuce ta yadda take neman agaji daga mawuyacin halin da ta shiga a yau. Tarbiyyar yara maza da mata ya sukurkuce, sai shaye-shaye da ayyukan ta’addanci ga matasanmu. ‘Yan siyasa sun tsunduma cikin tsafe-tsafe domin samun nasara. Zalunci da rashin gaskiya da amana da adalci ya share fili ya shimfid’a tabarmarsa a rayuwar shugabanninmu, abin dai sai wanda ya ji ko ya gani. Allah Ka yi muna agaji.

2.0  Ma’anar Kalmar Dimokurad’iyya


          Kalmar dimokurad’iyya asali ba kalmar Hausa ba ce, ararriyar kalma ce daga harshen Ingilishi, woto “Democracy”. A ma’ana ta Mac Millan Dictionary, kalmar tana nufin, wani tsari na gwaunati wanda jama’a ke jefa k’uriar za’ben wad’anda za su shugabance su.[ii] A k’amusun Hausa kuwa, dimokurad’iyya na nufin, tafarkin mulkin da mutanen k’asa ke za’bar shugabanninsu ta hanyar jefa k’uri’a.[iii] Dimokurad’iyya tsari ne da ke ba kowa ‘yancin shigowa a dama da shi a fagen neman shugabanci matuk’ar ya samu amincewar al’ummar da yake son shugabanta dangane da kyawawan halaye da d’abi’unsa. Haka ma akwai k’ayyadadden wa’adin da aka shata na tsawon lokacin da mutum zai yi yana gudanar da shugabancin. Saboda haka, idan wannan wa’adi ya cika zai sauka daga wannan matsayi a sake za’ben wani. Sai dai tsarin ya ba mutum damar sake neman shugabancin, ma’ana mutum zai iya sake nema karo na biyu, a wani matsayin ma mutum zai iya nema fiye da haka har sai sa’ad da wani ya fito ya kayar da shi. Saboda haka, irin wannan tsari na shugabanci sabon al’amari ne ga rayuwar Hausawa, domin ba haka lamarin yake a tsarin al’adun rayuwarsu ba. Shugabanci a al’adar Hausawa gadon sa ake yi, ko dai a wajen iyaye ko kuma a wajen kakanni. To sai dai kuma, irin wannan tsari na dimokurad’iyya tsari ne mai alfanu da kuma ba kowa ‘yancinsa ba tare da wata tawaya ba, amma fa idan an yi amfani da shi kamar yadda wad’anda suka shigo da shi suka tsara.

https://www.amsoshi.com/2017/11/06/1355/

3.0  Rayuwar Hausawa Kafin Shigowar Dimokurad’iyya


Kamar yadda aka bayyana a cikin gabatarwa, rayuwar Hausawa kafin shigowar dimokurad’iyya ta kasance gwanin ban sha’awa. Shugabanni sun kasance masu adalci da rik’on amanar talakawansu. Iyaye suna kula da tarbiyyar ‘ya’yansu kamar yadda ya kamata. Talakawa suna biyya ga shugabanni gwargwadon hali. ‘Ya’ya sun kasance masu ladabi da biyayya ga iyaye da ma magabata saboda kyakkywar tarbiyyar da suka tashi da ita. Iyaye sun sa ido ga ilimn ‘ya’yansu, da kuma aza su ga tafarkin yin sana’a. Babu mai zaman kashe wando balle ya sa ido ga abin da ba daidai ba. Zama lafiya ya wanzu a ko’ina, al’amarin dai gwanin ban sha’awa ga mai sauraro da d’an kallo. Bari mu dubi bayanin yadda rayuwar take dalla-dalla domin fed’e biri har wutsiya.

Zaman Lafiya: Masu iya magana na cewa, zama lafiya ya fi zama d’an sarki.`Kafin gur’batar dimokurad’iyya, k’asar Hausa k’asa ce da aka sani da zama lafiya da kwanciyar hankali. Babu tashe-tashen hankula balle a samu salwantar rayuwa da dukiyoyi. Zalunci da babakere ba su sami gindin zama ba balle su baje kolinsu. Shugabanni suna kwatanta adalci, don haka ba su fuskanci tawaye daga talakawansu ba. Saboda yanayin zama lafiya da ke akwai a k’asar Hausa, ya sa al’ummomi daban-daban suke yin tururuwar shigowa k’asar domin a ci gajiyarsa da su. Hakan ya sa duk d’an wata k’abila da ya d’and’ani zama a k’asar Hausa bai iya komawa k’asarsu domin ya ga wurin zama, sai dai ya rik’a zuwa ganin gida daga lokaci zuwa lokaci. Fad’ace-fad’ace da ayyukan ta’addanci sai dai Hausawa su ji labarinsu a wasu k’asashe. Rayuwa a k’asar Hausa in dai babu sa albarka, babu ko Allah wadai.

Ladabi Da Biyayya: Ladabi da biyayya manyan k’usoshi ne a cikin tarbiyyar Hausawa, wato muhimman halaye ne da Bahaushe yake so ya ga ana yi. Girmama na gaba da kyautata wa na baya su ne halayen da ake kira ladabi da biyayya (Alhassan da wasu 1982). A kullum burin iyaye ba ya wuce ganin ‘ya’yansu sun girma cikin halaye kyawawa masu nagarta, don haka suke koya musu yin ladabi da biyayya ga iyaye da ma na gaba gare su. Sukan koya musu ladabin magana wanda ya shafi koya musu tausasa murya lokacin magana da babba, kuma kar a tsura masa ido da kallo kamar yadda tumaki suke yi. Haka ma ba a gai da iyaye ko magabata a tsaye sai an duk’a musamman idan suna zaune. Ba a k’etare umarnin iyaye ko ba dad’i, sai dai a daure a aikata yadda suke buk’ata.

Kare ‘Diyauci: Bahaushe bai san karuwanci ba balle masu yin sa.’Ya’yan Hausawa mata tun suna k’anana akan yi k’ok’arin cusa musu al’adar nisantar maza da kuma illar da ke tattare da kusantar su. Don haka ne ko a wasannin dandali k’ungiyar mata daban na maza ma daban. Wannan tarbiyyar ba ta tsaya a nan kawai ba, hatta idan aka yi wa mace aure akan kai ta da wani farin k’yalle da ake kira bante wanda za ta fara kwanciya da shi. Ta wannan k’yalle ne za a gane ta kare d’iyaucinta ko akasin haka. Idan aka yi nasara ta kai bante wato ba ta ta’ba sanin d’a namiji ba sai ga mijinta na aure, iyayenta kan yi murna da kasancewa masu alfahari da ita. Idan kuwa aka sami akasin haka, to yarinyar ta bar abin fad’e da zubar da mutuncin iyayenta. Wannan al’ada ya yi tasiri ainun ga ‘yan mata wajen ganin ba su zubar da mutuncin gidansu ba, da kuma barin abin fad’e a baya.

Gaskiya Da Rik’on Amana: Hausawa mutane ne da suke da kyakkyawar tarbiyya da himmatuwa zuwa ga d’aukar halaye nagari irin su gaskiya da rik’on amana. Babu yaudara ko cin amana a rayuwar Hausawa. Wato mutane ne masu karimci da shimfid’ar fuska wadda aka ce ta fi shimfid’ar tabarma. Duk wanda ya had’a huld’a ta kasuwanci ko na zamantakewa da Hausawa zai tabbatar da cewa Hausawa mutane ne masu gaskiya. Wannan ne ya samar wa Hausawa kyakkyawar dangantaka ta kasuwanci tsakaninsu da al’ummomi daban-daban na cikin gida da ma sauran k’asashen duniya.

Zumunta: K’ok’arin kusantar ‘yan’uwa da abokan arziki da ziyartar su a kai-a-kai, ita ce zumunta (Alhassan da wasu 1982). Tarbiyyar Hausawa tana jaddada ziyarce-ziyarce tsakanin ‘yan’uwa da abokan arziki. A tsarin rayuwar Bahaushe, mak’wabci tamkar d’an’uwa ne, domin idan aka wayi gari sai an gaisa kafin kowa ya fita tasa harka. Don haka, idan wani abin farin ciki ko akasinsa ya samu mak’wabcin mutum, za a zauna a taya juna murna ko juyayi idan mara kyau ne. Haka ma duk wani abu da ya samu ‘yan’uwa na murna kamar haihuwa ko aure akan taru domin a sada zumunci kuma a k’arfafa shi. Har ta kai ga Bahaushe kan d’auki d’ansa ya ba d’an’uwansa rik’o domin k’arfafa zumuntar da ke tsakaninsu.

Mallakar Sana’a: Al’ummar Hausawa tun asali al’umma ce wadda ta dogara da kanta wajen samar da hanyoyin tattalin arzikinta. Ta haka ne ya zama a kowane gidan Bahaushe za ka tarar yana da sana’o’in da yake aiwatarwa. Don haka, yakan yi k’ok’arin gina yaransa bisa wannan sana’a domin su girma da ita, su kuma kauce wa zaman kashe wando da sa ido da yawon gararanba a cikin unguwa.

4.0  Illolin Dimokurad’iyya a Rayuwar Hausawa a Yau


          Da ma ana cewa, duk wani abu mai amfani ba za a rasa illa a cikin sa ba. Dimokurad’iyya wani tsari ne na tafiyar da rayuwar al’umma mai alfanu matuk’ar dai an yi amfani da shi kamar yadda aka tsara shi. To sai dai kuma, lamarin Dimokurad’iyyar a Arewacin Nijeriya a yau ya d’auki sabon salo wanda ya sha bamban da na wad’anda suka kawo shi, wato Turawa. A dimokurad’iyyar da ake gudanarwa k’asar Hausa a yau, an cakud’a gaskiya da k’arya, an mayar da gaba baya, ta yadda al’amurra suka kasa zuwa gaba sai dai baya. Wannan matsalar ta yi tasiri ainun a rayuwar Hausawa a yau, inda ‘yan siyasar k’asar Hausa suka mayar da dimokurad’iyya in ba ka yi ba ni wuri. Sukan bi duk wata hanya mai kyau ko akasinsa, galibi hanyoyi marasa kyau domin cimma burinsu na wani matsayi da suke nema. Hakan ya sa tsafe-tsafe ya samu gindin zama. Safarar miyagun k’wayoyi domin bai wa matasa ‘yan bangar siyasa ya baje hajarsa. K’ungiyoyin ‘yan daba suka mamaye unguwanni. Fitintinu da tashe-tashen hankula da salwantar rayukar al’umma da dukiyoyinsu ya zama ruwan dare game k’asar Hausa. Ga dai bayanin irin illolin kamar haka:

4.1  Rashin Zama Lafiya

Zama lafiya da aka sani a k’asar Hausa inda har wasu al’ummu kan shigo domin cin gajiyarsa, a yau ya yi ‘batan dabo. Tashe-tashen hankula ya wanzu a kusan kowane ‘bangare na k’asar Hausa. Allah kad’ai ya san adadin rayukan Hausawa da dukiyoyinsu da suka salwanta tun bayan gur’bacewar dimokurad’iyya. A yau za ka ji an kai hari a wannan sashe an kashe mutane masu tarin yawa da hasarar dukiyoyi, gobe ka ji an kai a wancan ‘bangare, haka dai lamarin ke ci gaba da aukuwa fiye da shekaru hud’u da suka gabata duk da sunan ci gaban dimokurad’iyya. To sai dai kuma, duk da irin wad’annan matsaloli da Hausawa ke huskanta a k’asashensu, sai ka iske ‘yan siyasa sun mik’e suna bayyana irin ci gaban da aka samu na tafarkin dimokurad’iyya, Allah dai ka yi muna magani.

4.2  Ta’bar’barewar Tarbiyya

          Kyakkyawar tarbiyyar da aka san matasan Hausawa da shi a da, a yau lamarin sai dai a shafa fatiha a watse. ‘Yan siyasa sun yi ruwa da tsaki wajen tabbatar da gur’bacewar tarbiyyar matasa a yau. Sukan sawo miyagun k’wayoyi da miyagun makamai da d’an kud’in da bai taka kara ya karya ba su raba wa matasa don su yi musu bangar siyasa. Saboda haka, a duk lokacin da wad’annan matasa suka sha wad’annan k’wayoyi sukan fita hayyacinsu, daga nan sai ayyukan ta’addanci su wanzu na kai wa abokan hamayyar ubangidansu da ma junansu hare-hare da lalata dukiyoyi, da yi wa mata fyad’e da makamantansu.  A wani lokaci ma har hayan matasa ake d’auka domin su hallaka wani abokin hamayya. Don haka, maganar mallakar sana’a ya sha ruwa, sai dai tunanin had’a k’ungiyoyin daba iri daban-daban. Haka ma lamarin karatun zamani (boko) da na addini (Musulunci) ga matasa ya yi rauni, domin ‘yan siyasa sun yi awon gaba da kyakkyawar tunanin matasan suka bar musu gur’batacce, don haka maganar neman ilimi ko sana’ar dogaro da kai bai taso ba. A sakamakon haka, matasa da yawa sun sami ta’buwar hankali, wasu sun zama musakai, wasu ma sun rasa rayuwa baki d’aya. Duk wad’annan matsaloli ne da ke faruwa da sunan ci gaban dimokurad’iyya, Allah ya kiyashe mu da irin wannan ci gaba na mai ginan rijiya.

4.3  Ta’bar’barewar Zumunci

           Mulkin Dimokurad’iyya ya zama ummul-haba’isin ta’bar’barewar zumunci a yau. Siyasa ta shiga tsakanin ‘yan’uwa ta d’aid’aita su. Ta shiga tsakanin abokai ta yanke musu k’auna. Ta raba soyayyar da ke tsakanin ma’aurata. Ta shiga tsakanin mak’wabta ta haddasa gaba a tsakaninsu, ta bi komai ta hargitsa. Sau da yawa za ka taras ana uwaka-ubaka tsakanin ‘yan’uwa, ko wa da k’ani, ko mata da miji, ko aboki da abokinsa, ko ma ka iske an yi hannun riga tsakanin d’a da mahaifi kowa ya kama gabansa. Haka ma sai ka iske ba a ga-maciji tsakanin mak’wabta, sai mak’wabci ya yo hayar ‘yan daba a kawo wa mak’wabcinsa hari a lalata dukiyoyinsa, duk kawai saboda bambancin jam’iyyar siyasa. Saboda haka, tilas zumunci ya ta’bar’bare, taimakon juna da ziyara da jink’ai suka nufi inda dare ya yi musu tun lokaci bai k’ure ba. A yau kowa kansa kawai ya sani, ya nufi inda zai sami arziki a k’ark’ashin wata jam’iyya, duk mai mutuwa ya rage nasa.

4.4  Wanzuwar K’ungiyoyin Daba na Matasa (Area Boys)

          Saboda irin ta’bar’barewar da Dimokorad’iyya ta yi a k’asar Hausa a yau, har ta kai ga wanzuwar k’ungiyoyin ta’addanci na matasa wad’anda ake kira “Area Boys” daban-daban biranen k’asar Hausa da ma k’auyukansu wad’anda ke k’ark’ashin kulawar wasu ‘yan siyasa. Wasu k’ungiyoyin ma har albashi ake yi musu a k’arshen kowane wata kamar sauran ma’aikatar gwaunati. Saboda haka, a duk lokacin da za a tafi yawon kamfe, za a kwashi wad’annan matasa (‘yan daba) cikin motoci a ba su miyagun makamai don ko ta kwana. Haka ma idan ana buk’atar cin zarafin wani abokin hamayya ko ma a kawar da shi a doron k’asa, irin wad’annan matasa ‘yan siyasa kan samu su biya musu buk’ata. Don haka, duk irin ta’adin da suka aikata komai ba a yi musu, saboda ko hukuma ta kama su sai iyayen gidansu su shiga su fita sai sun ga an sake su. Alal misali, a kwanakin baya ‘yan daba suka rik’a tsayawa a tsakiyar randabawul  a cikin garin Sakkwato suna tare motocin mutane wai sai an ba su rabonsu ko mutum ya huskanci walak’anci.

4.5  Yawaitar Tsafe-Tsafe                                                                                                                 A riwayar Bunza (2006) ya bayyana tsafi da bin wasu hanyoyi na gargajiya musamman yi wa iskoki hidima, da yanka, da bauta, domin biyan wata buk’ata, ko ko wani amfani, ko tunkud’e wata cuta.[iv] Ya ci gaba da cewa, Tsafi ya yi rawar gani wajen tabbatar da Bamagujiyar rayuwa ta Hausawan jiya. Da shi ake tink’aho don tsare kai da kaya. Da shi ake kuri wajen kariyar martabatar abin da aka gada kaka da kakanni. Da shi ake yin fice wajen wasanni da bukukuwan gargajiya da ake aiwatarwa a ko’ina a k’asar Hausa. Sai dai zuwan Musulunci ya taka masa birki ta yadda ya kasa motsi balle ya wataya. To sai dai kuma, a wannan zamani da ake ciki na tsarin dimokurad’iyya yana neman ya mayar da hannun agogo baya, domin a yau ‘yan siyasa sun tsunduma dumu-dumu cikin harkar tsafe-tsafe domin neman matsayi na siyasa. Sun ba Allah baya, sun fuskanci malaman tsibbu da miyagun bokaye domin biyan buk’ata. Saboda haka ake tura su zuwa ga sace-sacen yara ana cire wasu sassa na jikinsu, ko a tafi mak’abarta a tone k’abari a d’ibi wani sashe daga jikin mamaci, domin had’a miyagun asirrai wai a samu nasara.

 

4.6   Handama da Babakere

A ma’ana ta gaskiya, ba komai ne Dimokurad’iyya a Nijeriya ba face zalunci da rashin gaskiya da handamar dukiyar talakawa. A yau ‘yan siyasa suna neman matsayi ne ba don kare hak’k’in wad’anda suke wakilta ba, a’a, sai don kawai handamar dukiyoyinsu da kuma barazana ga rayukansu idan suka nemi su yi tawaye. Hakan ya sa suke bin duk wata hanya na ganin sun kai ga baitil-malinsu. Talakawan jiha ba su amfana da arzikinsu na ak’alla kashi talatin cikin d’ari da ake ware musu, an yi ruf-da-ciki da saura. Lamarin k’ananan hukumomi kuwa sai wanda ya ji ko ya gani, domin da zarar an yi albashi da abin da bai wuce kashi talatin cikin d’ari ba, sauran sai dai kawai ‘yan siyasa su yi tonton kowa ya kwashi rabonsa a hari wani wata mai zuwa. Talakawa sun shiga halin k’ak’a-nika-yi, abin da za su ci ma ya zama lalura balle a kula da lafiyarsu da sauran buk’atun rayuwarsu. Allah ya kiyashe mu da irin wannan ci gaba na dimokurad’iyya.

4.7  Cud’ed’eniyar Maza da Mata

Cud’ed’eniyar maza da mata wuri d’aya abu ne da al’adar Hausawa da ma addininsu (Musulunci) ba su aminta da ita ba, sai dai idan lalurar hakan ta kama. Amma a yau tsarin mulkin Dimokurad’iyya ya nuna cewa, mace za ta iya fitowa neman wani matsayi na shugabanci a fafata da ita kamar yadda namiji zai iya fitowa. Sau da yawa za ka iske an kwashi ‘yan mata da zawarawa har ma da matan aure cikin mota ana yawon kamfe da su kamar yadda takwarorinsu maza suke yi. A yanzu ma har an fara samun matan Hausawa suna fitowa takara suna tsayawa gaban dubban maza suna kamfe wai a za’be su a matsayin wakilan maza. A fad’ar wasu, wai duk abin da namiji zai iya yi, mace ma za ta iya yin fiye da haka. Wannan mummunan tsari da tunani a yau ya ratsa k’wak’walwar matan Hausawa na ganin  cewa za su iya gwagwarmaya da maza ta kowace fuska, don haka lamarin sai dai kawai addu’a Allah shi yi muna magani, ya kuma sa mu gane tafarki managarci.

5.0  Musabbabin Matsalar


          A duk lokacin da al’amurra suka sukurkuce suka sauya kamanni ba kamar yadda aka saba da su ba, tilas akwai dalilan da suka jawo haka. Don haka, akwai abubuwa da dama da suka zama ummul-haba’isin wad’annan matsaloli da suke ci wa rayuwar Hausawa tuwo a k’warya a yau. Ga wasu daga cikinsu:

Rashin Amfani da Doka da Oda: Ba shakka, rashin amfani da doka da oda na daga cikin abubuwan da suka haddasa wasu daga cikin illolin da aka bayyana a sama. A yau kowa na cin karensa ne babu babbaka musamman ‘yan siyasa ko masu wani muk’ami ko masu hannu da shuni. A yau idan kana tare da manya, duk laifin da ka yi hukunci ba ya hawa kanka. Don haka, duk dukiyar da ka sata na al’umma ko wani ha’inci ko kisan kai ko wani ta’addanci, ko an gane ba a yi ma komai, ka ci bilis. Haka ma, idan ‘yan ta’adda suka aikata wani ta’addanci aka kama su, sai ka iske wasu ‘bara-gurbin mutane sun yi ruwa sun yi tsaki sun hana hukuma aikinta. Idan ka ga doka ta yi aiki a yau, to ga talakawa ne wad’anda ba su da kowa sai Allah.

Sakacin Iyaye: Hak’ik’a akwai sakacin iyaye wajen lalacewar tarbiyyar matasa a yau. Sai ka iske iyaye sun haifi ‘ya’ya sun sake su kamar tumaki ba su tsare hakkin da Allah ya d’ora musu na tarbiyyansu da ta danganci addini da al’ada. Sau da yawa za ka iske iyaye ba su damu da sa ‘ya’yansu makarantar addini ba balle na zamani. Saboda haka, duk yaron da ya tsinci kansa cikin irin wannan yanayi rayuwarsa na cikin had’ari. Daga nan ne sai ka iske yaro ya had’u da miyagun abokai, sai shaye-shaye da had’a k’ungiyoyin daba, shi ke nan rayuwa ta lalace.

6.0  To Ina Mafita?


          Masu iya magana na cewa, ruwa na k’asa sai ga wanda bai tona ba. Ba shakka, duk yadda al’amurra suka ta’bar’bare ba za a yanke k’auna ga samun mafita ba. A kan haka nike ganin akwai hanyoyi da yawa wad’anda idan aka jaraba amfani da su watak’ila a sami maslaha a ceto rayuwar Hausawa daga bala’o’in da ke k’ok’arin ganin baya gare ta. Daga cikin wad’annan hanyoyi akwai sa hannun gwaunati, da iyayen yara, da kuma malaman addini.

6.1  Gwamnati


          Hak’ik’a gwaunati ce a sahun farko na wad’anda za su iya ba da tasu gudummuwa wajen samar da mafita dangane da wad’annan matsaloli na dimokurad’iyya da suke ci gaba da addabar rayuwar Hausawa a yau. Gwunati za ta iya daidaita al’amurra su dawo cikin hayyacinsu ta hanyar fito da wasu hanyoyi na dak’ushe bangar siyasa da amfani da matasa wajen ayyukan ta’addanci. Dole ne a yi amfani da doka da oda wajen hukunta duk wani d’an siyasa ko d’an bangarta da aka samu da hannu wajen aikata abubuwan da suka sa’ba wa doka. Dole ne gwaunati ta samar da wasu shirye-shirye na fad’akar da matasa illolin da ke tattare da bin ‘bara-gurbin ‘yan siyasa, da kuma irin had’urran da ke tattare da shaye-shayen miyagun k’wayoyin da suke yi wanda ke iya kai su ga halaka.

6.2  Iyaye

          Iyaye su suka fi cancanta da kula da halin da yaransu ke ciki, domin su ne Allah ya damk’a wa ragamar tarbiyyar rayuwarsu tun suna k’anana har zuwa girmansu. Tilas su tsaye tsayin daka wajen ba su ilimin addinii da na zamani domin su ci moraiyar rayuwarsu ta duniya da ma ta gobe k’iyama. Dole ne iyaye su d’ora ‘ya’yansu bisa turba ta sana’a domin kauce wa zaman banza wanda shi ke kai su ga fad’awa cikin miyagun hanyoyi. Dole su sa ido ga ire-iren abokan da ‘ya’yansu suke huld’a da su don kauce wa fad’awa hannun ‘bata-gari.

6.3  Malaman Addini

          Duk da cewa, malaman addinin Musulunci suna iya k’ok’arinsu wajen wa’azantar da al’umma a kusan kowane lokaci, kuma ana yayata fad’akarwar tasu a kusan dukkan kafafen yad’a labarai kama daga rediyo da talabijin da jaridu da mujallu da tauraron d’an Adam da intanet da makamantansu, zai kyautu su k’ara ba da k’arfi a kan wannan matsala da mulkin Dimokorad’iyya ya haifar a rayuwar Hausawa a yau. Su rik’a bayyana wa jama’a musamman masu ruwa da tsaki a kan lamarin siyasa irin mummunar sakamakon da ke jiran duk wani mai k’ok’arin cutar da al’umma, yake barazana ga rayuwarsu, ko yake lalata tarbiyyarsu, ya haddasa musu bala’i, ya hana su zama lafiya balle su bauta wa mahaliccinsu kamar yadda ya kamata.

Jawabin Kammalawa


          Tsarin dimokurad’iyya a k’asar Hausa a yau ya zama tamkar wani mulki na kama-karya da danniya da babakere da rashin tausayin na k’asa wanda ya gudana a zamanin jahiliyya, inda sai yadda shugabanni suka ga daman yi da talakawa. An gur’bata tunanin matasa ta yadda ba su iya fitar da suhe wuta. An talautar da jama’a domin a juya akalar rayuwarsu yadda aka ga dama. Aka kuma haddasa fargaba da rashin zama lafiya a rayuwarsu. Kowa son yake yi ya shiga harkar siyasa domin a ci karen da babu babbaka tare da shi. Al’amurra a rayuwar Hausawa a yau musamman talakawa ya zama abin tausayi ga duk wani mai imani na gaskiya. Tilas mu tashi tsaye mu had’a k’arfi da k’arfe domin ganin bayan wannan bala’i da ya kewaye kusurwoyin rayuwar Hausawa domin sake dawowa da kyakkyawar rayuwar da muka gada daga kaka da kakanni.

 

 

https://www.amsoshi.com/2017/11/08/makamin-dimokradiyya-a-falsafar-alada/

 

 

MANAZARTA


Alkali, B. 1968. “Hausa Community in Crisis: Kebbi in the 19th Century”, MA Thesis, Ahmadu Bello University, Zaria.

Birniwa, H. A. 1987. “Conservatism and Dissent: A Comparative Study of NPC/NPN and NEPU/PRP Hausa Polical Verse from Ca 1949 – 1983, PhD Thesis, Usmanu ‘Danfodiyo University Sokoto.

Birniwa, H. A. 1987. “Ra’ayin Rik’au da na Kawo Sauyi Cikin Wak’ok’in Siyasa”, Mak’alar da aka gabatar a taron k’asa da k’asa na Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,  Jami’ar Bayero Kano.

Bunza, A. M. 1996. “Gaskiya Ina Laifinki? Tsokacin Diddigin Musabbabin Karyewar Arzikin Nijeriya Cikin Wak’ar Gaskiya Mugunyar Magana, Ta Alhaji Muhammadu Sambo Wali Basakkwace,” Jami’ar Usmanu ‘Danfodiyo Sakkwato.

Bunza, A. M. 2000. “A Dad’e Ana Yi Sai Gaskiya: Laluben Gurbin Gaskiya Cikin Adabin Hausa”, Mak’alar da aka gabatar a taron k’ara wa juna sani, Jami’ar Usmanu ‘Danfodiyo Sakkwato  .

Bunza, A.M. 2006 Gadon Fed’e Al’ada. Tiwal Nigeria Limited, Surulere, Lagos.

Bunza, A.M. 2013. “Makamin Dimokurad’iyya a Falsafar Al’ada” Takardar da aka gabatar a

taron  k’ara wa juna sani na k’asa na farko a kan  Harshe da Adabi  da  Al’adun

Hausawa na Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano.

Burji, B. S. 1997. Gaskiya Nagartar Namiji. Baraka Press Limited, Kaduna.

Msutapha, S. 2003 “Gurbin Gaskiya Cikin Adabin Hausa”, kundin digirin MA, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Nasidi, Y. & Igoil, I. (ed)1997Culture and Democracy. Zaria: Ahmadu Bello University Press

Sarkin Gulbi, A. 2013 “Tsafe-tsafen Dimokrad’iyya” Takardar da aka gabatar a taron k’asa na

farko kan Harshe da Adabi da Al’ada, wanda Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya

Jami’ar Bayero Kano ta shirya.

[i]  Dubi Bugaje 2013, “Tarbiyya da Zamantakewar Hausawa Jiya da Yau”. Mak’alar da aka gabatar a taron k’ara wa juna sani na k’asa da k’asa kan Ta’bar’barewar Al’adun Hausawa a Yau, Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua, Katsina.

[ii]  Dubi Mac Millan English Dictionary for Advanced Leaners, International Edition, shafi na 369.

[iii]  Dubi k’amusun Hausa, 2006,  wallafar Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano shafi na 104

[iv]   Domin k’arin bayani game da lamarin tsafi, sai a dubi Bunza 2006, Gadon Fed’e Al’ada, shafi na 35-57.
www.amsoshi.com

Post a Comment

1 Comments

ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.