𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
Alaikum, malam dan Allah ina so a ban maganin mallaka amma a cikin ayoyin
Kur'ani dan na ji an ce akwai, saboda ina son saurayina ga shi za a yi maganar
kawo kuɗi, kuma
malam wallahi ban da niyyar cutar da shi saboda Allah. Sannan ina so a ba wa
kanwata maganin farin jini a temaka.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
Salam, ƴar
uwa a magana ta gaskiya, wacce take duk wani malami na Allah da Annabi, in dai
ba kuɗaɗenku yake son ya karɓe ba, to zai faɗa maku cewa ba wasu ayoyi
da Allah ya saukar da sunan ayoyin mallake miji ko saurayi ko na farin jini ga
mace, Allah S. W. T. Bai saukar da Alqur'ani da manufar haka ba, sai dai kawai
ayoyin Alqur'ani da hadisan Manzon Allah ﷺ
sun bayyana duk hanyoyin da mutum zai bi don ya sami karɓuwa a wurin Allah da wurin bayin Allah.
Kyawawan ɗabi'u da kyautata
mu'amala su ne tushe na gaskiya da mutum zai mallake zuciyar abokin rayuwarsa,
matuqar babu kyakkyawar mu'amala a tsakanin mata da miji, ko saurayi da
budurwa, to tabbas komin siddabarun da boka zai ba mutum ba zai taɓa samun nasarar mallake
abokin rayuwarsa ba, in ma ya samu to na ɗan
lokaci ne aka yi masa talala kafin Allah ya kama shi, sannan kuma ga fuskantar
mummunar makoma a wurin Allah ga wanda yake harka da bokaye da ƴan
tsibbu, ko da mai harka da bokaye ko ƴan tsibbu ya ga kamar ya ci nasara, to ya
sani ba nasara ya samu ba, talala Allah yake masa domin ya turmutsa shi a
Jahannama, saboda duk wanda ya mutu yana mu'amala da waɗannan miyagu to lallai zai haɗu da fushin Allah.
Bisa shawara
ga wadda take son mallake mijinta, ko take son ta yi farin jini, to ta dage da
yin addu'a ba dare ba rana, kuma ta dage da kyautata mu'amala a tsakaninta da
mijinta idan matar aure ce, idan kuma budurwa ce sai ta riqi kyawawan ɗabi'u da addu'a, da jin
tsoron Allah a cikin al'amuranta, ta dalilin haka sai Allah ya ba ki nasara a
rayuwarki, amma duk wata hanya akasin wannan za ta iya kai mutum ga rasa
imaninsa, saboda idan wannan buqata taki aka yi rashin sa'a kika faɗa hannun maras tsoron
Allah, to zai ce maki ne akwai maganin farin jini ɗin da na mallaka kuma ta amfani da ayoyin
Alqur'ani, wadda kuma qarya ce tsantsa ya faɗa
maki.
Saboda wasu ƴan
tsibbun suna yin amfani da Alqur'anin ne wajen yaudarar kwastamominsu, shi
wanda bai sani ba da zarar ya ga an ɗauko
Alqur'ani, ko an karanto wata ayar Alqur'ani, sai ya za ta maganin Allah da
Annabi za a ba shi, nan kuwa bai san yaudararsa za a yi ta hanyar amfani da
Alqur'anin ba, don haka a yi taka tsan-tsan a koma ga Allah kurum!
Allah ne mafi
sani.
Jamilu Ibrahim
Sarki, Zaria.
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.