𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, Malam dan Allah a ba ni mafita akan wannan matsalan da ke damu na, ni ne soyayya ta shiga tsakanina da wata yar' gurin kanin babana wanda suke uwa ɗaya uba ɗaya ma'ana kanwata kenan, Amma suna zargina akan aikin banza duk da hakan yakare a tunani ne kawai kuma har shi kanin baban nawa ya yi min maganar hakan, amma uwar yarinyar ba ta yimin maganar ba, amma alamunta ya nuna hakan. Sai dai babu Yanda za su yi ne kada a ce ba sa so, itama yarinyar da farko tafara bin irin ra'ayin iyayen amma ba ta fito fili ta bayyana min abin da take nufi ba sai dai tana yawan tambayoyina, kuma har wasu daga cikin kannenta sukan min wasu kallon da ke nuni da akwai magana, kuma mahaifiyata da babana suna son auren amma basu san can ana yimin irin wannan kallon zargin ba (zina) sai dai babu wata hujja da za su kawo (solid evidence) wanda zai tabbatar da hakan. Amma a yanzun yarinyar tana nuna tana so na sosai kuma babu matsala duk da hakan ina tsoron abin da zai iya biyo baya idan an yi auren ni kuma ba na son abin da zai ba ta mana zumunci, tabbas ni dai da za a fasa wannan auren danaji daɗi sai dai ban san yanda zan ɓullo ma wannan abun ba. Dan Allah a taimake ni da addu'a Istikhara na nemi zabin Allah domin koda kuwa ni ne za a ce mai laifi na yarda ni dai bana son auren da zai haddasa gaba a tsakkanin iyayenmu Na gode. Allah ya kara basira.
ADDU'AR NEMAN ZAƁIN ALLAH (ISTIKHARA)
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Godiya ta tabbata ga Allah,
salati da aminci su tabbata bisa Shugaban halittar Allah, da iyalan gidansa da
dukkan Salihan bayin Allah.
Na karanta dukkan bayaninka
tun daga farko har Ƙarshe.
Amma sai dai na lura kamar ka gina mafi yawan batutuwanka ne bisa zato. Misali:
Kana zaton kamar iyayen yarinyar da Ƙannenta
duk suna yi maka kallon mazinaci. Sannan yanzu kuma bayan ka riga ka samu
soyayyarka ta zauna azuciyar yarinyar, sai kake zaton kamar wai za a samu
matsala atsakanin Mahaifinka da ɗan'uwansa.
Gashi kuwa Allah (Maɗaukakin Sarki) ya hana
bayinsa muminai su rika gina al'amura akan zato. Allah ya ce:
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اجْتَنِبُوا كَثِيرًا مِّنَ الظَّنِّ إِنَّ بَعْضَ الظَّنِّ إِثْمٌ ۖ وَلَا تَجَسَّسُوا وَلَا يَغْتَب بَّعْضُكُم بَعْضًا ۚ أَيُحِبُّ أَحَدُكُمْ أَن يَأْكُلَ لَحْمَ أَخِيهِ مَيْتًا فَكَرِهْتُمُوهُ ۚ وَاتَّقُوا اللَّهَ ۚ إِنَّ اللَّهَ تَوَّابٌ رَّحِيمٌ
Ya kũ waɗanda
suka yi ĩmani! Ku nĩsanci abu mai yawa na zato. Lalle sashen zato laifi ne.
Kuma kada ku yi rahoto, kuma kada sashenku ya yi gulmar sashe. Shin, ɗayanku
na son ya ci naman ɗan'uwansa yana matacce? To,
kun ƙĩ shi
(cin naman). Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Mai karɓar
tũba ne, Mai jin ƙai (suratul
Hujurat Aya ta 12)
Kuma Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam Ya ce "KU RIKA YIWA MUMINAI ZATON ALKHAIRI".
Shawarar farko da zan baka
ita ce: Ka karkade duk wani mummunan zato daga zuciyarka, ka dogara da Allah a
cikin dukkan lamuranka. Ka sani cewa duk lokacin da Mutum zai Ƙulla wani muhimmin al'amari sai Shaiɗan
ya zo gareshi ya sanya masa waswasi da mummunan tunani domin ganin ya lalata
masa al'amarinsa.
Bayyanar da Ƙiyayya ga auren nan daga gareka zai iya
janyo maka matsaloli sosai. Musamman ma fushin mahaifanka, da zubewar
mutuncinka a cikin danginku, sannan koda nan gaba idan ka tashi yin aure, za su
iya bayyanar da Ƙiyayyarsu
ko suce babu ruwansu a cikin sha'aninka.
Ka mika wa Allah dukkan
al'amarinka, ka dogara gareshi. Ka roki Allah ya zaɓa
maka abin da zaifi zama alkhairi gareka arayuwar duniya da lahira. In sha
Allahu za ka samu nutsuwar jiki da ta ruhi. Sannan ka samu lokaci mai
muhimmanci kamar sulusin dare na ƙarshe
(kamar daga karfe uku na dare har zuwa alfijir) ka yi sallah raka'a biyu, ka
zauna ka yi wa Annabi salati sannan ka karanta addu'ar nan ta istikhara wacce
take cikin Sahihu Muslim, akwaita ma a cikin Hisnul Muslim.
Jabir ɗan
Abdullah ya ruwaito cewa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya kasance
yana koyar da mu istihara akan dukkan al'amura kamar yadda yake koya mamu Surah
a Alƙur'ani, kamar yadda Imamul Bukhariy ya
ruwaito a hadisi mai lamba ta 6382.
Sallar istikhara sallah ce
da ake yin raka'o'i guda biyu kamar yadda ake yin sauran sallolin nafila, abin
da ke bambanta su shi ne niyya. Ana yin sallar istihara ce don barin ma Allah
zaɓi a
kan wata buƙata da mutum ke da
ita. Sannan kuma Sallar istikhara sunnah ce ba farilla ba. Bayan mutum ya
kammala sallar, sai ya karanta wannan addu'ar:
اللّٰهُمَّ إِنِّيْ أَسْتَخِيْرُكَ بِعِلْمِكَ، وَأَسْتَقْدِرُكَ بِقُدْرَتِكَ، وَأَسْأَلُكَ مِنْ فَضْلِكَ العَظِيْمِ فَإِنَّكَ تَقْدِرُ وَلاَ أَقْدِرُ، وَتَعْلَمُ وَلاَ أَعْلَمُ، وَأَنْتَ عَلاَّمُ الغُيُوْبِ اللّٰهُمَّ إِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا الأمْرَ (وَيُسَمِّيْ حَاجَتَهُ) خَيْرٌ لِيْ فِيْ دِيْنِيْ وَمَعَاشِيْ وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، فَاقْدُرْهُ لِيْ وَيَسِّرْهُ لِيْ ثُمَّ بَارِكْ لِيْ فِيْهِ وَإِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا الْأَمْرَ شَرٌّ لِيْ فِيْ دِيْنِيْ وَمَعَاشِيْ وَعَاقِبَةِ أَمْرِيْ فَاصْرِفْهُ عَنِّيْ وَاصْرِفْنِيْ عَنْهُ وَاقْدُرْ لِيَ الْخَيْرَ حَيْثُ كَانَ، ثُمَّ أَرْضِنِيْ بِهِ
Ya Allah ina neman zaɓinka
domin ilminka, kuma ina neman ka ba ni iko domin ikon ka, kuma ina rokonka daga
falalarka mai girma, domin kai ne mai iko, ni kuwa ba ni da iko, kuma Kaine
masani, ni kuwa ban Sani ba, kuma Kaine masanin abubuwan fake, Ya Allah! Idan
kasan cewa wannan al'amari (sai ya ambaci buƙatar
tasa) alheri ne gareni a cikin addinina, da rayuwa ta, da kuma ƙarshen al'amarina, - a wata ruwayar da
magaggaucin al'amarina da majinkircinsa - ka ƙaddara
mini shi, kuma ka saukake mini shi, sannan ka albarkaceni a cikin sa, kuma idan
kasan wannan al'amari sharrine a gare ni a cikin addinina, da rayuwata da ƙarshen al'amarina - a wata ruwaya; da
magaugaucin al'amarina da majinkircinsa - Ka kawar da shi daga gare ni, kuma ka
kawar DA NI daga gare shi, kuma ka kaddara mini alherin a duk inda yake, kuma
ka sanya ni in yar da shi.
Ana karanta addu'ar ce bayan
an idar da sallar an yi sallama, sai mutum ya ɗaga
hannuwansa sama, ya yi yabo da jinjina ga Ubangiji, sannan ya yi salati ga
Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam. Daga nan kuma sai ya yi ita waccan
addu'ar ta istikhara.
Kuma ya halasta ga wanda ba
ya iya yin ta da Larabci ya furta ma'anoninta da Hausa, ko kuma da duk harshen
da yake iyawa, amma a yi addu'a da Larabci shi ne ya fi kamar yadda malaman Fiƙhu suka bayyanar.
Duk lokacin da kaji wani
mummunan tunani ya zo maka game da lamarin nan, yi sauri ka yi addu'a ka nemi
tsarin Allah daga sharrin shaiɗan.
Duk wanda ya nemi zaɓin
Mahalicci, kuma ya yi shawara da talikai muminai, kuma ya yi azama a cikin
lamarinsa, to bazai yi nadama ba. In sha Allah. Domin Allah Maɗaukakin
Sarki ya ce: "Kuma ka shawarce su cikin lamarinka, idan kuma ka ƙuduri aniya, to ka dogara ga Allah.
Daga ƙarshe ina yi maka fatan dukkan alkhairi,
da fatan Allah ya sanya maka alkhairi a cikin aurenka da dukkan lamuranka.
Ameen.
WALLAHU A'ALAM.
Ku kasance damu cikin wannan
group domin ilimintarwa, Fadakarwa da Tunatarwa.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.