Kundin Binciken Neman Digiri Na Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, Satumba, 2016
NA
ASHIRU USMAN GABASAWA
BABI NA BIYAR
KAMMALAWA
5.0 Shimfiɗa
Domin kammala wannan nazari, za a waiwaiyi abubuwan da suka
gabata a cikin kowane babi a taƙaice. Sannan akwai
sakamakon wannan nazari da aka gudanar domin jaddada mahimmancinsu cikin
nazarin harshe. Za a kuma bayar da shawarwari duk a cikin wannan babi na biyar,
wanda shi ne babi na ƙarshe.
5.1 Taƙaitawa
Babi na ɗaya ya yi tsokaci ne kan
gabatarwa. A babin an bayyana manufar wannan da farfajiyarsa da kuma
mahimmancinsa, musamman ga masu nazari da kuma masana da ma mahimmancinsa ga
al’ummar Hausawa. Haka kuma mun kawo mtsalolin da muka fuskanta ya yin gudanar
da wannan bincike a ƙarshe kuma na kammala
wannan babi ne ta hanyar naɗe tabarmarsa.
A babi na biyu kuwa bayan an shimfiɗa
tabarmar wannan babin, sai muka shiga yin bitar waɗansu
ayyuka na masana da manazarta waɗanda suka danganci wannan
nazari, an yi bita kan aro da ƙirƙira da kuma bita kan Hausar rukuni. A ƙarshe kuma an kammala wannan babi da naɗe
tabarmarsa.
Babi na uku bayan shimfiɗarsa ya yi bayani kan
tsarin gudanar da bincike da adadin bayanan da aka tattara a lokacin da gudanar
da aikin da hanyoyin tattara waɗannan bayanan, cikin
babin dai an kawo yadda aka tattaro bayanan da kuma bayan samuwar bayanan
hanyoyin da akabi wajen sarrafa waɗannan bayanai da muka zaƙulo su. A karshe shima an yi kamar sauran babi an
naɗe
tabarmarsa.
Babi na huɗu mai laƙabi jadawalin bayanai an rarraba irin kalma ko
kalamin da aka samo daga wannan rukuni na ‘yan siyasae arewacin
Najeriya kan hanyoyi guda uku ta ɗaya kalmomin da aka faɗaɗa
ma’anarsu da na biyu ƙirƙirarrun kalmo daga na asali na uku kuma kalmomin
aro da aka sarrafasu a cikin wannan rukuni, haka aka samarwa kowannensu wani
jadawali don sauƙaƙa fahimtar manazarta da ɗaliban
ilimi. A ƙarshe aka naɗe
tambarmar babin.
Babi na ƙarshe, shi ne na biyar. A
cikin wannan babi akwai abubuwa uku: jawabin kammalawa, da shawarwari. Daga ƙarshe kuma manazarta wato litttafai da muƙalu da kundaye da sauran abubuwan da aka yi
nazari lokacin da ake gudanar da wannan binciken. A ƙarshe, ba za a manta da waɗanda
zanta da su ba, domin samo bayanai daga gare su.
5.2 Sakamakon Bincike
A wannan gaɓar ce za a kawo jerin
abubuwan da wannan nazari ya gano ko ya fahimta dangane da Hausar ‘yan
siyasarmu na arewacin Nijeriya. Ga wasu daga cikinsu:
Daga cikin mahimman masu amfani da Hausar ‘yan siyasa akwai:
‘Yan jam’iyyu daban-daban, da magoya bayansu da sauran jama’a.
Lokutan amfani da Hausar kan fara ne yayin yaƙin neman zaɓe,
ta hanyar tarukka, gangami da shirye-shiryen kafafen yaɗa
labarai da bayan kafa gwamnati. Haka kuma, samuwar kalmomi irin waɗannan
a jam’iyya na sa abokan adawa karaya. Kuma yin amfani da wasu
kalaman cikin jama’a kan kawo tashin
hankalin al’umma kamar yadda wasunsu ke kwantar musu da hankali.
Wannan nazari ya gano hanyoyin da Hausawa ‘yan siyasa ke
samar da wannan Karin harshensu na rukuni. Hanyoyin sun yi shafuwar aro da ƙirƙira
kamar haka: Sarrafa kalmomin Aro, da ƙirƙira sababbin kalmomi da kumafaɗaɗa
ma’anar kalmomin asali
Mawaƙa da kafafen yaɗa
labarai sun taimaka wajen samuwa da ƙara
yaɗa
Hausar ‘yan siyasa ta fuskoki daban-daban.
Hausar da ‘yan siyasa ke sarrafawa wadda ta sha bamban da
yadda ake amfani da ita a al’amurran yau da kullum. Sau da yawa sai an nemi
tafinta kafin a iya fahimtarta, musamman ga waɗanda ba su cikin wannan
rukuni. Ta haka samuwar wannan Hausar ke faɗakar da sauran jama’a
halin da rukunin ‘yan siyasar ke ciki.
Abubuwan da ke haifar da Hausar ‘yan siyasa: Adawa, da
tsokana, da kuma ƙoƙarin tallata jam’iyya ko ɗan
takara da mayar da martani.
Hausar ta ƙara bunƙasa harshen Hausa. Dalilin siyasa an samu
wadatuwar kalmomin fannu da zantukan waɗanda suka danganci siyasa
da mulki.
Hausar ta ƙunshi gamin-gambizar
harsuna uku Hausa, da Larabci da kuma Ingilishi.
Jinsin maza a rukunin ya fi na mata samar da kalmomin amma
kuma wajen yaɗa su ga al’umma samari da ‘yan mata ne don su
suka fi kowa yin amfani da su.
Samuwar kalma ɗaya a wannan rukunin, ta
hanyar sukar abokin hamayya ko zolayarsa na haifar da samuwar a ƙalla sababbi da dama, musamman wajen ƙoƙarin mayar da martini a
tsakanin ‘yan siyasa.
Hausar na bayyana manufofin ‘yan siyasa da jam’iyyunsu domin
yawaitar irin waɗannan kalmomi a bakunan
jama’a kan sa a gane magoyaban kowace jam’iyya.
Kalmomin siyasa na zama hannunka mai sanda ko gargaɗi
ko nuna adawa kan salon mulkin shugabanni.
Yawan amfani da waɗannan kalmomin a bakin ɗan
takara kan sa a gane cewa, ya taɓa
riƙe wani muƙami
ko kuwa tazarce yake son yi ko kuma wannan shi ne karonsa na farko na yaƙin neman zaɓe.
Wata Hausar kan bayyana salon mulkin da ‘yan siyasar ke da ƙudurin yi wa al’umma.
Amfani da irin waɗannan kalmomi ga ‘yan
siyasa kan zama kamar wani gishirin zance ne a cikin bayaninsu wanda in ba su
surkinsu a kai-a kai zancensu zai zama lamin zance.
5.3 Shawarwari
Kamar yadda aka sani, yin tsokaci kan wani abu ko wani lamari
yana sa jama’a su farga idan ba a san abin ba a sani. Idan kuma ana sane, sai
aka yi waste da shi, sai ya zama wata hanya ta tunatarwa ga al’umma game da
mahimmancin wannan abun. Wannan aikin ya nuna wa waɗanda
ba su sani ba cewa, wannan rukuni na ‘yan siyasa ya taka rawa matuƙa a cikin harshen Hausa musamman wajen bunƙasa shi da aro da ƙirƙira. Domin duk harshen da ke aron kalmomi daga
wani harshe, to wata rana zai ba da mamaki.
Kasancewar harshen Hausa shi ne harshe na biyu daga cikin
manyan harsunan da ake amfani da su a nahiyar Najeriya. Don haka, duk harshen
da ake buƙasa shi da kalmomin aro
da ƙirƙararru
to kuwa shima ya kusa ga kai wa fagen manya a duniya.
Haka kuma, tanadi wajen inganta harsunan mutane ba shi da
babbanci da inganta rayuwar al’umma gaba ɗaya. Domin harshen Hausa
saboda tanadin da aka yi masa ya sa a yau al’ummar Hausawa da ma harshen Hausa
suka kasance ja-gaba a nahiyarmu ta Najeriya. Binciken ya nuna cewa, ba
al’ummar da ta fi yawan amfani da harshenta a nahiyar Najeriya, irin al’ummar Hausawa.
Muna fatan a samu kafuwar wata hukuma mai kula da irin waɗanan
baƙin kalmomi domin watsa su cikin al’ummar
da ba su san irin wainar da ake tuyawa ba a rukunin a ƙoƙarin samun haɓaka harshen Hausa.
A ƙarshe, muna kyautata
zaton wannan aikin zai taimaka ga ɗalibai masu sha’awar
nazarin harshen Hausa. Allah Ya sa aikin ya yi amfani da dukkan al’umma
baki ɗaya.
5.4 Naɗewa
Kamar yadda bayanan cikin wannan babi suka nuna a sama, babin
ya tattauna bayanai a kan waiwayen abubuwan da nazarin ya ƙumsa, da abubuwan da aka gano daga Hausar ‘yan
siyasa da kuma shawarwarin
bincike.
MANAZARTA
RUKUNIN LITTAFAI:
Arnett, E.J. 1972. Gazzetters Of Northern Provinces Of
Nigeria: Vol. 1.
London: Frankcass.
Bargery, G.P. 1934. A Hausa-English Dictionary And
English-Hausa Dictionary Vocabulary. Zaria: Ahmadu Bello University Press
Limited.
Fage, U.U. 2002. Ire-iren Karin Harshen Hausa na Rukuni. Kano:
Benchmark Publishers Limited.
Fagge, U. U. 2012. Hausa Language and Linguistics. Zaria:
Ahmadu Bello University, Press Limited.
Fishman, J. (ed) 1972. Reading In sociology Of Language.
Mouton Paris
Gee, P. J. 2014. An Introduction to Discourse Analysis Theory
and Method. Fourth Edition. London: Routledge.
Imam, A.G. 2009. Asalin Aro, Ma’anarsa da Ire-Irensa.
070-66182880: Kano.
Kirk-Green, A.H.M. 1966. The Emirates Of Northern Nigeria.
London: Oxford University.
Muhammad, D. (ed.) 1990. Hausa Metalangauge’ (ƙamus na Keɓaɓɓun Kalmomi). Ibadan: University Press.
Sa’id, M. (ed.). 2006. ƙamusun
Hausa Na Jami’ar Bayero. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar
Bayero.
Skinner, N. 1965. ƙamus
Na Turanci Da Hausa-English, Hausa Illustrated Dictionary (Babban Jagora Ga
Turanci). Zaria: Northern Nigerian Publishing Company Ltd.
Yakasai, S.A. 2012. Jagoran Ilmin Walwalar Harshe. Sokoto:
Garkuwa Media Services
Yule, G. 1985. The Study of Language: An Introduction.
Australia:
Cambridge University Press.
.
RUKUNIN MAƘALU
Abba, T. 2013. "Coinage And Neologism in Kano
Politics" A Paper Presented at the 1st National Conference on Hausa
Language, Literature and Culture, Organized by the Centre for the Study of
Nigerian Languages, Bayero University, Kano. Held on 14th-16th, January, 2013.
Abbas, N.I. da Umar, M.M. 2016. ‘Harshe da Siyasar Canji A
Arewacin
Najeriya’ A Paper Presented at the 1st National Conference on
tha Role of Language, History And Religion in the Development, Integration and
Security of Nigeria. At Usmanu Ɗanfodiyo University,
Sokoto, held on 1st -3rd March, 2016.
Bature, A. 2013. "Sababin Kalmomi a Hausa" A Paper
Presented at the 1st
National Conference on Hausa Language, Literature and
Culture, Organized by the Centre for the Study of Nigerian Languages, Bayero
University, Kano. Held on 14th-16th, January, 2013.
Busa, A.M. 2013. "Hausa Loans Words In Gbagyi" A
Paper Presented at the 1st National Conference on Hausa Language, Literature
and Culture, Organized by the Centre for the Study of Nigerian Languages,
Bayero University, Kano. Held on 14th-16th, January, 2013.
Dambo, 2013. "ƙirƙirarrun Kalmomin Hausa Ina Makomarsu" A Paper
Presented at the 1st National Conference on Hausa Language,
Literature and Culture, Organized by the Centre for the Study of Nigerian
Languages, Bayero University, Kano. Held on 14th-16th, January, 2013.
Ɗantumbishi, M.A (ba shekara) ‘Neologism In Hausa’ Department
of
Nigerian Languages, Usmanu Ɗanfodiyo
University Sokoto
Salihi,T.M. 2013. "Baƙin
Kalmomi da Gamin Gambiza Daga Turanci Zuwa Hausa" A Paper Presented at the
1st National Conference on Hausa Language, Literature and Culture, Organized by
the Centre for the Study of Nigerian Languages, Bayero University, Kano. Held
on 14th- 16th, January, 2013.
Umar, M.M. 2013. Hausar Masu ƙwallon
ƙafa a Cikin Garin Sakkwato.
Maƙalar da Aka Gabatar a
Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya.
Jamai’ar Usmanu Ɗanfodiyo,
Sakkwato.
Yakasai, M.G. 2013. "Adon Harshe a Fagen Dimokuraɗiyya
a Kano" A
Paper Presented at the 1st National Conference on Hausa
Language,
Literature and Culture, Organized by the Centre for the Study
of Nigerian Languages, Bayero University, Kano. Held on 14th-16th, January,
2013.
Yakasai S.A. 2003. ‘Sadarwa Tsakanin Maza da Mata’ Takardar
da Aka Gabatar a taron ƙarawa Juna Ilimi, Sashen
Nazarin Harsunan Najeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato, 2 ga Oktoba 2003.
Yakasai, S.A 2005. “Aro da ƙirƙira: Nazarin Samuwar Sababbin Kalmomin Hausa a
Jami’a da Kuma Garin Sakkwato”: MaƘalar da Aka Gabatar a Sashen Nazarin Harsunan
Nijeriya. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
RUKUNIN KUNDAYE
Aliyu, U. 2007. ‘Kalmomin Aro na Zamani’ Kundin Digiri na Ɗaya. A Sashen Nazarin Harsunan Najeriya, Jami’ar
Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato, Najeriya.
Asara, G.M. 2013. Hausar Dillalai a Jihar Sakkwato. Kundin
Digiri na Biyu. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Besse, K.M. 2015. ‘Dangatakar Harshe da Siyasa a Sakkwato’
Kundin Digiri na Ɗaya. A Sashen Nazarin
Harsunan Najeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo
Sakkwato, Najeriya.
Garba, S.A. 2010. ‘Hausar Gidan Rediyo BBC’ Kundin Digiri na
Biyu. Sashen Nazarin Harsunan Najeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato, Najeriya.
Giro, M.M. 2012. ‘Aron Kalmomi da Tsofaffin Kalmomin Hausa A
Littafin Mace Mutum’ Kundin Digiri na Ɗaya.
A Sashen Nazarin Harsunan Najeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato, Najeriya.
Sirajo, I. 2001. Hausar Kasuwanci: Yanayin ƙirƙirar
Sababbin Kalmomi a Kasuwar Garin Sakkwato. Kundin Digiri na Ɗaya. Jami’ar Usman Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Yakasai, S.A. 1999. Language Across Two Borders: A
Sociolinguistic Study of Hausa in ƙonni
And Illela Border Towns. PhD Thesis. Bayero University, Kano.
Zailani, A.A. 2012. ‘Hausar Kan Titi’ Kundin Digiri na Biyu.
A Sashen Nazari Harsuna Da Al’adun Afrika, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya.
Najeriya.
1 Comments
[…] Karanta wani […]
ReplyDeleteENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.