Ticker

6/recent/ticker-posts

Jirwayen Kishi a Wasu Wakokin Baka Na Mata

Article Citation: Bakura, A. R., & Sani, A.-U. (2025). Jirwayen kishi a wasu waƙoƙin baka na mata. Danyamusa Journal of Current Research in Hausa Studies, 5(1), 90–109. ISSN: 2814-2306.

JIRWAYEN KISHI A WASU WAƘOƘIN BAKA NA MATA

Daga

Adamu Rabi’u BAKURA, Ph.D.
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau
Arbakura62@gmail.com & adamubakura@fugusau.edu.ng

Da

Abu-Ubaida SANI, Ph.D.
Department of Languages and Cultures,
Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | official@amsoshi.com
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736

Tsakure

Manufar wannan takarda ita ce fito da hoton ɗabiar kishi a wurin matan Hausawa. An yi garkuwa da wasu waƙoƙin baka na musamman da suke gudanarwa domin ganin wannan hoto na kishi. Kadadar nazarin ta taƙaita ga laluben kishin da ya bayyana a waƙoƙin da suke gudanarwa a lokutan wasu al’adu kamar na daɓe da raino da kuma gaɗa. An yi haka ne domin fayyace yadda kishi yake a rayuwarsu da kuma a yanayin zamantakewarsu. Takardar ta yi amfani da hanyoyin tattara bayanai waɗanda suka haɗa da hira da sauraren waƙoƙi daga bakin wasu daga cikin matan da suke rera su. Haka kuma, an dubi wasu daga cikin ayyukan da magabata suka gudanar a matakan ilimi daban-daban domin a naƙalci batun da ake nazari, sannan kuma a cike giɓin da ake da shi a wannan fage. Binciken ya gano cewa, akwai nason kishi a cikin wannan ɓangaren adabin baka. Bugu da ƙari, tasirin da kishi yake da shi a wurin mata, shi ne ya sa ya shiga cikin waƙoƙin da suke gudanarwa na musamman. Daga ƙarshe, takardar ta ba da shawara ga jami’o’i da hukumomin adana tarihi da al’adu da masana a kan su bayar da cikakkiyar kulawar da ta kamata don ganin an zurfafa bincike wajen gano ɓirɓishin kishi a sauran ɓangarorin adabin Hausa.

Fitilun Kalmomi: Waƙa, Waƙoƙi na Musamman, Kishi, Adabin Baka

1.0 Gabatarwa

Ɗabiar ɗanadam ta ƙaunar shahara a wani fanni na zamantakewa ko kuma na rayuwa, ita ce ta buɗe masa sha’awar yin kere ta yadda zai zarce kowa a cikin tsaransa da ma waɗanda suka girme shi. Shi ne dalilin da ya sa wasu mutane sukan yi tsayin daka wajen ganin sun zama makaɗaita a wasu fannoni na rayuwa. Ga alama, yanayin ɗanadam na son zaman lafiya ba tare da ya fuskanci cutarwa daga wani ba, kamar yadda shi ma ba ya ƙaunar musguna wa wani, shi ne ya ba shi karsashin yin kaffa-kaffa da yanayin da aka tsinci kai. Hasali ma, wasu daga cikin mutane sukan zaɓi rayuwa cikin kaɗaici, saboda suna tunanin shiga cikin mutane yakan kawo kishi da juna. Kamar dai wasu al’ummu na Larabawa da dangoginsu, matan Hausawa suna cikin rukunin jinsin da ba sa maraba da samun kishiya a zamantakewarsu ta aure da sauran mu’amalolinsu.

Idan an lura da fasahohin Hausawa na tatsuniya, wata makaranta ce da take nuna irin yadda mata suke baya-baya da zama da kishiya. Hakan shi ne ya sa Gizo ba shi da wata mace da ta wuce Ƙoƙi. Ke nan, rashin ƙaunar zama da kishiya da kuma kishi a wurin mata yana da tushe idan aka bibiyi labarai da waƙoƙin baka na Hausawa. A bisa haka ne kuma wannan takarda ta dubi jirwayen kishi a cikin wasu waƙoƙin baka na mata waɗanda suka haɗa da, na daɓe da reno da kuma na gaɗa. Takardar ta karkata akalarta wajen waƙoƙin baka na musamman, domin kallon ɓirɓishin kishi a cikinsu.

1.1 Bita

 Ƙoƙarin takardar na fito da bayanan da ta ƙuduri aniyar fayyacewa, shi ne ya sa ta bayyana maanonin muhimman kalmomin da aka gina taken bincike a kansu. An yi haka ne, saboda a samu sauƙin fahimtar alƙiblar da takardar ta dosa. Kalmomin da aka bayyana ma’anonin nasu a wannan muhalli su ne: Waƙa da waƙa ta musamman da kuma kishi.

1.1.1 Waiwaiyen Ma’anar Waƙa

A lugga, waƙa tana nufin, “furta abin da ke cikin ƙwaƙwalwa” (Bargery 1993, sh. 1075). A wata ma’anar kuwa, waƙa takan kasance wata murya ko zaƙin murya mai shiga zuciya da faranta rayuwa. Misali, Bahaushe yakan ce:

        i.            Ai na zaci waƙa ce.

      ii.            Ya matse sauti kamar, mai waƙa.

    iii.            Zaƙin murya sai ka ce zabiya.

Ta wata fuskar kuwa, waƙa takan kasance wata magana wadda akan rera da baki, aka tsara bisa wani zubi na musamman, kamar yadda Garba (1990 sh. 152) ya bayyana.

Idan aka dubi ma’anar waƙa a mahangar fannin adabi kuwa, za a tarar cewa, masana adabin baka da dama sun bayyana maanarta a wurare mabambanta, gwargwadon fahimtarsu. Daga cikin masanan, Gusau (1984 sh. 4) inda ya bayyana ma’anar waƙar baka cewa:

Waƙar baka ita ce wani saƙo cikin zance na azanci da ake rerawaBa faɗa kurum ba, ta cikin hikima da fasaha da zaɓaɓɓun kalmomi, Waɗanda suka dace da saƙon. Kuma tana zuwa gunduwa-gunduwa, Dangane da sautin murya da kiɗa da amshi da gaɗa da taɓi ko zabi--yanu, mai saka zuciya jin daɗi

Shi kuwa Umar (1987, sh. 28) cewa ya yi:

“Waƙa ita ce nauin sarrafaffen harshe da ake gabatarwa da sigar gunduwoyin zantukan da ake kira baitoci ko ɗiyoyi, waɗanda ake ginawa a kan kari ƙayyadadde, kuma ake rerawa da wani irin sautin murya na musamman.”

Ta la’akari da waɗannan maanoni, wannan takarda tana iya cewa, waƙa ita ce ta kasance tsararriyar magana da ke ƙunshe da fasaha da hikima da ake rera ta, gunduwa-gunduwa, cikin wani amo na musamman.

1.1.2 Waƙoƙi na Musamman

Waƙoƙi na musamman su ne waƙoƙin da tun can asalatan, su aka fi sani a farfajiyar ƙasar Hausa. Waƙoƙi ne waɗanda ake aiwatar da su a keɓaɓɓantu lokuta. Gusau (2024 sh. 9) ya bayyana su a matsayin waƙoƙin da “... ake rerawa a lokutan da ake gudanar da wasu keɓantattun ayyuka na rayuwa ta zamantakewa da kuma ta zaman aure.” A taƙaice ke nan, waƙoƙi na musamman ana gudanar da su ne a wasu ayyanannun lokuta. Ire-iren waɗannan waƙoƙi sun haɗa da:

i.                    Waƙoƙin daɓe[1]

ii.                  Waƙoƙin daka

iii.                Waƙoƙin gaɗa[2]

iv.                Waƙoƙin niƙa

v.                   Waƙoƙin raka amayar

vi.                Waƙoƙin reno[3]

vii.              Waƙoƙin tashe, da sauransu

1.1.3 Kishi

Bargery (1993) ya bayyana kishi a matsayin “ganin ƙyashi a tsakanin kishiyoyi.” Ya ci gaba da kawo rabe-raben kishi da suka haɗa da kishin birni da kishin kai da kishin sauri da kuma kishin zuci.” Bakura (2014 sh. 8) ya rawaito Tambuwal inda aka bayyana ma’anar kishi da cewa: “Abu ne da ke cikin zukatan al’umma, dabbobi, da ƙwari wanda ya ƙunshi jiyewa (ganin ƙyashi) a kan wani abu da suke tarayyarsa.” Gwargwadon yadda aka fahimci waɗannan ma’anoni, ana iya cewa kishi wani yanayi ne da zuciya ke shiga na son ganin an samu ɗaukaka sama da sauran tsara tare da yin hamayya da duk wani mai yunƙurin kamo ta ko tarayya da ita a farfajiyar ɗaukaka ko jin daɗinta. Kishi na iya kasancewa hanya ta gwagwarmaya da ke tattare da zargi da tuhuma da saɓani da rashin jituwa da husuma da mugun nufi, domin ƙoƙarin kare keɓantacciyar ƙauna ga abin so ba tare da yin tarayya da wani ba.

2.0 Dabarun Gudanar da Bincike

An taƙaita wannan bincike kan nazartar kishi a cikin waƙoƙin baka na musamman. Wannan yana nuna cewa, ba a nazarci sauran nau’ukan waƙoƙi ko adabi da suka kawo hoton kishi ba. A bisa haka, duk matanonin da aka dogara da su domin ƙalailaice lamarin kishi a wannan mahanga sun fito ne daga waƙoƙin baka na musamman.

Maganar Hausawa da suke cewa: “Gani ya kori ji” wata maɓuɓɓuga ce da take nuna ƙwarewarsu wajen tantance gaskiyar bayanai. Sakamakon cewa, a tunaninsu, ganin abu yakan hana karɓar jita-jitar da a ƙarshe takan zama hadisin Bamaguje. Bisa ga haka, wannan takarda ta yi ƙoƙarin tuntuɓar mata tsofaffi da waɗanda suka kwana biyu, domin jin wasu bayanai daga gare su a matakin farko. Bugu da ƙari, an yawata wuraren da ake rera waƙoƙin da suka danganci gaɗa da raino, inda aka naƙalto wani abu daga gare su.

Haka kuma, takardar ta yi laakari da cewa, magabata sun gudanar da ayyuka da dama masu alaƙa da kishi. Haka ya sa aka leƙa wasu daga cikin ɗakunan karatu, inda aka dubi rubuce-rubucen da aka riska a matakan ilimi daban-daban. Takardar ta yarda da maganar Hausawa da suke cewa, matambayi ba ya ɓata inda ta tuntuɓi wasu masana da suka ratsi aladun Hausawa. Kasancewar wannan zamani da ake ciki na amfani da wayar hannu da sauran hanyoyin sadarwa, an yi amfani da su, kuma hakan ya taimaka wa masu bincike ta fuskar tattaro bayanai.

3.0 Muhallin Kishi a Waƙoƙin Baka na Mata

A ƙoƙarin wannan takarda na laluɓen gurbin kishi a cikin waƙoƙin baka na mata, an kasa waƙoƙin baka mata zuwa manyan gidaje guda biyu kamar haka:

        i.            Waƙoƙin manyan mata

      ii.            Waƙoƙin ‘yan mata

3.1 Kishi a Waƙoƙin Manyan Mata

A nan waƙoƙin manyan mata na nufin ire-iren waƙoƙin da manyan mata suke rerawa. Yawanci sukan rera su ne a lokacin aikace-aikace daban-daban. Kamar yadda Sani (2025 sh. 21) ya kawo, mata sukan yi amfani da ire-iren waƙoƙin nan domin huce takaici da fito da abubuwan da suke ƙunshe a cikin zukatansu. Misalan ayyukan sun haɗa da: daɓe da reno da lugude da niƙa da sauran makamantansu.

3.1.1      Kishi a Waƙoƙin Daɓe

Daɓe wata tsohuwar al’ada ce da Hausawa suka gada kaka da kakanni. Wannan al’adar ana aiwatar da ita ne a yayin da aka gina sabon ɗaki. Mata sukan taru inda za su riƙa zuba tsakuwa (birji) da ruwa (yayyafawa ruwan ake), tare da daddakawa ta hanyar amfani da waɗansu kayan aiki masu kama da taɓarya. Za su yi ta faman dakawa har ɗakin ya yi sumul-sumul, kamar an sanya siminti.

A mafi yawan lokuta, tsofaffi da mata masu matsakaicin shekaru aka fi gayyata wajen daɓe. Hasali ma dangin amarya da abokan arziki ne sukan aiwatar da shi. Suna gudanar da shi a ƙarƙashin jagorancin wata mace da sukan yi wa laƙabi da suna Lula. Ita Lula, duk wurin da ta daɓa ba wata mace da za ta sake bi ta kansa, saboda ya daɓu. A yayin da ake aiwatar da daɓen akan samu ɗaya daga cikin matan ta riƙa bayar da waƙoƙi, sauran mata suna amsawa. Mai ba da waƙar ita ake kira zabiya.

Waƙoƙin daɓe suna da nasu sigogi kamar yadda sauran rukunoni na waƙa suke da nasu. Gusau, (2008, sh. 226) ya fito da wani abu da ya danganci sigogin waƙoƙin daɓe, inda yake cewa: Waƙoƙin daɓe sukan ƙunshi begen wasu mutane da zambo ga abokan hamayya da habaice-habaice ga kishiyoyi da kalmomin batsa har da na zage-zage da na raha da annashuwa.” Abu ne mai matuƙar wuya a sami waƙar daɓe tun daga farkonta har zuwa ƙarshe ba tare da an samu habaici ko zambo a cikinta ba.

Ɓullar habaici da zambo a cikin waƙoƙin mata, shi ne yake kawo samun ɓirɓishin kishi a cikinsu. A mafi yawan lokuta, duk lokacin da mace za ta yi habaici ko zambo, babu inda zai faɗa idan ba a kan kishiyarta ba, ko kuma uwar mijin da suke takin-saƙa da juna. A duba misali a cikin wannan waƙar da take ƙasa:

Ya Bisimillahi zan fara,

Na fara da sunan Allah,

Du aikin da ba Bisimillah,

Bai ƙarko bare ƙarshen ƙwarai,

A kore! A kore! A kore mana uwargida,

Ko tana da mageduwa.

Ran kwanan gadon miji tsoron baya,

Ya ba ni, ya ga arkane!

Ko da baƙin ciki za ya kashe ta,

Sai ta gan ni a wannan gida.[4]

Idan aka dubi ɗiyan waƙar da suke sama, za a ga yan daɓe sun nemi a saki uwargida. Ba don komai suka yi hakan ba, sai gudun kar ta haddasa wa amarya wata cuta da suka kira mageduwa.[5] Wannan ya nuna ƙarara irin tsabar ƙyama da mata suke nuna wa kishiya wanda ya haifar da ‘yan daɓe suke neman a saki uwargida. Hasali ma, sukan yi mata arashi da cewa amaryar ta zo da shirin zama daram a wannan gida. Haka kuma, sun bayyana yanayin da uwargidan za ta fuskanta na damuwa, saboda tarewar amarya a gidan mijin.

Ga al’adar waƙoƙin mata na daɓe, sukan zambaci uwar gida da amarya. A lokaci guda kuma, akan kai wa uwar miji farmaki. Wannan yakan faru ne kasancewar mata da dama suna ɗaukar uwar mijji a matsayin kishiyarsu, kamar yadda wasu daga cikin iyayen maza mata suke ɗaukar matan ‘ya’yansu a matsayin kishiyoyinsu. Hakan ya sa ake samun adawa da juna, har ake jin amon lamarin a cikin waƙoƙin daɓe. Misali:

Uwar miji ta zama bunsuru,

Tana bobowa,

Ta faɗa cikin tukunyar tsaba,

Tana ta yin bobowa,

Har shigifa ta tsage.[6]

Idan an lura, shaɗara ta uku a wannan waƙa ta bayyana yadda masu daɓen suka siffanta mahaifiyar maigida da bunsuru. Hakan yakan faru ne saboda yadda take shiga cikin lamuran gudanar da harkokin gida. Shigar tata takan hana matar miji (surukarta) rawar gaban hantsi, ta yadda shawararta ba za ta zama karɓaɓɓiya ba.[7] Kishin irin wannan katsalandan shi ya sa suka yi wa uwar miji zambo ta hanyar siffanta ta da bunsuru, mai kuka, wanda ya janyo ɗaki ya tsage. Haka kuma, waƙar ta bayyana yadda suke nuna ƙyamarsu ga irin iyayen miji mata waɗanda suke shigar sugula, wajen bayar da abinci.

 A fage guda kuma, masu daɓe sukan taka wata muhimmiyar rawa wajen ruruta (haɓaka) wutar kishi ta hanyar waƙoƙin da suke rerawa. Sau da yawa, sukan yi wa uwar gida gugar zana a yayin da suke gudanar da daɓe, ta hanyar yabon amarya. Duk sukan yi haka ne domin su taya ‘yar’uwarsu kishi, kamar yadda yake a cikin waƙar da suke cewa:

Na gan ki kina mur-mur,

Kawo ruwa mu daɓa.

 

Ko uwargida ba ta so ba,

Kowa ƙasa mu daɓa.

 

To uwargida a ɗau haƙuri,

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Don uwargida ba ta so,

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Ai zaman kishiya sharri ne,

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Na ga ana zurum ba magana,

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Kai su oh-oh dai an tsufa,

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Wai ko ana kishi ne?

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Lallai kishi ya ci su oh-oh!!

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Wai kishin mi kika yi ne?

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Ko kishin uwa kika yi ne?

Kawo ƙasa mu daɓa.

 

Tana kishin gida da uwa ne,

Kawo ƙasa mu daɓa[8].

Tirƙashi! Da wahala a samu macen da za ta ji waɗannan kalamai kishi bai yunƙuro mata ba. Domin ko ba komai, jeregen waƙar ya nuna cewa, ‘yan‘uwan amarya suna ganin zama da uwar gida sharri ne. A bisa haka ne suka yi mata habaici da cewa, ta tsufa. A ɗabiance ko mace ta kai shekara sittin ba ta son a kira ta tsohuwa. Hasali ma sukan fito fili ƙarara su ce, wai uwar gida tana jin haushin maigida ya yi amarya, saboda ta tsufa. Babu shakka duka waɗannan ɗiyan waƙa suna fito da yadda ‘yan’uwan amarya suke taya ta kishi.

3.1.2 Kishi a Waƙoƙin Reno

Ga al’ada, waƙoƙin reno suna ƙunshe da zambo da habaici domin amayar da abin da yake cikin zuciyar mai tawai. Waɗannan waƙoƙi sukan bayyana hoton yanayin da mace take ciki na rashin jituwa a tsakaninta da sarkuwa ko kishiya ko miji da ‘yan’uwansa. A ƙoƙarinta na neman kare kanta ko ‘ya’yanta daga tsangwamar mutanen gida, takan gudanar da waƙe-waƙe a lokacin da take renon ɗanta, saboda ta huce haushinta, ba tare da jin kunya ko tsoro ko kuma fargaba ba.

Mata sukan gina waƙoƙin reno ta hanyar amfani da tubalin kishin uwar miji. Wannan yakan faru ne idan mace ta fahimci uwar mijinta tana yi musu katsalandan a cikin harkokin gudanar da gida. Wani lokacin kuma uwar kan yi wa ɗanta hannunka-mai-sanda ne kawai, ta hanyar tsawatar da shi a kan ɗauko salon rayuwar da bai dace da shi ba. Ire-iren waɗannan dalilai ne suke sa matar ɗa ta ɗauki karan tsana ta ɗora wa uwar miji, kamar yadda yakan auku ga kishiya. Shi ne kuma dalilin da ya akan wayi gari a ji tana yi wa sarkuwa habaici ko zambo cikin waƙa, a yayin da take renon abin goyonta. Misali:

E lale lale,

Aminu sha nononka,

Ba na awaki ne ba,

Ba na jakkai ne ba,

Gobe gida can za mu,

Tun da abin dai ƙi ne.

Gidanku ne dolenka,

Gidanmu ni dolena,

In har an yaye ka,

Sai ta shigo ɗakina,

Ta ɗauki duk aikina.

In ka girma ina nan,

Za ka biya min arfa,

Har Haji in ya samu,

Kowa ba ya hanawa,

Allah don ikonka,

Raya Aminu nawa[9].

A nan, kishi ne ya yunƙuro ya rufe wa matar ɗa ido har take ce wa surukarta, idan ta tafi gidansu, to ita surukar ta zo ta maye gurbinta. Wannan waƙa da makamantanta, kishi ne yake haifar da su.

A wasu lokuta kuma, mata sukan gina waƙoƙin reno ne domin su mayar da martani ga kishiya. A ire-iren waɗannan waƙoƙin za a tarar cewa, suna ƙunshe ne da habaici ko zambo ga kishiya, tare da nuna kushewa a kan ‘ya’yanta. Hasali ma mai waƙar tana ɗaukaka ɗanta ko ‘yarta, yayin da a ɗaya ɓangaren take nuna kasawar kishiya tare da ƙasƙantar da ‘ya’yanta, kamar yadda za mu gani a cikin wannan waƙar:

Ke ce ‘yar gadangama,

Sai a ɗora ki gaban gado,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Allah shi ya ba ni ke ba wani ba,

Dole ne a sa ki gaban gado

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Ga ki kyakkyawa, abin son gani gun kowa,

‘Yar kura sai baƙin jini ga muni,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.[10]

Waɗannan ɗiyan waƙa da suke sama sun siffanta kishiya da wata dabbar daji, wato kura wadda a duk tarsashin namun dawa ba mai baƙin jini kamarta. Duk da kasancewarta mai ƙarfi sosai, ta kasance matsoraciya. Ba ta yarda da yin faɗa da kowa ba, sai ƙananan dabbobi da marasa lafiya. Ba ta da zuciyar farauto wa kanta abinci, sai ta yi ta raɓe-raɓen neman mushe. Hasali ma har takan kai ga tona kaburbura. Irin wannan siffantawa an yi ta ne domin ƙasƙantar da kishiya.

Waƙar ta ci gaba kamar haka:

An ce ɗan hakin da ka rena da ma,

Shi ne wanda za ya tsone idonka,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Bilkisu kin riga kin yi sa’a,

Sai dai kawai a bi ki a baya,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Ga ki nan, ki wataya, ki yi yawo,

Mahassada na kallo,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Su wance da an yi lamo,

Ana jiran mu ji kunya,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Farin wata sha kallo,

Bilkisu ‘yar Ibrahim,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Zara kin fito gari ya waye,

Tauraruwar gabas mai haske,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Sai mu zo mu yi murna,

Ga farin-wata ya ɓullo,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.[11]

Dubi yadda kishiya take ɗaukaka yarta ta hanyar siffanta ta da wata babbar tauraruwa da take duniyar samaniya, mai tsananin haske da take fitowa kusa da wata (wato Zara). A ɗaya gefen kuma, ta yi ƙoƙarin ƙasƙantar da kishiya da ‘yarta a inda ta ke cewa:

‘Yar ballagaza ana shirin a yi ƙwambo,

Ga shi ba abin sai kuri

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Sai ku zo, ku yi kallo,

Kwalliya abin banza ce,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Mai kyau ko ba ƙyale-ƙyale abin kallo ne,

Sai ko zo, ku yi kallo,

Bilkisu ta fito tai kyawo,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Ran aurenki za a sha mamaki,

Domin ganin abin da na tara,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

Idan aka dubi waɗannan ɗiyan waƙar, za a tarar da an siffanta kishiya da mai aiwatar da lamurranta tamkar marar hankali. Hakan ya sanya duk wani tsarin da ta yi wa yarta na ado domin ta burge samari yakan kasance na banza. Ta kuma nuna irin kyakkyawar sifar da Allah ya yi wa yarta, wanda hakan ya wanzar mata da farin jini a tsakanin al’umma, ba tare da wasu ƙyale-ƙyalen sutura ba.

A wata fuskar kuma, kishiyar ta siffanta kanta da kare saboda yadda yake biye da ubangidansa sau-da-ƙafa tamkar mahaliccinsa. Abokin maigidansa amininsa ne. Kamar yadda yake adawa da abokin gabar maigidansa a kowane irin yanayi yake. Hasali ma yana da hikima da hazaƙa, inda yakan koyi duk wani abu da aka koya masa. An yi irin wannan kwatance ne a cikin waƙar saboda a bayyana yadda mace take tsananin kare mijinta daga duk wani aibu. Tana cewa:

An so a kori kare gun ɗunya,

To ga shi yau kare ya gane,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

Yayin da ta dawo kan ‘yarta kuwa, ta nuna duk abin da ta zayyana game da ita ba cika-baki ba ne. ‘Yarta ta shahara a tsakanin yayunta da suke uba ɗaya har ta zarta su. Hakan ya sa tilas su bayar da kai bori ya hau, saboda lamari ne daga Allah. Idan suka yi jayayya da hukuncin Allah kuwa, zai haifar musu da wulaƙanci da tozarta a cikin alumma. A dubi abin da take cewa:

Ba ni son yin fahari a kanki ‘yar Ibrahim,

Gudun nake mu yi sakaci,

A hau a tattaka mu,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Bilkisu kin riga kin yi fice,

‘Yan uba suna kallon ki,

Dole su bi ki a baya,

In sun ƙiya, suna yin kunya,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Duk wanda bai ajiye ba,

Idan yana son ɗauka,

Ku tabbata zai yi kunya,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

A ɗan waƙar da ke biye ta siffanta kishiyarta da jaki wanda ya kinkimo abin da ya fi ƙarfinsa. Hasali jaki yana daga cikin dabbobi marasa basira. Ga abin da take cewa:

Jaki da kayan taiki,

Ko ina za a nufa?

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Kin riga su kin ce Allah,

Balkisu kin riga kin zarce,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

To mahassada kun ji mu,

Bilkisu yau fa sai dai Allah,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.

 

Domin fa kun riga kun yi sake,

Domin mai ba mu shi ne Allah,

In mun rasa fa sai mu kira shi,

Ku zo, ku zo, ku yi kallo.[12]

Idan aka yi nazarin wannan waƙar za a tarar tana tattare da habaici da zambo ga kishiya da ‘ya’yanta. Ba wani abu ne ya kawo su ba face kishi. Sakamkon ƙyama da tsabar kishi, har kishiya takan ka da baki ta kira kishiyarta da suna “ballagaza.” Kazalika, an ga yadda amfani da waƙoƙin reno ya jawo mata suke ƙoƙarin ruruta wutar kishin ‘yan-uba ta hanyar nuna kasawar ‘yan‘uwan jaririn da ake yi wa tawai, kamar yadda ya zo a cikin wannan waƙar.

Kishi a tsakanin matan mutum ɗaya yakan ɗauki salailai mabambanta ta fuskar yadda sukan gabatar da shi. Sau da yawa idan kishi ya yunƙuro wa mace, sai ta tsiri tawai tana yi wa kishiya arashi ta hanyar la’akari da irin jinsin ‘ya’yan da take haifa. Misali idan mai tawai tana haihuwar ‘ya’ya jinsin maza ne, idan kishiyarta kuma mata take haifa, sai kawai a ji tana arashi cikin waƙar da take yi a lokcin da take tawai, a inda za a ji tana cewa:

Ba ni ciki don Gwamma,

ba ni ciki don Adama,

Sai ƙodago abin jefayya,

Mai karab da kalme gona.[13]

Haka kuma, wasu matan sukan ce wa kishiya:

Ɗauki mai damuttsan banza,

Da ba su ɓarkata komai,

Ɗauki ki gwada mana yadda,

Kishiya ka lalacewa kamar

Hakin shinkafa.

Kauɗa ba a son ki sai ran taushe,

Galma ba a son ki sai ran aiki.[14]

Duk ire-iren waɗannan waƙe-waƙe ana yin su ne domin a nuna ƙyama ga kishiya. Bugu da ƙari, a fagen tawai ba a bar suruka a baya ba, domin ita ma takan yi wa jikanta. A yayin da suke yin tawai ne sukan amayar da ƙololon kishinsu da yake cikin zuciyarsu, musamman wanda ya shafi matar ɗa. Misalin irin waƙoƙin da suke yi su ne:

Da bagaruwa abin kirki ce,

Da mun sha ɗiya,

Wanda bai raga ma miji ba,

Balle matan gida.[15]

A nan za a fahimci cewa, uwar miji tana ƙoƙarin nuna munanan halayen matar ɗanta, don haka ne ta kwatanta ta da bagaruwa. Wannan yakan faru ne a sakamakon hamayyar da take tsakaninsu.

3.2 Muhallin Kishi a Waƙoƙin Baka na ‘Yan Mata

Wannan kaso kuma, ya ƙunshi waƙoƙin da ‘yan mata suke gudanarwa a cikin gaɗa. Ire-iren waɗannan waƙoƙin su ma suna da keɓaɓɓun lokutan da ake gudanar da su. Ga al’ada, an fi gudanar da waƙoƙin gaɗa a lokutan hasken farin wata da kuma na bukukuwan aure da na suna.

3. 2.1 Kishi a Waƙoƙin Gaɗa

Duk da kasancewar ‘yan mata ba su riga sun yi aure ba, kishi yana ɗaya daga cikin jigogin waƙoƙinsu. Wannan yana faruwa ne saboda damar da suka samu na amayar da abin da ba za su iya kauce masa ba, wato zama da kishiya. A al’adance da kuma tsarin addinin Musulunci, an bai wa namiji damar auren mata fiye da ɗaya. Wannan shi ya haifar da waƙoƙin ‘yan mata suke yi tattare da zagi da zambo da ƙyama ko ƙi ga kishiya.

Baya ga haka, idan an dubi yanayin waƙoƙin, za a tarar suna ƙunshe ne da saƙonnin manya a hannun yara. Hakan ya sa a duk lokacin da suke rera waƙe-waƙensu na gaɗa, za a zagi kishiya ko a yi mata zambo, a kuma ta’allaƙa duk wani mugun abu gare ta. Misali, a waƙar Abalilan cewa ake yi:

Yaraye alo nanaye yaraye alo,

Abalilan yaraye alo nanaye,

Na yi gaisuwa ta ƙi ta ƙyale,

Na yi sallama ta ƙi ta amsa,

Shegiya uwar ‘yan kishi,

Ba mijinki zan aura ba,

Sai na je na auri ubanki,

In yi kishiya da uwakki,

Dole na ki ce, abalilan,

Dole na ki ce min gwaggo (Yahaya, 1997, sh. 81).

A waƙar Zama-Wa-Zama, an bayyana irin rashin ragowar da ke akwai tsakanin kishiya da kishiya saboda tsananin kishi. Ga abin da ake cewa:

Zama-wa-zama na je ganin gida,

Na iske baba da inna a zaure,

Suna ƙidayar goro,

Sun ba shi goro goma,

Biyar a wannan hannu,

Wasu biyar a wannan hannu,

Babban cikinsu ya faɗi,

Na durƙusa in ɗauka,

Sai aka ce abin ba kunya,

Sai na ce uhum na bar shi,

Amma zuciya ba ta so ba.

 

Zama-wa-zama na je ganin gida,

Wata kishiya tsinanna,

Ta ce mu ga ɗanɗan namu,

Ɗanɗan namu har ya girma,

Sai na zakuɗo na ba ta,

Ta jujuwa ta yanke,

Sarar jini ya baltsa.

 

Zama-wa-zama sai ta haifi nata ɗanɗan,

Ta je ganin gida ta dawo,

Sai na ce mu ga ɗanɗan namu,

Ta zakuɗo ta ba ni,

Niko na jujuwa na fyaɗe,

Na kawo wuƙa na yanke,

Na ce na rama ƙetar kishi.[16]

Ba kawai an tsaya a ramuwar gayya ne ba; har ma akan bayyana kishiya a matsayin ɓarauniya. A waƙar A’isha ta Asshibi an nuna cewa kishiya ta yi sata, kamar yadda za a gani a ƙasa:

A’i ta Asshibi,

Mai ɗan jallo,

Ta yo, ta yo,

Mai ɗan jallo,

Ta yo sata,

Mai ɗan jallo,

Maza ku tare muna,

Mai ɗan jallo

Ihu ihu,

Mai ɗan jallo (Yahaya, 1997, sh. 81).

Ko bayan zargin kishiya da ake yi da ‘yan ɗauke-ɗauke ba, akan faɗaɗa zargin wani lokaci saboda kishi. Waƙar Jar Miya tana ɗauke da misali, inda ake cewa:

Bayarwa: Jar miya zan aura,

Amshi: In babu jar miya me zan yi da koriya?

 

Bayarwa: Uwar miji ta zagen,

Amshi: Na durƙusa ina nema mata gafara.

(Sani da Gobir, 2021, sh. 308)

A wannan gaɓa dukkanin ‘yan wasa za su durƙusa ƙasa, tamkar dai suna nema mata gafarar da gaske. Waƙa kuma za ta ci gaba kamar haka:

Bayarwa: Uban miji ya zagen,

Amshi: Na durƙusa ina nema masa gafara.

 

Bayarwa: Kishiya ta zagen,

Amshi: Na lillisa ta na juya ta,

            Na kai ta ofishin‘Yansanda,

            Sun lillisa ta sun juya ta,

            Shegiya‘yar banza,

            Sun kai ta lahira sai ga ta a duniya,

            Shegiya‘yar banza. (Sani da Gobir, 2021, sh. 308)

Za a tarar cewa ba a yi wa kishiya kowace irin nasiha/rangwame, saboda tsananin ƙin da ake yi mata. Hasali ma ba a nuna ana jin kunyar ta, domin akan fito gaba-gaɗi a yi mata duk wani abu na cin mutunci kamar yadda muka gani a waƙar da ta gabata.

A wasu waƙoƙin akan siffanta kishiya da mummunar sifa ta duk wani abu da bai dace ba. haka kuma, akan nuna rashin muhimmancin ɗan kishiya, kamar yadda yake a waƙar Ayye Mama Ayye Mama, a inda ake cewa:

Bayarwa: Ayye mama-Ayye mama

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Ayye mama-labo-labo

Amshi: Mamale iye.

Bayarwa: Ayye mama ta tafiyarta

Amshi: Mamale iye.

 

 

Bayarwa: Ba ta da inna, ba ta da baba

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Ba ta da ɗan ƙanen aikawa

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Sai ɗan kishiya taka aike,

Amshi: Mamale iye

 

Ko ɗan kishiya da kwabo-nai

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Sai ya murguɗa mata baki

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Sannan za a aike shi ya je

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Zama da kishiya tilas ne

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Ba don uwar gidana so ba

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Ka san kishiya ‘yar kishi ce

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Mai mugun hali, mai zunɗe

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Mai baki irin na kututta

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Da aure yana raka aure

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Da na bi ki mun tafi tare

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Sai dai kishiya nika tsoro

Amshi: Mamale iye.

 

 

Bayarwa: Ko tuƙin tuwo in koya

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Ayye mama labo-labo

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Ayye mama ta tafiyarta

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Sai wataran, idan mun sadu

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Da ni da kishiya ai faufau

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Da ni da kishiya ko sannu

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Sai in na gan ta in fyaɗe ta

Amshi: Mamale iye.

 

Bayarwa: Kuma in na gan ta in share ta

Amshi: Mamale iye.[17]

Ba nan kaɗai suka tsaya ba, sukan gina waƙe-waƙensu a kan tubalan kishin kai. Sukan faɗakar da kansu tare da yin kashedi ga irin ‘yan matan nan da suke sakar wa miyagun maza fuska. Ga misali a ƙasa:

Bayarwa: Mainaƙiye Mainaƙiye,

Amshi: Mainaƙiye.

 

Bayarwa: Mainaƙiye ta ƙofar Marke,

Amshi: Mainaƙiye.

 

Bayarwa: Mainaƙiye shigo ɗaka ɗari,

Amshi: Mainaƙiye.

 

Bayarwa: Ban yarda ba ban yarda ba,

Amshi: Mainaƙiye.

 

Bayarwa: Ban yarda ba da bukkag gona,

Amshi: Mainaƙiye.

 

Bayarwa: Ban yarda ba a sangarta ni,

Amshi: Mainaƙiye.

 

Bayarwa: Ban yarda ba a sangarta ni,

Amshi: Mainaƙiye.

 

Bayarwa: Ban yarda ba a kai ni a baro,

Amshi: Mainaƙiye. (Gobir da Sani, 2021 sh. 18)

4.0 Sakamakon Bincike

Yayin wannan bincike, an fahimci cewa kishi wani abu ne da ya zama ruwan dare, wanda ya game kowace halittar Ubangiji, ba wai ya ta’allaƙa ga ɗan’adam ne kawai ba. Ana samun sa a tsakanin aljannu, kamar yadda yake a cikin mutane. Haka kuma, an samu nason kishi a tsakanin Mala’iku, kamar yadda nassin Alƙur’ani mai tsarki ya nuna.

Wani abin sha’awa kuma shi ne, a ƙasar Hausa duk mutumin da ba ya nuna kishin iyalinsa akan ɗauke shi bai san ciwon kansa ba. Haka alamarin yake ga mata. Idan mace ba ta kishin kanta da na mijinta akan ɗauke ta tamkar ballagaza. Wannan nazari ya gano cewa, kishi wata ɗabi’a ce da manya suke koyar da yara (musamman mata) a matakai daban-daban. Akan fara koyar da su tun daga lokacin reno da na gaɗa da kuma a wasu bukukuwa da taruka kamar na daɓe da sauransu.

Ƙin ƙarawa kuma, an fahimci cewa nason kishi ya ratsa adabin Hausa. Kai tsaye an samu misalansa a cikin waƙoƙin baka na musamman. Hoton kishi da yake bayyana a cikin ire-iren waɗannan waƙoƙi yana nuni ga yadda Hausawa suka ɗauki lamarin kishi. Haka kuma, a ciki ana iya ganin kwatankwacin mizaninsa a cikin zuciyarsu.

4.1 Kammalawa

Tabbas waƙoƙin baka na musamman wani fage ne daga cikin adabin baka na Hausawa mai nuna hoton rayuwarsu. Yakan yi nuni da hotuna har na abubuwan da ba a gani, misali kishi. Kamar yadda takardar ta kawo, tsattsafin kishi ya bayyana a cikin waƙoƙi daban-daban. Wannan yana nuna cewa, waƙoƙin baka na musamman muhimmin fage ne da za a iya nazartar sa idan ana son fahimtar yanayi da mizanin kishin Hausawa, musamman mata.

Kamar yadda aka gani, an gabatar da wannan nazari ne domin fito da yanayin yadda kishi ya yi naso a cikin adabin Bahaushe (waƙoƙi na musamman). An yi haka ne domin fayyace yadda kishi yake a rayuwar al’umma. Haka ya sa aka yi garkuwa da adabin baka domin a gano haƙiƙaninsa. Ta haka ne ake fatar cewa wannan bincike zai taimaka wajen gane kishi da irin tasirin da ya yi ga rayuwar jama’a. Domin kuwa idan an fahimce shi za a iya samar da zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin al’umma. Daga ƙarshe ana bai wa jami’o’i da hukumomin adana tarihi da al’adu da manyan makarantu da shugabanin al’umma da masana da su bayar da cikakken tallafin da ya kamata don ganin an zurfafa bincike wajen gano ɓirɓishin kishi a sauran ɓangarorin adabi. Haka shi zai ba da dama a fahimci yadda yake a sauran al’ummomi da suke a kowane ɓangare na wannan nahiya tamu. Sakamakon kuwa zai taimaka wajen haskaka hanyoyin inganta zaman lafiya.

Manazarta

Ahmad, U. B. (2002). Jiya A Yau: Daɗaɗɗun Waƙoƙin Hausa. Ahamdu Bello University Press.

Bakura, A.R. (2003). Gurbin Kishi a Adabin Hausa: Tsokaci a Zube na Baka da Waƙa. [Kundin digiri na biyu da ba a buga ba]. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Tsangayar Fasaha da Nazarin Addinin Musulunci, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.

Bala, M. da Wasu (1993). Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai da Waƙoƙinsa. [Kundin Digiri na Farko da ba a buga ba]. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.

Bargery, G.P. (1934). A Hausa-English Dictionary and English-Hausa Vocabulary. Bugu na Biyu. Ahmadu Bello University Press Limited.

Garba, C.Y. (1990). Ƙamus na Harshen Hausa. Evans Brothers.

Gobir, Y.A. & Sani, A-U. (2021). Waƙoƙin Hausa Na Gargajiya. Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. https://www.amsoshi.com/2026/05/wakokin-hausa-na-gargajiya.html

Guau, S.M. (Bb). Wasanni da Waƙe-Waƙen Yara a Ƙasar Gusau. Kungiyar Hausa, Jami’ar Bayero, Kano.

Gusau, S.M. (1984). Nazarin Zaɓaɓɓun Waƙoƙin Makaɗan Baka Na Hausa ittafi na Ɗaya. Sashen Koyar da Harshen Hausa, Babbar Kwalejin Tarbiyyar Malamai, Jihar Sakkwato.

Kano, C.N.H.B.U. (1993). Nazari a Kan Harshe da Adabi da Al’adu na Hausa, Littafi na Uku. Gaskiya Corporation Limited.

Muhammad, S. da Yahaya, I.Y. (Bb). Darussa a Kan Adabin Hausa. Institute of Education Ahmadu Bello University.

Sani, A-U. & Gobir, Y.A. (2021). Wasanni a Ƙasar Hausa. Amal Printing & Publishing Nigerian LTD. https://www.amsoshi.com/2026/05/wasanni-kasar-hausa.html

Sani, A-U. (2025). Raujin hikima: Gurbin waƙoƙin gargajiya a rayuwar Hausawa. Njinga & Sepé: Revista Internacional de Culturas, Línguas Africanas e Brasileiras. São Francisco do Conde (BA), UNILAB, Brazil, 5 (Especial I), 11-23. https://revistas.unilab.edu.br/index.php/njingaesape/article/view/2340

Umar, M.B. (1987). Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Gargajiya. Triumph, Gidan Sa’adu Zungur.

Yahya, A.B. (1997). Jigon Nazarin Waƙa. Fisbas Media Services.

 

 



[1] An samo tushen kalmar daɓe ne daga “daɓaa” wadda take cikin jerin kalmomin aikatau. Takan ɗauki ɗafa-ƙeyan wasalin {-e} ko{-o} da kuma {-u}. A luggace kalmar “daɓe” wata hanya ce da ake bi ana dukan birji (tsakuwa) da aka zuba a farfajiyar ɗaki ko wani muhalli domin ya danƙare, ya yi ƙarfi sosai, kamar an yi siminti (Bargery, 1934, sh. 175).

[2] Waƙoƙin gaɗa su ne waɗanda yara ‘yan mata suke rerawa a wurin biki ko kuma dandalin wasanni. Ana haɗa waƙoƙin da tafi da kuma rawa.

[3] Waƙoƙin reno su ne waƙe-waƙen da ake yi wa jarirai a lokacin da ake yi musu tawai (wasa/reno). Waƙoƙi ne da ake yi wa jarirai domin a sa su sakewa da motsa jiki da kuma sa su yin barci (Yahaya 1997, sh. 51).

[4] I. Maidaji (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 26 ga watan 12, shekarar 2002).

[5] Mageduwa kuwa wani nau’in ciwo ne da yake cinye ‘yan yatsun ƙafa. Cutar tana faruwa ne a dalilin cizon wani ƙwaro mai jiki da zane-zane da dogon baki.

[6] Y. Mafara (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 24 ga watan Disamba, shekarar 2002)

[7] M.N. Maru (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 12 ga watan Satumba, shekarar 2002).

 

[8] K.M. Damage (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 6 ga watan 9, shekarar 2002)

[9] I. Maidaji (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 26 ga watan 12, shekarar 2002).

[10] Y. Mafara (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 24 ga watan Disamba, shekarar 2002)

[11] I. Maidaji (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 26 ga watan 12, shekarar 2002).

[12] L. Abdu (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 20 ga watan Disamba, shekarar 2002)

[13] Y. Mafara (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 24 ga watan Disamba, shekarar 2002)

[14]  R. Mafara (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 24 ga watan Disamba, shekarar 2002)

[15] Hira da ‘Yar’umma Mafara, ranar 24/12/2002.

[16] R. Amadu (keɓantacciyar tattaunawa, ranar 24 ga watan Disamba, shekarar 2002)

[17]  Hira da Faɗimatu Rabi’u, Guiwa Lowcost, Sokoto ranar 15/03/2025.

Jirwayen Kishi a Wasu Wakokin Baka Na Mata

Post a Comment

0 Comments