Ticker

6/recent/ticker-posts

Shawari Ga Ahlus Sunna Masu Tattauna Mas'alar Makomar Iyayen Annabi (SAW)

Ya kamata Ahlus Sunna masu tattaunawa a kan wannar mas'ala, ta makomar iyayen Annabi (saw), su lura da abubuwa kamar haka:

1- Wannar mas'ala, mas'ala ce ta tausayawa, ba ta farin ciki da nishaɗi da jin daɗi da murna ba. Saboda bayan Allah ya hana Annabi (SAW) iznin nema wa mahaifiyarsa gafara, Annabi (SAW) kuka ya yi, har sai da ya saka Sahabbansa kuka, saboda tausaya wa mahaifiyarsa.

«بكى، وأبكى من حوله»

Saboda haka mu ma ya kamata mu taya Annabi (SAW) tausaya wa mahaifansa, ba mu ɗauki mas'alar a matsayin abin nishaɗi da farin ciki, ko gadara ba.

2- Ita wannar mas'ala, mas'ala ce ta labarin gaibi. Ahlus Sunna kuwa imani suke yi da duk wani labari da Allah da Manzonsa suka bayar, ko da ya saɓa da hankulansu da aɗifarsu, kuma ya saɓa da yadda ransu yake so.

Kuma su Ahlus Sunna ba sa kutsawa cikin mas'ala ta gaibi, saboda Allah ne kaɗai ya san haƙiƙanin gaibi. Kawai Ahlus Sunna sallamawa suke yi. Wannan ya sa:

3- Ahlus Sunna ba sa Tawili a mas'alolin labarai na gaibi. Saboda hakan kutsawa ne cikin abin da ba su da ilimi a kan haƙiƙaninsa.

Wannan ya sa kuskure ne ƙoƙarin yin Tawilin Hadisan da suka zo a wannar mas'ala, da fassara su da baffan Annabi (saw), a maimakon mahaifinsa.

4- Abin da ya kai wasu ga ƙoƙarin yin Tawilin Hadisan shi ne zaton cewa; akwai cin karo (التعارض) tsakanin Hadisan da wasu Ayoyin Alƙur'ani. Alhali akwai wani abu mai muhimmanci, wanda da yawan mutane ba sa lura da shi, shi ne; asali ba a samun cin karo tsakanin labarai guda biyu.

Ma'ana; idan Allah ya ba da labarin cewa: Ba ya azabtarwa sai bayan ya aiko Manzo, kuma ya ba da labarin bai aiko Manzo ga Larabawa kafin Annabi (saw) ba,

To ba za a samu cin karo da labarin da Annabi (saw) ya bayar na cewa; Babansa yana wuta, ya kuma nemi iznin zai nema wa mahaifiyarsa gafara, amma ba a ba shi izni ba.

To ka ga duka waɗannan labarai ne da suka zo a Nassoshin Alƙur'ani da Hadisi. Don haka Nassoshi ne na Labari (نصوص الخبر), ma'ana; ba Nassoshi ne na umurni da hani (نصوص الطلب؛ الأمر والنهي) ba.

To sai masu Tawili su ce: akwai cin karo (التعارض) a tsakanin waɗannan Nassoshi na waɗannan labaran.

Alhali duka labarai ne guda biyu; ɗaya Allah ne ya ba da labarin a cikin Alƙur'ani, ɗayan kuma Manzonsa (saw) ne ya ba da labarin a cikin ingantattun Hadisai. To a ƙa'ida; ba a samun cin karo (التعارض) tsakanin Nassoshin labarai. Don haka ba zai yiwu a ce akwai cin karo (التعارض) tsakanin waɗannan labarai da Allah da Manzonsa (saw) suka bayar ba. Don idan an ce akwai cin karo, to dole ɗaya zai zama ƙarya, ƙarya kuwa ta koru a labarin Allah da na Manzonsa (saw).

Saboda haka malamai - irin su Alƙali Abubakar al-Baƙillaniy, al-Khaɗib al-Bagdadiy, al-Gazzaliy da Ibnu Ƙudama - sun tabbatar da cewa; ba a samun cin karo (التعارض) tsakanin Nassoshin labarai, sai dai ana iya samun cin karon ne a tsakanin Nassoshin umurni da hani, amma ba na labarai ba, kamar dai yadda "al-Naskhu" (النسخ) yake shiga cikin Nassoshin umurni da hani, amma ba ya shiga cikin Nassoshin labarai. Al-Khaɗibul Bagdadiy ya ce:

"وليس في نص القرآن ولا نص الحديث عن رسول الله صلى الله عليه وسلم تعارض، قال الله تعالى: {ولو كان من عند غير الله لوجدوا فيه اختلافا كثيرا} [النساء: 82]، وقال مخبرا عن نبيه صلى الله عليه وسلم: {وما ينطق عن الهوى * إن هو إلا وحي يوحى} [النجم: 4]، فأخبر أنه لا اختلاف في شيء من القرآن، وأن كلام نبيه وحي من عنده، فدل ذلك على أن كله متفق، وأن جميعه مضاف بعضه إلى بعض، ومبني بعضه على بعض إما بعطف، أو استثناء، أو غير ذلك".

الفقيه والمتفقه للخطيب البغدادي (1/ 535)

Haka Abu Hamid al-Gazzaliy ya ce:

"معنى التعارض التناقض، فإن وقع في الخبر أوجب كون واحد منهما كذبا، ولذلك لا يجوز التعارض في الأخبار من الله تعالى، ورسوله، وإن وقع في الأمر والنهي والأحكام، فيتناقض، فيرفع الأخير الأول، ويكون نسخا، وهذا متصور".

المستصفى (ص: 279)

5- Wannan ya sa ba ya daga cikin Manhajin Ahlus Sunna rarraba tsakanin Nassoshin Shari'a zuwa: "ƙaɗ'iy da zanniy" (القطعي والظني). Su Ahlus Sunna suna karɓan Aƙida da labari daga Annabi (saw) daga dukkan Hadisin da ya inganta. Sawa'un "Mutawatiri" (المتواتر) ne, wato "ƙaɗ'iy" (القطعي), ko "Ahaad" (الآحاد), wato "zanniy" (الظني). Kuma sawa'un:

(قطعي الثبوت والدلالة، أو ظني الثبوت والدلالة، أو العكس).

Don haka, a wajen Ahlus Sunna, matuƙar dai Hadisin ya zo ta ingantacciyar hanya, hanyar maruwaita amintattu, to suna karɓarsa, su tabbatar da shi, su sallama masa, su gaskata labarin da ya ƙunsa. Ba sa gwara tsakanin Nassoshin Shari'a, alhali duka daga wuri ɗaya suka fito.

Saboda haka iƙrarin cewa; Hadisan makomar iyayen Annabi (saw) sun zo ne ta hanyar zato, kuma dalalarsu ma zato ne (ظني الثبوت والدلالة), ba "maslaki" ne na Ahlus Sunna wajen kafa hujja ba, "maslaki" ne na ƴan bidi'a:

(إنما ذلك من مسالك المبتدعة في الاستدلال).

6- Sa'annan babu cin karo tsakanin Nassoshin, saboda Ayoyin da masu Tawilin Hadisan suke kafa hujja da su gamammu ne (عامة), su kuma Hadisan keɓantattu ne (خاصة), don haka babu cin karo tsakanin Ayoyi gamammu, da Hadisai keɓantattu, kamar yadda yake a ilimin "Usulul Fiƙhi".

7- Wannan ya sa akwai mutane da dama waɗanda Annabi (saw) ya ba da labarin suna wuta, kamar Amru bn Luhayyi, wanda ya sunnanta bautar gumaka a cikin Larabawa, da Abdullahi bn Jud'an...

Kuma hatta cikin Alƙur'ani, Allah ya nuna cewa; zai azabtar da mushrikai ƴan Jahiliyya, ba don ya yi musu ni'imar Muslunci ba, inda ya ce:

{وَاعْتَصِمُوا بِحَبْلِ اللَّهِ جَمِيعًا وَلَا تَفَرَّقُوا وَاذْكُرُوا نِعْمَتَ اللَّهِ عَلَيْكُمْ إِذْ كُنْتُمْ أَعْدَاءً فَأَلَّفَ بَيْنَ قُلُوبِكُمْ فَأَصْبَحْتُمْ بِنِعْمَتِهِ إِخْوَانًا وَكُنْتُمْ عَلَى شَفَا حُفْرَةٍ مِنَ النَّارِ فَأَنْقَذَكُمْ مِنْهَا} [آل عمران: 103]

A Tafsirin Ayar sai Ibnu Jarir ya ce:

"يقول تعالى ذكره: وكنتم على طرف جهنم بكفركم الذي كنتم عليه قبل أن ينعم الله عليكم بالإسلام، فتصيروا بائتلافكم عليه إخوانا، ليس بينكم وبين الوقوع فيها إلا أن تموتوا على ذلك من كفركم، فتكونوا من الخالدين فيها، فأنقذكم الله منها بالإيمان الذي هداكم له".

تفسير الطبري ت شاكر (7/ 85)

Ka ga sai Allah ya ce: sun yi kusan faɗawa cikin wuta, sai Allah ya tsamar da su. Ka ga sai Allah ya nuna cewa; zai azabtar da su a kan kafircin da suke kai kafin aiko Annabi (saw), ba don ya yi musu ni'imar Muslunci ba.

Haka Annabi (saw) ya ba da labarin ana azabtar da wasu mutane cikin Bani Najjar, a cikin ƙabarburansu, alhali sun mutu ne a zamanin Jahiliyya, kafin zuwan Muslunci:

عن جابر بن عبد الله، يقول: "دخل النبي صلى الله عليه وسلم يوما نخلا لبني النجار، فسمع أصوات رجال من بني النجار ماتوا في الجاهلية يعذبون في قبورهم، فخرج النبي صلى الله عليه وسلم فزعا، فأمر أصحابه أن يتعوذوا من عذاب القبر".

مسند أحمد ط الرسالة (22/ 58) صحيح مسلم (4/ 2199)

Don haka duka waɗannan dalilai keɓantattu ne (نصوص خاصة), suna keɓance gamayyar waɗancan Nassoshi (عموم النصوص).

Ma'ana; dalilai keɓantattun suna nuna cewa; ko da ba a aiko musu Manzo wanda ya keɓance su ba, to lallai da'awa ta iso gare su, hujja ta tsayu a kansu, amma suka yi shirka, don haka sun cancanci azaba.

8- Kuma abin da zai nuna maka cewa; akwai waɗanda da'awa ta isa gare su, hujja ta tsayu a kansu, shi ne maganar Zaid bn Amr bn Nufail, inda yake faɗawa Ƙuraishawa, cewa; babu wanda yake kan Addinin Annabi Ibrahim (as) sai shi kaɗai:

عن أسماء بنت أبي بكر رضي الله عنهما، قالت: "رأيت زيد بن عمرو بن نفيل قائما مسندا ظهره إلى الكعبة يقول: «يا معاشر قريش، والله ما منكم على دين إبراهيم غيري»".

صحيح البخاري (5/ 41)

Haka kuma ya kasance yana inkari wa Ƙuraishawa a kan abin da suke yi na shirka, suna yanka dabbobi wa gumaka, yana aibanta su da hakan, yana tsayar musu da hujja:

عن عبد الله بن عمر رضي الله عنهما، "أن النبي صلى الله عليه وسلم لقي زيد بن عمرو بن نفيل بأسفل بلدح، قبل أن ينزل على النبي صلى الله عليه وسلم الوحي، فقدمت إلى النبي صلى الله عليه وسلم سفرة، فأبى أن يأكل منها، ثم قال زيد: إني لست آكل مما تذبحون على أنصابكم، ولا آكل إلا ما ذكر اسم الله عليه، وأن زيد بن عمرو كان يعيب على قريش ذبائحهم، ويقول: الشاة خلقها الله، وأنزل لها من السماء الماء، وأنبت لها من الأرض، ثم تذبحونها على غير اسم الله، إنكارا لذلك وإعظاما له".

صحيح البخاري (5/ 40)

Saboda haka, abu mai muhimmanci shi ne isan saƙon Manzo, idan saƙon ya isa ga mutum, kuma ya fahimce shi, to shi kenan, hujja ta tsayu a kansa. Allah ya ce:

{وَأُوحِيَ إِلَيَّ هَذَا الْقُرْآنُ لِأُنْذِرَكُمْ بِهِ وَمَنْ بَلَغَ} [الأنعام: 19]

Don haka duk wanda saƙon Allah ya isa gare shi, ta hanyar kowane Manzo, to hujja ta tsayu a kansa.

9- Wannan ya sa Malamai suke kasa "Ahlul Fatra" a dunƙule zuwa gida uku:

1) Waɗanda da'awa ta isa gare su, kuma suka yi imani, to waɗannan ƴan Aljanna ne. Kamar: Ƙiss bn Sa'idah, Warƙatu bn Naufal da Zaid bn Amr bn Nufail.

2) Waɗanda da'awa ta isa gare su, kuma hujja ta tsayu a kansu, amma sai suka canza, suka yi shirka, to waɗannan ƴan wuta ne. Kamar Amru bn Luhayyi, da Abdullahi bn Jud'an da sauransu.

3) Waɗanda da'awa ba ta isa gare su ba, ko ta isa gare su amma suna cikin gafala, hujja ba ta tsayu a kansu ba, to waɗannan su ne mafi yawan ƴan Jahiliyya, su ne waɗanda a kansu Allah ya ce:

{لِتُنْذِرَ قَوْمًا مَا أُنْذِرَ آبَاؤُهُمْ فَهُمْ غَافِلُونَ} [يس: 6]

To waɗannan Malamai sun yi saɓani a kansu, magana mafi ƙarfi ita ce: waɗannan su ne za a yi musu jarabawa a ranar Ƙiyama.

Wannan shi ne zance mafi inganci game da "Ahlul Fatra".

Saboda haka, duk waɗanda Annabi (saw) ya ba da labarin cewa; ƴan wuta ne, to da'awa ta isa gare su, ta fiskar yadda hujja ta tsayu a kansu. Kamar Amru bn Luhayyi, da Abdullahi bn Jud'an, da iyayensa (saw), da ire-irensu.

Don haka waɗanda za a musu jarabawa a Lahira, cikin "Ahlul Fatra", su ne waɗanda da'awa ba ta isa gare su ba, ko kuma da'awar ta isa gare su, amma kuma hujja ba ta tsayu a kansu ba, saboda suna cikin gafala. Shi ya sa Ibnul Ƙayyim ya yi bayanin kafircin da yake sa a azabtar da mutum, da kuma wanda ba ya sakawa, inda ya ce:

"إن العذاب يستحق بسببين:

أحدهما: الإعراض عن الحجة، وعدم إرادة العلم بها وبموجبها.

الثانى: العناد لها بعد قيامها، وترك إرادة موجبها.

فالأول كفر إعراض.

والثانى كفر عناد.

وأما كفر الجهل مع عدم قيام الحجة، وعدم التمكن من معرفتها، فهذا الذى نفى الله التعذيب عنه حتى تقوم حجة الرسل".

طريق الهجرتين (ص: 414)

Saboda haka, kafirci na kau-da-kai bayan bayyanar hujja, da kafirci na tauri kai, su suke sa mutum ya shiga wuta.

Amma kafirci na jahilci, wanda mai shi bai ma san me ake ciki ba, to shi ne wanda ba za a azabtar da shi ba, sai bayan an tsayar masa da hujja, ta hanyar Manzanni.

Kuma ita tsayuwar hujja a kan mutum, Allah ne ya san wanda da'awa ta isa gare shi, har hujja ta tsayu a kansa. Ibnul Ƙayyim ya ce:

"والله يقضى بين عباده يوم القيامة بحكمه وعدله، ولا يعذب إلا من قامت عليه حجته بالرسل، فهذا مقطوع به فى جملة الخلق. وأما كون زيد بعينه وعمرو بعينه قامت عليه الحجة أم لا، فذلك مما لا يمكن الدخول بين الله وبين عباده فيه، بل الواجب على العبد أن يعتقد أن كل من دان بدين غير دين الإسلام فهو كافر، وأن الله سبحانه وتعالى لا يعذب أحدا إلا بعد قيام الحجة عليه بالرسول. هذا فى الجملة، والتعيين موكول إلى علم الله عز وجل وحكمه".

طريق الهجرتين وباب السعادتين (ص: 413)

Bayan haka, mutane sun banbanta wajen tsayuwar hujja a kansu, suna banbanta gwargwadon wuri zuwa, da zamani zuwa zamani, da mutum zuwa mutum. Ma'ana; za a iya samun ƴan zamani kaza hujja ta tsayu a kansu, amma ƴan zamanin bayansu ba ta tsayu a kansu ba.

Ko a zamani ɗaya, amma ƴan gari kaza hujja ta tsayu a kansu, amma ƴan wani garin ba ta tsayu a kansu ba.

Haka tsakanin mutane, za a samu wani hujjar ta tsayu a kansa, amma wani mutumin kuma, ko wasu mutanen, hujjar ba ta tsayu a kansu ba. Saboda abun ya danganta, ta yadda saƙon Manzon Allah ya isa gare shi. Shi ya sa Ibnul Ƙayyim ya ce:

"إن قيام الحجة يختلف باختلاف الأزمنة والأمكنة والأشخاص، فقد تقوم حجة الله على الكفار فى زمان دون زمان، وفى بقعة وناحية دون أخرى، كما أنها تقوم على شخص دون آخر".

طريق الهجرتين وباب السعادتين (ص: 413)

Saboda haka lamarin tsayuwar hujja a kan mutane wani fage ne na ilimin gaibi mai faɗi, wanda ya wuce ilimin halitta, sai dai Allah mahalicci masanin gaibi, kuma masanin halin bayinsa.

Idan kuma an ce; lallai duka "Ahlul Fatra" ne za a yi musu jarabawan, to ai Allah ya san waɗanda za su ci jarabawan, ya kuma san waɗanda za su faɗi, waɗanda su ne za su shiga wuta. To daga cikinsu ne Allah ya sanar da Annabi (saw) waɗanda ya ga daman ya sanar da shi, kamar yadda Ibnu Kasir ya ce:

"وإخباره صلى الله عليه وسلم عن أبويه وجده عبد المطلب بأنهم من أهل النار، لا ينافي الحديث الوارد عنه من طرق متعددة؛ أن أهل الفترة والأطفال والمجانين والصم يمتحنون في العرصات يوم القيامة...

فيكون هؤلاء من جملة من لا يجيب، فلا منافاة ولله الحمد والمنة".

البداية والنهاية (٣/ ٤٢٩)

A wani wajen ya ce:

"وامتحانهم لا يقتضي نجاتهم، ولا ينافي الإخبار عنهم بأنهم من أهل النار؛ لأن الله يطلع رسوله صلى الله عليه وسلم على ما يشاء من أمر الغيب".

البداية والنهاية (٢/ ٥٥٥)

Shaikh Shanƙiɗiy ya ce:

"وبهذا الجمع تتفق الأدلة، فيكون أهل الفترة معذورين، وقوم منهم من أهل النار بعد الامتحان، وقوم منهم من أهل الجنة بعده أيضا، ويحمل كل واحد من القولين على بعض منهم علم الله مصيرهم، وأعلم به نبيه صلى الله عليه وسلم، فيزول التعارض".

دفع إيهام الاضطراب عن آيات الكتاب (ص: 141)

To ka ga waɗannan Malamai biyu, sun tabbatar da cewa; waɗanda Annabi (saw) ya ba da labarin suna wuta, suna cikin waɗanda ba za su ci jarabawan da za a musu a ranar Lahira ba. Da ma tun fil-azal Allah ya sansu, sai ya sanar da Annabinsa (saw) su.

10- Tawilin da wasu suke yi, suke cewa; ai baffansa ake nufi, ba mahaifinsa ba, to ya kamata su sani; shi Tawili - a wajen masu shi - ba haka kawai ake yinsa ba, a'a, dole sai da ƙarina.

Saboda haka babu wata ƙarina a cikin Hadisan da za ta sa a yi Tawilinsu, daga mahaifi zuwa baffa.

11- Sukan ce: ai hatta a cikin Alƙur'ani lafazin baba "أب", ya zo da ma'anar baffa da kaka. Alhali sun manta da cewa: duk inda ya zo da hakan to an samu ƙarina, ƙarinar ita ce: an anbaci sunan baffan ko kakan ƙarara a fili, an anbace su da sunayensu. Don haka a fili an san ba mahaifi kaɗai ake nufi ba, har da kaka da baffa.

12- Kuma wata ƙa'ida mai muhimmanci da ya kamata su sani, shi Tawili ana yinsa ne a lafazi "zahiri" (الظاهر), wato lafazin da yake da ma'anoni fiye da ɗaya, amma kuma ma'ana guda ɗaya ta fi rinjaye a kan sauran ma'anonin. To asali irin wannan lafazi, wajibi ne a bar shi a kan ma'anarsa ta "zahiri", ba za a kawar da ita, a yi tawilin lafazin ba sai da ƙarina mai ƙarfi.

To idan mun duba lafazin "baba" (أب), za mu ga cewa; lafazi ne "zahiri", saboda yana da ma'ana mai rinjaye, ita ce: "mahaifi". Shi ya sa da zaran wani ya ce maka: "Yau na ga babanka", to mahaifinka ne zai fara zuwa a tunaninka, sai dai idan ya mutu ne, ko wata ƙarinar daban, wacce za ta sa ka yi tunanin baffanka ko wani daban.

Amma da cewa ya yi: na ga babanka Isiyaku, alhali Isiyakun baffanka ne, ba mahaifinka ba, to babu wata jayayya, an san "baba" a nan baffanka Isyaku ake nufi, saboda an kira sunansa ƙarara. To kamar haka ne duka Ayoyin da suka zo a cikin Alƙur'ani. Kamar faɗin Allah:

{أَمْ كُنْتُمْ شُهَدَاءَ إِذْ حَضَرَ يَعْقُوبَ الْمَوْتُ إِذْ قَالَ لِبَنِيهِ مَا تَعْبُدُونَ مِنْ بَعْدِي قَالُوا نَعْبُدُ إِلَهَكَ وَإِلَهَ آبَائِكَ إِبْرَاهِيمَ وَإِسْمَاعِيلَ وَإِسْحَاقَ إِلَهًا وَاحِدًا وَنَحْنُ لَهُ مُسْلِمُونَ} [البقرة: 133].

Da faɗinsa:

{وَاتَّبَعْتُ مِلَّةَ آبَائِي إِبْرَاهِيمَ وَإِسْحَاقَ وَيَعْقُوبَ} [يوسف: 38]

Amma a Hadisin baban Annabi (saw), babu wata ƙarina da za ta sa a fahimci baffansa ake nufi, ko kakansa, don haka dole sai dai a bar Hadisin a zahirinsa.

To idan an ce: "baba", ma'ana mai rinjaye ta lafazin shi ne "mahaifi". Shi ya sa da zaran an faɗi lafazin, kai tsaye mahaifi ake nufi.

13- Sa'annan kuma idan sun yi Tawilin Hadisin baban Annabi (saw) da baffa, to wane Tawilin suka yi wa Hadisin mamarsa kuma?!

14- Haka kuma, idan sun yi Tawilin Hadisin baban Annabi (saw), to wane Tawilin suka yi wa sauran waɗanda Annabi (saw) ya ce: ƴan wuta ne, alhali su ma "Ahlul Fatra" ne, kamar baban shi wanda ya tambayi Annabi (saw) ya ce: ina babana? Sai Annabi (saw) ya ce: "Yana wuta".... Da sauran waɗanda Annabi (saw) ya ce suna wuta, irin su Amru bn Luhayyi, Abdullahi bn Jud'an, da sauransu?!

15- Saboda haka, sam babin labarai da Allah da Manzonsa suka bayar, da sauran lamura na gaibi, na labarin makomar wasu a Lahira da sauransu, ba a kutsawa cikinsa da hankali ko aɗifa ko shubuhohi. Kawai sallamawa ake yi, a miƙa lamarin ga Allah, a ce:

"سمعنا وصدقنا وآمنا".

Shi ya sa irin waɗannan Hadisai na labarin makomar iyayen Annabi (saw) da sauransu, duka daidai suke da Hadisan siffofin Allah, waɗanda Salaf suke cewa:

"أمروها كما جاءت".

Ma'ana; ku bar su a yadda suke, a yadda suka zo, kada ku yi shisshigi, ku kutsa cikinsu.

16- Idan an lura, duka waɗannan bayanai an fiskantar da su ne ga Ahlus Sunna, waɗanda sun yarda da Hadisan. Don haka ba ana magana ne da ƴan bidi'a, ko sauran masu ƙaryata Hadisan ba.

17- Saboda haka, ya ku Ahlus Sunna ku sauƙaƙa wa junanku wajen tattauna mas'alar, mas'ala ce wacce bai kamata a zafafa a kanta ba, idan za a kalle ta a ilmance. Duk wanda yake ganin zai yi Tawilin Hadisin, to a bar shi, to amma bai halasta yana amfani da kibiyoyin ƴan bidi'a yana harba su kan Ahlus Sunna masu tabbatar da Hadisan a zahirinsu ba, kamar jifansu da cewa; ba sa son Annabi (saw), ko cewa; suna cutar da Annabi (saw). Gaskiya wannan zalunci ne, da ketare iyaka. Saboda duk wanda ka yi masa hukunci ba ya son Annabi (saw), to fa kai tsaye ka kafirta shi.

Idan kuma ka ce: yana cutar da Annabi (saw), to ka jefa shi cikin munafukai, waɗanda su aka sani da cutar da Annabi (saw), alhali duka waɗannan ja'iran hukunce - hukunce ne.

18- Kuma ya kai mai Tawilin Hadisin, kada ka manta cewa; shi mai tabbatar da Hadisin ba daga aljihunsa ya fitar da abin da yake faɗan ba, a'a, aiki ya yi da Hadisai ingantattu. Kuma ba a samu inkarin zahirin Hadisan ba sai a ƙarnonin baya, amma a ƙarnonin farkon al'umma, duk waɗanda suka yi magana a kan Hadisan, ko suka ruwaito su a littatafansu, tabbatar da su a kan mahaifan Annabi (saw) suke yi, ba sa Tawili.

Don haka, shin zai yiwu a ce duka manyan Malaman Addini da suka tabbatar da Hadisan a kan mahaifan Annabi (saw), su ma maƙiya Annabi (saw) ne, ko masu cutar da shi (saw)?!

19- Sai kuma ku masu tabbatar da Hadisan a kan mahaifan Annabi (saw), ya kamata ku san wani abu guda mai muhimmanci; wannar mas'ala, mas'ala ce mai sosa rai. Mas'ala wacce hatta Annabi (saw) sai da ya yi kuka a kanta, Sahabbansa suka yi kuka, a lokacin da Allah ya hana shi nema wa mahaifiyarsa gafara. Saboda haka don Allah a dena tayar da mas'alar idan ba da buƙata ba. Kuma idan ma buƙata ta sa an tayar da ita, to don Allah mu zama cikin masu taya Manzon Allah (saw) tausaya wa mahaifan nasa, don shi har kuka ya yi, ya saka Sahabbansa kuka.

20- Sa'annan kuma sau da yawa za ka ji masu Tawilin Hadisan suna cewa; bayyana Hadisan makomar iyayen Annabin (saw) ba shi da wani amfani.

To a gaskiya wannar magana kuskure ce. Saboda abubuwa kamar haka:

(A) Da a ce ba shi da amfani, shin Annabin (saw) zai faɗa?!

Kana nufin Annabi (saw) zai faɗi abin da ba shi da amfani kenan?!

(B) Kuma ai wajibi ne mu gaskata dukkan labarin da Annabi (saw) ya bayar, mu yi imani da shi.

(C) Kuma hukunce - hukuncen Allah kashi uku ne:

(1) Hukunci na Shari'a.

(2) Hukunci na Ƙaddara.

(3) Hukunci na "Jaza'i", wato hukunci na sakamako.

To mas'alar makoma a Lahira, tana cikin nau'i na uku ne, wato Hukunci na "Jaza'i". Don haka kamar yadda wajibi ne ka yi imani, ka gaskata hukuncin Shari'a da na Ƙaddara, to haka wajibi ne ka yi imani, ka gaskata duk wani hukuncin Allah na jaza'i, da sakamako da zai yi wa bayinsa, musamman waɗanda Allah ya ba da labari a cikin Alƙur'ani, kamar makomar Fir'auna, ko Annabi (saw) ya ba da labari, kamar makomar iyayensa, da sauran waɗanda ya ba da labarin suna wuta, alhali sun mutu kafin aiko Annabi (saw).

21- Kuma ya wajaba masu Tawilin Hadisan su zama masu adalci, su dena zargin masu tabbatar da zahirin Hadisan da cewa; suna tayar da fitina, suna yawaita magana a kan mas'alar. Tsakani da Allah kowa ya san cewa; ƴan bidi'a ne suke tayar mas'alar, don su rinƙa tunzura gama-garin mutane, don su ƙyamaci Ahlus Sunna/ƴan Izala. Har ya kai ga taruka da maulidi suke shiryawa, na iyayen Annabi (saw). Bai daɗe ba, kwanan nan na ga sun yi taro a kan iyayen Annabi (saw). To a ƙa'ida; duk lokacin da aka bayyana ɓarna da bidi'a, to ya wajaba a yi inkarinta, a yi bayanin abin da ya tabbata a Sunna da Hadisai.

22- Daga ƙarshe, wannar mas'ala ce mai sauƙi idan za a kalle ta da madubi na ilmi, mai girma ce idan da zallar aɗifa za a kalle ta, kuma za ta iya janyo fitina.

Ilimi kuwa shi ne gaba da aɗifa. Don haka wanda ya tabbatar da Hadisan a kan mahaifan Annabi (saw), bisa imani da Hadisan Annabi (saw) ya yi dadai.

Haka shi ma wanda ya yi Tawili, saboda ya kasa fahimtar Hadisan a zahirinsu, don ganin Ayoyi da suke nuna cewa; ba a aiko musu manzo ba, shi ma yana da uzuri.

Amma duk wanda zai yi raddi ga ɗaya ɓangare, bisa mummunar manufa, ko a haɗe da jahilci da zalunci, to ya sani zai haɗu da Allah, kuma zai girbi mummunan aikin da ya shuka

23- Don haka ina ƙara maimaitawa, su masu tabbatar da Hadisan a kan mahaifan Annabi (saw), Sunna ita ce; muna taya Annabi (saw) tausaya musu, saboda shi har kuka ya yi, haka Sahabban da suke tare da shi su ma sun yi kuka.

Allah ka shiryar da mu hanya madaidaiciya.

✍️ Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)

  25 August, 2026

Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

Post a Comment

0 Comments