A wannar kasa da muke rayuwa a cikinta, a wannan lokaci da muke ciki, musamman a wannan hali na kuncin rayuwa da muke ciki, mutane suna cikin rudu da damuwa, kowa yana neman mafita, da yanayi da zai samu saukin kuncin tsadar rayuwa.
Kowa cikin mutane yana ta
fadi-tashi na neman jin dadin rayuwa; a ce ya fi karfin abincinsa shi da
iyalansa, ya fi karfin kiwon lafiyarsa da ta iyalansa, ya fi karfin dawainiyar
ilimi da karatunsa da na iyalansa, ya mallaki gida da abin hawa na alfarma, dukkan
wata bukata a rayuwa yana iya biyanta, bayan ya samu iyali irin kalar da ya fi
so, har yana samun daman tafiye-tafiye na shakatawa.
Mafi yawan mutane sun dauka
wannan kadai shi ne sa'ada da jin dadin rayuwa. Shi ya sa kowa ya gigice ya
bazama wajen neman tara dukiya, yana ganin a nan sa'ada da jin dadin rayuwa
take. Wasu kuma neman mulki da shugabanci ido rufe, wasu kuma neman shahara da
neman suna da girma da daukaka a wajen mutane, da sauran hanyoyi da mutane suke
zaton a nan za su samu sa'ada da jin dadin rayuwa.
To idan muka lura da kyau za
mu ga masu wannan sun takaita jin dadin rayuwa ne a kan gangar jiki kadai, shi
ya sa duka tunaninsu ya kare a kan hanyoyin jin dadin rayuwa na zahiri.
Alhali mutum nawa suka samu
kudi, ko shahara ko mulki, ko mata, amma kullum a cikin bakin ciki da damuwa
suke?
Mutum nawa ne suka samu irin
wadannan abubuwa, amma suna kashe kawunansu, saboda damuwa?
Mutum nawa suke da wadannan
abubuwa, amma sun afka cikin shaye-shaye da ta'amuli da miyagun kwayoyi, don
neman kwanciyar hankali?
Mutane nawa suna da kayan
jin dadin rayuwa na zahiri amma kuma sun afka aikata miyagun laifuka na
ta'addanci da zubar da jini?
Ashe kenan hakikanin jin
dadin rayuwa, da samun sa'ada da kwanciyar hankali da samun rayuwa mai dadi
tana bayan wadannan abubuwa gaba daya.
Duk wanda yake son rayuwa ta
hakika to ya amsa ma Allah da Manzonsa ga kiran da suka yi masa. Allah ya ce:
{استجيبوا
لله وللرسول إذا دعاكم لما يحييكم} [الأنفال: ٢٤].
Duk wanda yake son rayuwa
mai dadi to ya yi imani da Allah ya yi kyakkyawan aiki. Allah ya ce:
{من
عمل صالحا من ذكر أو أنثى وهو مؤمن فلنحيينه حياة طيبة} [النحل: ٩٧].
Duk wanda yake son nitsuwa a
zuciyarsa to ya rike zikiri da ambaton Allah. Allah ya ce:
{ألا
بذكر الله تطمئن القلوب} [الرعد: ٢٨].
Rashin zikiri da ambaton
Allah shi yake janyo kuncin rayuwa. Allah ya ce:
{ومن
أعرض عن ذكري فإن له معيشة ضنكا} [طه: ١٢٤].
Hakikanin rayuwa, da rayuwa
mai dadi tana cikin rayuwar ruhi, wacce ake raya ta da imani da jin tsoron
Allah. Lallai duk wanda ya riki wannar hanya ba zai taba shiga cikin kuncin
rayuwa ba, ko da ba shi da sisin kwabo a rayuwarsa. Kuma wannar hanya ita ce
hanya ta hakika ta samun arziki da fita daga mawuyacin halin rayuwa, na talauci
da fatara da yunwa da tsadar rayuwa. Allah ya ce:
{ولو
أن أهل القرى آمنوا واتقوا لفتحنا عليهم بركات من السماء والأرض} [الأعراف: ٩٦]
Saboda haka bin hanyoyi na
Shari'a, sannan sai aiki da sabuba na halal na samun arziki su suke samar da
kwanciyar hankali da sa'ada da jin dadin rayuwa.
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
10 August, 2023
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.