Ticker

6/recent/ticker-posts

Sarkin Gummi Na Sha Biyar: Sarkin Mafaran Gummi Justice Lawal Hassan

Jagora: Mai daraja ɗan Marahwa jikan Andi riƙa ƙwarai

Y/Amshi: Taka lahiya dai uban Bango,

Bida arna,

Mai martaba kak ka ɗau wargi,

Emiyan Gummi Lawal zarumin Sarki

Jagora: Kun gadi hanƙuri

Y/Amshi: Kuma kun gadi taimako,

Mulkin duniya naku na Sarki,

Riƙa da ƙarhin Allah na mai hwada sai madi

Jagora: Sarki ga farin jini

Ga kyauta ga fara'a

Wajjan fasinaliti jikan Ali ba ayi kamatai ba

Y/Amshi: Kama da ɗan Aisha na nada Daudu yad dawo

Jagora: Yaushe rabo na da ganin daba?

Y/Amshi: Tun lokacin su Sarki Andi,

Na ɗan Aisha tun tun tun,

A lokacin Mamman ga dawaki...

Jagora: Naga dawaki iri-iri

Y/Amshi: Akwai wani wanda ban saba kallo ba,

Bida arna,

Mai martaba kak ka ɗau wargi,

Emiyan Gummi Lawal Hassan zarumin Sarki

Jagora: Kowas san Sarki Andi,

Da ganin Sarki Lawal

Igizatili mutun ko bai  tambaya ba,

Jagora /Y/amshi: Yasan zuriyash shi ce babu tsentseni,

Bida arna,

Mai martaba kak ka ɗau wargi,

Emiyan Gummi Lawal Hassan zarumin Sarki

Jagora: Sarkin Tabshi ina godiya gun Wahidun Rahimin Sarki

Y/Amshi: Yanzu hwaɗin Nijeriyag ga,

Kowane taro akai,

Da dud Gummi ta sabka ban zullumin komi

Jagora: Wajen fasaha

Y/Amshi: Ba akai irin namu Sarki ba,

Jagora: Wajen fahimta

Y/Amshi: Ba akai irin namu Sarki ba,

Jagora:

In an ka shiga ga mulki

Y/Amshi :

Ba akai irin namu Sarki ba,

Jagora :

In an kazo ga ilmi

Y/Amshi :

Ba a kai irin namu Sarki ba,

Jagora :

Haka nan wurin muruwa

Y/Amshi :

Ba a kai irin namu Sarki ba,

Jagora:

Sannan wurin bajinta

Y/Amshi :

Ba akai irin namu Sarki ba,

Da ace kazo lokacin ana yaƙi,

Da kana kama Jangwarzo,

Gobirawa kuyi hattara banda ganganci,

Ku zo ku kai caffa,

Maigidan naku ne yazzo,

Jagora :

Ɗauko Ɗan guma jini

Y/Amshi :

Ka ɗauko takobin Waru,

Ƙasag Gobir dum muna son tazan hannu,

Bida arna,

Mai martaba kak ka ɗau wargi,

Emiyan Gummi Lawal Hassan zarumin Sarki.

Ɗiyan waƙa ne ☝️☝️☝️☝️☝️☝️☝️daga cikin wata waƙa da Sarkin Taushin Gummi, Alh. Sani Ɗan Aino Gyalange ya rerawa mai martaba Sarkin  Gummi na 15, wato Sarkin Mafaran Gummi Justice Lawal Hassan mai amshi "Bida arna, mai martaba kak ka ɗau wargi, emiyan Gummi Lawal Hassan zarumin Sarki".

Sharhin namu na yau zai ƙumshi abubuwa masu dama gwargwadon hali.

Sarkin Taushi Alh. Sani Ɗan Aino ɗa ne ga Makaɗa Muhammadu Ɗan Aino Gyalange wani mashahurin Makaɗin noma da aka yi a garin Gyalange hedikwatar gundumar Gyalange a masarautar Gummi, Jihar Zamfara. Ya yi kiɗa ne da ganga ta ratayawa da ɗansa Alh. Sani ya gaje/gade shi bayan rasuwarsa sai ya sauya salon sabgar ta hanyar amfani da Taushi a maimakon ganga kuma ya shiga fagen kiɗan sarakuna da na jama'a.

Ya yi karatun addini da na zamani domin har takardar shaidar malanta ta ƙasa (NCE) ya samu ya kuma yi aikin koyarwa a matakin makarantar furamare. Shi ne ma dalilin da yasa ake tsintar wasu kalmomi na turanci a cikin waƙoƙinsa, misali a wannan waƙa ya yi amfani da kalmomi biyu na turanci "fasinaliti/personality da igizatili/exactly.

Ya yi zamani da Sarakunan Gummi guda 3, Sarkin Mafaran Gummi Alh. Aliyu Isah da Sarkin Mafaran Gummi Alhaji Aliyu Adamu Abara da kuma Sarki  dake akan karagar mulki a halin yanzu, kenan Sarki na 13 dana 14 da kuma na 15. Ya rasu kusan watanni 6 da suka wuce yana da kimanin shekaru 61 a duniya. Allah ya kyauta makwanci, amin.

A cikin waɗannan ɗiyan waƙa Sarkin Taushi Sani Ɗan Aino Gyalange ya zayyana wasu daga cikin halayen mai martaba Sarki Justice Lawal Hassan da kuma irin yadda kasancewarsa Sarki ya sanya masarautar Gummi ta ƙara samun daraja da ɗaukaka a idon duniya.

A ciki dai ya fito da salsalar mai martaba Sarki "Kowas san Sarki Andi, da ganin Sarki Lawal igizatili mutun ko bai tambaya ba, yasan zuriyash shi ce babu tsentseni".

Wane ne Andi da Sarkin Taushi Sani Ɗan Aino Gyalange ya kwatanta da mai martaba Sarki?

Muhammadu Andi shi ne Sarki na 10 a masarautar Gummi yayi sarauta daga shekarar 1910-1933, shi kuma ɗan Sarkin Marafan Gummi na 7 ne, wato Sarki Abdullahi Laje da yayi mulki daga shekarar 1867-1892, shi kuma ɗan Sarkin Mafaran Gummi na 5 ne, wato Sarki Ɗan A'isha wanda  ya yi sarauta daga shekarar 1847-1864, shi kuma ɗan Sarkin Mafaran Gummi na farko ne, wato Sarki Muhammadu Waru wanda ya yi sarauta daga shekarar 1782 zuwa 1807, shi kuma ɗan Sarki Ali Bazamfare ne wanda ya samar da masarautar Bukkuyum ta Jihar Zamfara.

Sarki Muhammadu Andi ne ya haifi Malam Hassan, Malam Hassan ɗan Muhammadu Andi ɗan Abdullahi Laje ɗan Umaru Ɗ/Aisha ɗan Muhammadu Waru ɗan Ali Bazamfare shi ne mahaifin mai martaba Sarki Justice Lawal Hassan na yanzu da ya zama Sarki a shekarar 2013.

Gummi Gumama ta Ali mai kamar yau sallah, dogon birnin garin mai saje ". Wani Mafarauci ne da ake kira Muhammadu Bangu sanadiyar samar da wannan suna " Gummi" saboda wata kibiyarsa da yake yiwa kirari "Guma jini ba amon dahi" ko kuma batun da yake yi idan ya yi amfani da ita ya kashe wata dabba ta daji ya kance "na guma mata/na guma mashi kibiya" sannu a hankali sai wannan wuri da yake zaune ya ɗauki suna "Gumi ko Gummi".

Sarkin Gummi na farko wato Muhammadu Waru ɗa ne ga Ali Bazamfare da ya fito daga cikin Zamfarawan Mafara/Talata Mafara tun suna zaune a Tumfafiya /Tumfafi a matsayin hedikwatarsu wato kafin su koma Mafara/Talata Mafara a lokacin mulki Sarki Ɗangarji.

Ali Bazamfare ya nusa kudu maso yammacin Tumfafiya har zuwa Fakai  da Danko a masarautar Zurun Jihar Kebbi ta yau.  Ya haifi 'ya'ya 3 maza, Kure wanda ya baro a Danko a matsayin Sarki da Ɗanƙofa da kuma Muhammadu Waru.

Muhammadu Waru ya ɗebi jama'a zuwa wani wuri da ake kira Kagarar Fulani dake kusa da tungar da Mafarauci Muhammadu Bangu ya zauna da sannu a hankali ta amsa sunan "Gummi" a shekarar 1782 ya samar da tsarin mulki irin na sarauta da laƙabin "Sarkin Mafara" domin tawilin asalin inda mahaifinsa ya fito wato Mafara/Talata Mafara.

Ya yi mulki har zuwa wafatinsa a shekarar 1807 saboda haka ma ne suka yi mu'amala ta ƙud da ƙud da masu jihadin jaddada addinin musulunci na Daular Usmaniyya da Mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo Tagammadahullah Birahamatihi ya jagoranta a lokacin.

A cikin waƙar Sarkin Taushi Sani Ɗan Aino Gyalange ya dawo da wani tarihi domin tunatar da mai martaba Sarki (duk da zuriyar Dakka ne abun ya faru dasu ba zuriyar Buda Jan Masari inda Ali Bazamfare mahaifin Muhammadu Waru kakan Sarki bane , amma dai  dukan su jinsin Zamfarawa ne) cewa akwai buƙatar ya ci ƙasar Gobir /Gobirawa da yaƙi har ma yana nuna masa cewa "Da ace kazo lokacin ana yaƙi, da kana kama Jangwarzo, Gobirawa kuyi hattara, kuzo ku kai caffa maigidan naku na yazzo".

Wannan wani abu ne da ya faru a shiyoyin 1760s zuwa 1770s lokacin da Sarkin Gobir Ibrahim Babari mahaifin Sarkin Gobir Malam Umaru Bawa Jangwarzo ya mamaye Zamfarawa har ma ya ƙwace masu hedikwata da ake kira Birnin Zamfara a lokacin mulkin Sarkin Zamfara Maroƙi ɗan Sarki Malo (Kangon Birnin Zamfara a halin yanzu yana  kusa da garin Isa, Ƙaramar Hukumar Mulkin Isa ta Jihar Sakkwato ta yau).

Lallai Sarkin Taushi Sani Ɗan Aino Gyalange ya haikato muna lamurra masu yawa da muhimmanci a cikin wannan waƙa.

A wannan hoto mai martaba Sarkin Mafaran Gummi na 15 ne mai mulkin Masarautar Gummi mai daraja ta ɗaya a Jihar Zamfara, Nijeriya, Justice Lawal Hassan Gummi.

 Allah SWT ya ƙarawa mai martaba Sarki lafiya da nisan kwana mai albarka, ya jaddadawa dukan magabatanmu rahama ya sa mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani Alfarmar Fiyayyen Halitta Rasulallahi Sallallahu Alaihim Wasallam, amin ya rabbal alamin.

Daga Taskar:

Hon. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin Birnin Magaji) Jihar Zamfara, Nijeriya.

5/08/2026.

Sarkin Gummi Na Sha Biyar: Sarkin Mafaran Gummi Justice Lawal Hassan

Post a Comment

0 Comments