𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Salamu alaikum waramatullah malam don Allah ka taimaka min, mlm mijina shi baya saduwa dani haka kawai sai ya saka condum shin idan na hana shi kaina na yi laifi ne? Na gode
MIJINA BA YA SADUWA DA NI SAI
YA SAKA CONDUM
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis Salaam Wa
Ramatullahi:
Toh Wannan Magana ta ki
Akwai Maganganu akai sosai, shin meyasa yake son sa Condom idan zai yi Jima'i
da ke? Haihuwar ne baya so ko Kuma mene ne? sa'annan idan haihuwar ce baya so
shin kema ba ki son Haihuwar ne? idan dukkan ku ba ku son haihuwar ne sai yake
sa Condom, toh sai mu ce babu komai wannan, idan Kuma shi ne baya son haihuwar
ke kuma kina so, toh a nan akwai bayani sosai, za mu yi a gaba. sa'annan idan
yana Jima'i da ke ba ki gamsuwa ne ya sa kike son hana shi domin ba ki gamsuwa?
dole ne a samu Amsosin nan daga gurin ki, Amma kafin nan ga bayanin kamar haka;
1. Abu na Farko Shi ne
Matukar Ke Kina gamsuwa da Mijin ki a Haka, shi ma yana Gamsuwa da ke a Hakan
wato idan ya Saka Kororon Roban (condom) dukkanku Kuna samun Gamsuwa. toh
Wannan Hurumin Mijin ki ne ya Sadu da ke ta yadda yake Son Yin Jima'i da ke
Wannan Hakkkin Sa ne, Domin inda Allahu Subhanahu Wata'ala Yana Cewa, Matayen
Ku Gonakin ne ku je Musu ta inda Kuke so, amma banda ta Duburar ta.
Amma idan Shi ne Kaɗai
yake Gamsuwa Buƙatar
sa ta biya, Amma ke ba ki Gamsuwa ba ki Jin komai idan ya Saka Wannan Kororon
Roban (condom), amma idan bai Saka ba ya Sadu da ke Kin fi Gamsuwa da shi, toh
nan Kuma Wajibi ne gare shi ya Chanja Lalalel, domin Kamar yadda kike Gamsar da
shi yake gujewa neman Matan banza a waje, toh Shi ma yakamata tsaya ya miki
Haka, babu Cuta babu Cutarwa a Ciki.
Amma indai ba Zai rika
Gamsar da ke ba, Sannan ya Ƙi
Chanja Lalalel, kuma Hakan yana Cutar da ke ba ki Gamsuwa dalilin haka kada ki
faɗa
Cikin halaka na zina ko Madigo, toh ki nema Magabatan ku wato Waliyyan ku sai
ki kai Maganar gaban su a Kira sa. Kafin ki fara Ɗaukar
Salon rabuwa da shi Domin kada ya cutar da ke, ki koma Saɓawa
Ubangijin ki ta wajen Aikata abun zai gamsar da ke ko Zina ko Madigo.
Hakazalika, Idan Har hakan
da yake yi ba ki Gamsuwa kuma Kinyi-Kinyi ya gyara ya Ƙi Gyarawa, toh za a iya Raba Wannan
Auren domin Kada Ke ki Faɗa Cikin Saɓawa
Ubangijin ki Wajen yin zina ko Madigo dole ne a raba Auren, Mafi Yawanci a
yanzu abun da wasu Matan Aure suke yi kenan wallahi idan Mijin su baya gamsar
su sai su shiga group na batsa da Namiji ko Mace sun yi musu magana shikenan
sai su yarda su ba da kansu ko Zina ko Madigo sabida haka irin wannan gara an
raba Auren yafi.
2. Na Biyu Shi ne, Idan Har
Ke Kina Son Haihuwa, Shi Kuma Mijin ki baya Son Haihuwa wata Kila Shiyasa yake
Saka Kororon Roban (condom) don kada ki Samu Ciki ki Haihu, kin ga Ra'ayin ki
da nashi ya Banbanta, toh tunda Ke Kina Son Haihuwa Shi Kuma baya Son Haihuwar
Shiyasa ya Saka Wannan robar domin kada Ki Samu Ciki ki Haihu, toh nan ma Za ki
iya Hana shi Kanki, Sa'annan Ki Nemi Magabatan ku ki Sanar da su Cewa ga Abun
da yake tafiya a Tsakanin ku, idan an kira shi ya dawo ya gyara yana Son
Haihuwar ya dena Saka Wannan Kororon Roban (condom), Shikenan haka ake buƙata, idan Kuma ya ƙi ya dena kuma ke kina Son Haihuwa. Toh
kina da Zaɓin ki idan Kin ga Za ki iya Zama da shi
a Haka ba ki Gamsuwa da shi, Sa'annan babu Haihuwa da shi, toh sai ki Ci Gaba
da Zama da shi a Hakan ba tare da yin korafi ba, idan Kuma kina Son Haihuwa,
kuma Kina Son ki Rika Gamsuwa da shi idan yana Jima'i da ke, sai ga shi bayan
Son Haihuwar, kuma ba ya Gamsar da ke, toh Wajibi ne a Raba Wannan Auren domin
gudun faɗawa
cikin halaka na zina ko na Madigo.
Haihuwa na Allah ce idan
Allah ya ga dama, sai ya gama Saka Kororon Roban sa ya Sadu da ke, Sai Ciki ya
shige Miki kuma Ki Haihu, don haka babu Abun da ya gagari Allah. sa'annan ki
sani cewa ke Mace ce kina buƙatar
taimako nan gaba idan kin karar da Karfin ki gaba ɗayan
sa gurin Jima'i babu Yara wallahi za ki dawo ki yi Allah Wa dai da rayuwar ki,
domin Mazajen yanzu ba irin na da bane yanzu sai ki ji ya sake ki, Karfin ki ya
kare ba ki da Yaro ko ɗaya Kuma kin zo Matakin da
lallai kina buƙatar Yaro a kusa da
ke amma babu, don haka Mata a Rika yin nazari sosai kafin ayi abu musamman Yan
Mata da a yanzu kuke son yin Family planning, ke ko haihuwa 1 ba ki yi ba wai
kin je kin yi Family planning idan Allah ya tashi kama ku sai Allah ya rike
haihuwar ki ko kun dawo kuna son haihuwar wallahi ba za ku samu ba.
Ko kuma ki haifi Yara 2 ku
ce ayi Family planning don a samu Tazarar Yaran ku, toh idan Allah ya tashi
kama ku wallahi sai Allah ya ɗauke Yaran kab duk su Mutu
ku dawo yanzu kuna son haihuwar amma wallahi ba za ki taɓa
haihuwa ba ke da haihuwa sai dai a Lahira idan ana Yi, Hakan ya taɓa
faruwa da wata Mijin ta ya ce ta yi Planning ta ce Wallahi ba za ta yi ba ya
buga ya Rawa ta ki, ta yi tambaya aka bata shawara kada ta yi wallahi haka ta ƙi yin Family planning nan, sauran Ƙishiyoyin suka yi, Kun San me ya faru?
Wata Rana suka shirya Yaran
su za su kai ziyara zuwa wani garin, sai suka yi Hatsari Yaran kab suka mutu
babu wadda ya tsira a motar, waɗannan matan da suka yi
Family planning suka dawo suna Buƙatar
Yara ko da 1 ne babu Allah ya rike haihuwar, ita wadda ta ƙi yin Family planning ɗin
sai haihuwa ta ke Yi ta kira tana godiya ta ce lallai ta ga illar family
planning da Kuma iKon Allah, ta ce da ita ma ta yi Family planning nan yaya
zatayi? toh kun ga irin abubuwan dole ne fa a matsayin ki na Mace ki tsaya ki yi
nazari akai sosai kafin ki aikata shi, Mazan wannan Zamanin ba Yan Amana bane
su ce ki yi ki dena haihuwar su je su Auro me haihuwa kina ji kina gani tana
haihuwa ke kuma babu.
3. Na uku, idan Kuma wata
Kila Kina da Ciwo ne a tare da ke, ko Kuma Shi yanada Ciwo a tare da shi ba'a
son a ɗauki
ciwon, toh nan ma idan Shi ne mai Ciwon Za ki iya Hana shi Kanki, Domin kada ya
Raɓa
miki Cuta, Sa'annan rabuwa da shi shi ne ya fi Alkhairi fiye miki akan Zama da
shi yana ɗauke da Ciwo, toh sai dai idan Zai tashi
ya nemi Magani. Idan ma kene mai Ciwon, toh Gaskiya rashin Gamsuwar ki a Wajen
sa hakan zai iya sa Ki raba Aure Domin Gujewa Sheɗan
na Zina. Dafatan Kin Fahimta Koh?
WALLAHU A'ALAMU.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.