Citation: Abdullahi Lawal DIKKO (Ph.D) (2022). Mata A Ma’aunin Sarrafa Harshen Hausa. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Ɓol. 10, Number 1. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State Uniɓersity, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
MATA A MA’AUNIN SARRAFA HARSHEN HAUSA
By
Abdullahi Lawal DIKKO (Ph.D)
Tsakure
Wannan maƙala yunƙuri ne domin fito da mata a ma’aunin sarrafa harshen Hausa. An yi
binciken ne da niyyar gano yadda jinsin matan Hausawa ke amfani da sarrafa
harshe domin a tabbatar da cancantar mata a ma’aunin sarrafa harshe. Wato an zaƙulo yadda mata ke amfani da hikimarsu wajen amfani da harshen
Hausa ta fuskoki mabambanta tare da bayyana irin kalmomin da suke amfani da su
a cikin maganganunsu na yau da kullum, kamar karin magana da habaici, da sara
da saye saboda haka wannan maƙala ta nazarci irin
gudummuwar da jinsin mata ke ba da wa wajen amfani da harshen Hausa, wanda
kusan in an gwama su da maza ana iya cewa sun yi wa mazan zarra wajen amfani da
hikimomin sarrafa harshe da kuma yin amfani da wasu keɓaɓɓun zantuka da kalmomin harshen Hausa. Manufar
wannan maƙala ita ce a fito da wasu muhimman al’amura da
suka shafi sarrafa harshe waɗanda mata suka fi amfani
da su, da kuma zayyana yadda suke amfani da su fiye da maza. Maƙalar ta gano cewa jinsin mata suna taimakawa wajen fito da al’adun
Hausawa ta hanyar mata. Baya ga haka dukkanin saƙon da mata ke ƙoƙarin isar wa ta hanyar waɗannan fuskoki da aka
nazarta, yana isa dai dai babu wani cakuɗeɗeniya ko caɓewar zantuka. A ƙarshe an fahimci cewa jinsin mata sun cancanci ma’aunin nazarin
harshensu, saboda muhimman bayanai da aka samu da kuma irin saƙonni da suke isar wa cikin hikima da adana harshen ya tabbata har
tsawon rayuwa, kuma mata sun kasance ma’ajiya da makaranta ta sarrafa harshe ga
‘ya’yan Hausawa. A lokacin gudanar da wannan nazari an fuskanci waɗansu matsaloli dangane da halayar mata musamman abin da ya shafi
kunya wajen gano muhimman bayanai daga bakinsu. Sa’annan sun fi yin al’amuran
su tskaninsu da ‘yan uwansu mata.
Gabatarwa
Harshe na taka muhimmiyar rawa wajen sadarwa ga
kowace irin al’umma. Wajen yin magana, ana iya banbance jinsin ta mace da na
namiji. A cikin wannan takardar an yi ƙoƙarin ankarar da abubuwan da suka shafi jinsin matan Hausawa wajen
amfani da harshe, sakamakon haka, an nuna damar da harshen mata ya samu wajen
walwala ta fuskar magana ta hanyar shimfiɗa zantukansu akan turbar
da ta dace, domin isar da saƙonsu cikin hikima da zalaƙa da nuna basirarsu wajen amfani da harshen. Sa’annan a cikin
wannan maƙala an fito da misalai dabam – daban daga sara
da saye da karin magana da kuma habaici inda aka zayyana irin Hausar matan,
tare da kawo misalan kalmomin da suka ta’allaƙa ga mata. Bugu da ƙari wannan takarda ta ƙyallaro mana harshe na
da tasiri wajen fito da al’adar Malam Bahaushe a fili ta hanyar bayyana wasu
muhimman al’amurran da suka shafi hikimar matan Hausawa da ayyukansu. Sannan
kuma an tattauna wasu muhimman batutuwan da suka shafi jinsin mata a cikin maƙalar.
Ma’anar Harshe
Bunza (2013, sh. 209) ba wani abu ne harshe,
face hanyar sadarwa da ke wakana tsakanin mutum da mutum ta fuskar magana da
daidaitaccen lafazi da aka saba da shi, sadarwa ta fuskar magana ita ce,
harshe, kuma ita ce sunan da ake bai wa kowane harshe a doron ƙasa.”
Harshe shi ne tubalin gina duk wata zamantakewa
da cuɗanya a tsakanin al’umma, sai dai dabarun sadarwa
na iya zuwa ta sigogi mabanbanta, wato hanyoyi da dama, daga ciki akwai ishara,
akwai magana da baki, akwai taɓa mutum a sassan gaɓoɓi da makamantansu.
Bita
Masana kimiyyar harshe da nazarin walwalar
harshe da sarrafa harshen sun yi ƙoƙarin bayyana mana al’amurran da suka shafi waɗannan fage ta fuskoki da dama, da kuma irin rawar da suka taka.
Saboda haka, za mu yi waiwaye kaɗan don mu fa’idantu ga
abin da suka furta domin ya zama matashiya ko ishara ga manazarta. Daga ciki
akwai waɗanda suka bayyana mana irin cigaban da aka samu
a harshen Hausa. A yau tare da ba da shawarwari irin waɗannan masana sun haɗa da Abubakar (2006) da
Muhammad (2006) da Amfani (2011).
Abubakar (2006) ya yi tsokaci a kan Hausa a yau,
in da ya waiwaya baya, ya zayyana cewa in ana son a san yau sosai to dole a
kalli jiya a fahimce ta da kyau sosai, ya cigaba da bayyana yadda aka fara
amfani da harshen Hausa.
Muhammad (2006) kuwa ya nusar da mu game da
muhimmancin harshen da yake cewa: “in ka ɗebe iskar shaƙa da ruwa da abinci, kusan babu wani abin da ya kai harshe
muhimmanci ga ɗan Adam, in ban da ilimi wanda shi ɗin ma kuma sai da harshen ake naƙaltarsa sosai.
Hudson (1996) da Wardhaugh (2007) sun yi tsokaci
kan abin da ya shafi walwalar harshe inda Hudson (1996, sh. 43) ya yi tsokaci
dangane da irin abubuwan da suka shafi nazarin kimiyyar harshe musamman ma a
nazarin ilimin walwalar harshe binciken ya tabbatar da ana iya samun banbance –
banbance na karin harshe na yanki da na rukuni ko shiyya. Amma Wardhugh (2007,
sh. 11) ya yi sharhi game da surki, ya nusar da cewa duk inda aka sami mutum
guda ko biyu suna tattaunawa a tsakaninsu to dole a samu tasirin surki a cikin
zantukansu.
Dangane da maƙaloli da suka
shafi ɗabi’un mata ta fuskar kunya a cikin al’amurran
rayuwar mata a yau akwai aikin Bilkisu (1991) da Gusau (1994) da Rabi (2010).
Bilkisu (1991) ta yi bayani a kan gwagwarmayar
mata wajen bunƙasa halin da suke ciki a yau. Ita kuwa Rabi
(2010) ta bayyana cewa “kunya hanya ce ta nuna ɗa’a da kawaici, wato, idan mutum zai yi abu, ya duba abin da zai
je ya dawo ta ɓangaren kansa da tsakaninsa da jama’a da kuma
mahaliccinsa.”
Ƙwarewar Mata Wajen Sarrafa Harshen Hausa
Wasu dalilai ne d za’a iya tabbatar da haka.
Abin da ya takalo wannan batu a wannan wuri shi ne ra’ayin da ake da ita game
da amfani da harshe ta fuskar fifiko a tsakanin mata da maza Laboɓ (1982, sh. 191). Mata suna ganin sun fi maza laƙantar harshe da sarrafa shi, amma wannan batu bai hana maza su ma
su rinƙa ganin sun fi mata ba. Babbar hanyar da za a
iya tantance haka ita ce ta yin la’akari da abin da manazarta da masana suka
hango, da kuma muhimmancin harshe, A tsarin zamantakewar al’ummar Hausawa,
akwai waɗansu muhimman abubuwa da ba a taɓa iya kauce musu, sai da su rayuwa ke tabbata cikin nasara da
walwala. A nan, ana iya bugun ƙirji a ce harshe shi ne
farko, wato ginshiƙi ne na rayuwar kowace al’umma. Dukkanin
al’amurran rayuwa da harshe ake yin su, dole mutum ya yi magana da ɗan uwansa ko abokin zamantakewarsa domin rayuwa ta bunƙasa. Harshe ke gina al’umma, harshe ke gina ƙasa a samu ci gaba. Harshe ake amfani da shi a makarantu na ilimin
addini ko ilimin boko. Makarantar farko ga al’umma ita ce mata, domin su ne ke
fara koyar da magana da tarbiyya kai har ma da karatu a kowane fage. In haka ne
mata suna taka muhimmiyar rawa wajen amfani da harshe da tabbatar da
muhimmancinsa.
Majid (2012, sh. 105) ta yi bayani kamar haka:
“Ji nan Bashir ka da ka sa na yi magana da yawa, ka san abin da zai ja ni na
ce. Don haka, bari ka ji. Na riga na zartar da auranka. In kuma za ka ƙi, sai ka ƙi. Ka san ni, ka san abin da zan iya yi maka
tasiri kuma ka san zamowar ka ɗan aba zai yi maka komai
ba.”
Kalamanta sun nuna cewa a nan, mata ba su faye
yawan son magana ba, ko su biyu ne ko kuma fiye. Sun fi son a yi magana kai
tsaye ‘yar kaɗan. Tsarin zamantakewar Hausawa ya yo naso daga
tarbiyyar da suka samu daga addinin Musulunci saboda ba a yarda ka saki matarka
ta tafi duk in da ta ga dama ba. Dole sai da kulawa. Abu ne da addinin
Musulunci ya yarda da shi. Ba a yarda mace ta shiga cikin maza tana cakuɗeɗeniya da su ba, ko kuma ta riƙa garari kamar maza. Adamu (2001, sh. 79) ta bayyana cewa: “keɓanta da mata ke yi ya takura su daga yin al’amuran da suka shafi
gida sai dai da taimakon ‘ya’yansu mata da yara, wajen sayo musu duk wani abu
da suke buƙata, ko kuma sayar da wani abu na ƙaruwa da suke yi.” Saboda haka, zaman gida ya taimaka masu wajen
amfani da harshe sosai.
Wani abin la’akari cikin wannan batu mata shi ne
akwai banbancin fahimta a cikin al’amuran da suka jiɓanci lamarin jinsintaka, Yakasai (2009, sh. 191). Haƙiƙa masana irin su Ma da Broker sun nazarci
matsalar rashin fahimta tsakanin maza da mata, kuma sun amince tasirin al’ada
ne ya haifar da bambanci tsakanin maza da mata cikin sadarwa. Haka kuma nazarin
maganganun yara, sun gano cewa matan Turawa suna da al’ada mabambanciya kuma
hakan ya yi tasiri kan mu’amala tsakanin maza da mata. Keɓantuwa da shiga jama’a kowane akwai irin tasiri da yake
haifarwa.
Ma’aunin Harshen Mata
Yakasai (2012, sh. 95): ya nuna cewa ana amfani
da abubuwa daban – daban wajen sadarwa da suka haɗa da kalmomi da ishara
da gaɓuɓɓa da kuma ɗabi’a. Wannan bayani ya yi daidai domin ai ita sadarwa yanayi ne
da ake sarrafa bayanai tsakanin al’umma, cikin tsarin kalmomi da ishara da
kuma ɗabi’a wato kafin sadarwa ta tabbata. Wajibi ne a
sami fahimtar juna tsakanin mai magana da kuma wanda ake yi wa magana. Idan har
waɗannan kalamai da aka zayyana na da muhimmanci ga
al’umma a matsayin sinadarin gina zantuka a rayuwa. Duk inda aka sami jinsin
namiji da mace, za a iya gane waya fi cin gajiyar abin ko ya fi amfani da shi,
ko wa ya fi zama kan gaba a wajen amfani da harshen. Mata sun cancanci ma’auni
a wajen nazarin harshensu, domin kuwa yadda suke amfani da harshen Hausa ana
iya cewa abin a duba ne musamman abubuwan da suka danganci sarrafa harshe.
A nan, ba mun yi la’akari da yawan kalmomu ne da
kowane ke amfani da su ba, illa mun bi wasu muhimman bayanai ne da nazarin ya
hango ta hanyar amfani da sarrafa harshe a bakin matan Hausawa.
Matan Hausawa da kansu sun bigi ƙirji, sun tabbatar da cewa sun fi maza amfani da karin magana.
Babban dalilin su shi ne mata suka fi zaman gida, sa’annan ga zama cikin
kishiyoyi. Domin haka ba a raba su da habaici ga kishiyoyinsu a cikin gida
saboda ta wannan hanya ce suke iya mayar da martani da cusa wa kishiya baƙin ciki. Mu’amalarsu da ɗabi’unsu na zamantakewa
sun ta’allaƙa da cikin gida.
Harshen mata ya cancanci ma’auni wajen yin
nazari, akwai su da cuɗanya da mutane da gudanar da hulɗoɗi sosai a tsakanin su da juna da kuma sauran
al’ummomi ta fuskoki mabanbanta. Sakamakon haka, suna da ƙoƙarin son a san sun san harshe ta hanyar amfani
da harshe a cikin maganganunsu na yau da kullum.
A lokacin tattaunawa da aka yi da mata kai
tsaye, sun kawo waɗannan misalan habaici.
i.Wash Allah! Uwar Sani wash
Allah!
Na ciwo Uwar Sani na ciwo.
Daddanna Uwar Sani
Daddanna Uwar Sani ƙungurun Uwar Sani ya Karye
ii.Tankarin Gida ɗa namiji
Ko mace tankar gida ce don ko ba ta so a fidda
rabonta.
iii.Bana mun yi ɗa,
Bana babu kaɗi,
shekarata goma ina kaɗi,
Banga amfanin ka ba auduga,
Bari in raurau da maje gaba
Dan maje gaba ya fi zani wuya
Gaskiyar magana ita ce, mata a nan, sun yi
amfani da sarrafa harshe ta hanyar habaici domin mayar da martini da
kishiyoyinsu kamar yadda muka gani a misalan da ya gabata. Wani abin la’akari
shi ne mata akwai su da nuna kaɗifiri da son a sani da nuna burgewa a lokacin da
suke tattaunawa. Ba ka raba su da amfani da kalmomin sara a cikin zantukansu.
Kalmar da ake kiran kishiya:
|
Kalma |
Ma’ana Wurin mata |
|
Shu’uma |
Mace mai kissa da
kinibibi |
Kalmar da ake kiran dangin miji:
|
Kalma |
Ma’ana
Wajan Jama’a |
Ma’ana
Wurin Mata |
|
Gidan ƙaya |
Inda ba mafita ko gidan wahala |
Gidan da ake zaune da uwar miji |
Kalmomin da ake kiran samari:
|
Kalma |
Ma’ana
Wajan Jama’a |
Ma’ana
Wurin Mata |
|
Na waje na |
Na kusa da ni |
Saurayin da ake so |
Haƙiƙa mata na amfani da saye domin sakaya ko ɓoye wani abu da ba a son a faɗi kai tsaye, ko ba a son
wani ya san abin da ake nufi ko aka faɗa. Haka kuma mata na
amfani da saye domin sirrantawa a tsakaninsu. Irin waɗannan kalmomi da mata kan yi sayensu sun haɗa da kalmomin jinin al’ada. Misali su kan kira su da sunaye kamar
haka:
Ta hau danja
file ya fashe
Jar mota
tana busy
Manja baƙo daga ɗanja
Kalmomin sara da suka danganci aure:
|
Kalmar
saye |
Ma’ana |
|
Baya kwanciya da ni |
Baya jima’i da ni |
|
Ba ya ɗaukar kwano na |
Ba mu saduwa |
Karin magana na daga cikin zantukan hikima da
matan Hausawa ke amfani da su acikin zantukansu na yau da kullum, yana
taimakawa wajen tattauna a tsakanin da juna wajen mayar da martini kan wani
magana da ya auku, misali: Gyaran hali ko wata matsala da ke aukuwa ko nishaɗantarwa ko nuna haɗin kai da zumunta.
Misalan Karin Maganan da Mata ke yi sun haɗa da:
i.Haka tara, inji
kishiyar mai mageɗuwa.
ii.Allah uba inji
shegiya.
iii.Ƙaƙa zan yi da abin da ya gagari wuta, inji
kishiyar ƙonanniya.
iv.Karuwa, ba ta kiwon
kaza.
v.Jiya ba yau ba tsohuwa
da ɗaga azzakari.
Ta fuskar sarrafa harshe, an sami mata da suka
ciri tutar yabo da basira a harkar waƙoƙi na Hausa tun daga ƙarni na 19 har
zuwa ƙarni 20 da na 21. Waɗannan mata mawaƙa sun yi waƙoƙi a fannoni da dama. Maƙasudin wannan, shi ne
bayyanar da sunayensu, domin su zama masu amfani ga manazarta kuma mu tabbatar
da cewa lallai in ana batun ƙwarewa a maganar harshe
to, mata a wannan fage ba baya ba, kama tun daga waƙoƙin addini da na Nishaɗantarwa. Daga ciki irin waɗannan mata akwai:
|
Mawaƙiya |
Jigon
Waƙoƙi |
|
i.Burmani Choge |
Sana’a/kishi/ilimi |
|
ii.Ladi mai kutinga |
Zuga/tarihi/salsala |
|
iii.Uwaliya mai Amada |
Soyayya/aljanna |
|
iv.Nana Asma’u Ɗiyar Shehu Usman Ɗanfodiyo |
Tuhidi/gargaɗi/wa’azi |
|
v.Modibbo bilo |
Wa’azi gargaɗi |
|
vi.Hauwa Gwaram |
Faɗakarwa/ra’ayin
mata |
Babu shakka, siyasa na da muhimmanci, sanadiyyar
walwalar harshe da ake samu a ciki, matan da suka yi fice na amfani da sarrafa
harshe sosai. Akwai mata da suka yi fice ana gwagwarmaya da su wajen taka
muhimmiyar rawa domin ƙwato wa mata ‘yancinsu, waɗannan mata kan hau duro su yi jawabi don a san da zaman su da
tsarinsu. Daga ciki sun haɗa da:
i.Hajiya Gambo Sawaba
Zaria
ii.Asabe Reza Kano
iii.Hajiya Jummai ‘Yar
rawar Banjo Zaria
iv.Hajiya Lela Dogon
Yaro Kaduna
v.Naja’atu Muhammad Kano
Dangantakar Harshen Mata Tsofaffi da Mata Matasa
A sauƙin fahimta, da sanin
makaman mata, dangane da batun magana tsakanin mata tsofaffi da mata matasa,
akwai abubuwan lura da suka kamata a yi la’akari da su. Bahaushe kan ce waƙa a bakin mai ita ta fi daɗi. Saboda haka a wannan
fage an yi hira da tattaunawa da mata domin wannan takarda ta bayyana abin da
ake so a isar sosai. Ga abin da nazari ya samar:
a) Mata matasa akwai ƙuruciya, amma mata
tsofaffi suna haɗawa da karin magana.
b) Mata Matasa ba a raba mu da zagi. Misali:
Uwarka, Ubanka. Amma da wuya ka ji tsofaffi suna zagi sai dai a ce: “ɗan danbolan uwa ka ci gidanku” da sauransu.
c) Wurin magana ta yau da kullum, mata tsofaffi sukan ce kin yi
kalace? ‘Yammata matasa kuwa sai su ce: “kin yi break fast?”
d) A wajen zantukan hikima tsofaffi kan ce: “Ai
hali ya ce je ki kar ki daɗe.” Ma’anar wannan zance duk in da ka ke halinka
zai bika.
e) Wani lokaci mu mata tsofaffi in mun yi magana sai a ce “ɗumin tsufa ce”.
f) A wajen murya akwai bambanci tsakanin muryar mata tsofaffi da mata
matasa. Muryar tsofaffi ba ta ƙara kamar ta mata
matasa. Akwai su da tausasa murya da yi mata kwaskwarima domin ta yi zaƙi ta ratsa zukata. Misali: mata tsofaffi kan ce ni ban iya da
kayan tambaɗar banza.
Babu shakka ana iya bugun ƙirji, idan aka yi la’akari da wannan bayanai na mata tsofaffi da
mata matasa. Sai dai su kan su ‘yan mata sun tabbatar da cewa mata tsofaffi
akwai su da amfani da karin magana da yin amfani da tsofaffin kalmomi irin na
dauri, fiye da mata matasa. Sannan tsofaffi akwai su da amfani da tsara magana
cikin azanci da hikima. Amma wajen amfani da sarrafa harshe kamar sara da saye
da surki mata matasa sun fi zarra a nan, sanadiyyar karatun boko a zamanance.
Kammalawa
Daga ƙarshe wannan maƙalar ta cimma nasarar bayyana cancantar mata a ma’aunin sarrafa
harshen Hausa, kamar yadda taken takardan ya bayyana. An fito da manufar
takardar, sannan an fito da muhimman bayanai da suke tabbatar da keɓantuwar mata a wasu muhimman fage na hikimomin malam Bahaushe tare
da nuna zantukan da suke da alaƙa ga matan Hausawa da kuma irin gudunmuwar mata
wajen amfani da keɓantattun zantuka na mata da kuma kalmomin da
mata ke amfani da su. Bugu da ƙari takardar ta bayyana
muhimman abubuwan da ke tabbatar da ƙwarewar mata wajen
sarrafa harshe da kuma irin abubuwan da ake dubawwa wajen tabbatar da cancantar
zama ma’auni a wajen nazarin harshe. Sannan an fahimci cewa duk wani abu da
maza ke amfani da su wajen sarrafa harshe mata ma ba a bar su baya ba. Mafi yawan
lokuta kamar yadda aka gano a wannan bincike zaman gida ya bai wa mata damar
taka gagarumin rawa wajen yin amfani da harshe da koyar da shi musamman ga
yara. Sannan waɗansu al’amuran sarrafa harshe ya keɓanta ga mata su suka fi amfani da su.
Daga cikin abubuwa da wannan aiki ya gano ta
fuskar ƙwarewa wajen sarrafa harshe shi ne ta hanyar
amfani da harshe a cikin zamantakewar al’ummar Hausawa sakamakon harshe ginshiƙi ne na rayuwar Hausawa wajen magana. Makarantar farko na koyar
magana ita ce mata, domin kamar yadda binciken ya gano nan ne ake koyar da yaro
iya magana. Saboda haka, ilimin addini da na boko sai da harshe ake iya sarrafa
shi. Sa’annan binciken ya gano yadda ake iya tantance harshe mace da namiji,
wadda binciken ya danganta shi da irin kayayyakin da ake tanada su tabbatar har
tsawon rayuwan, daga ciki akwai muhimman abubuawan da aka yi rikodin a
faya-faye ko aka dauka a rediyo ko kuma litattafai da aka rubuta domin amfanin
al’umma. Bugu da ƙari, binciken ya tabbatar da cewa duk abin da
maza ke iya yi mata na yi wani lokaci har su fi mazan. Sannan kowani irin aiki
da maza ke yi a yau mata na yi tun daga aikin ofis har zuwa karantarwa, harkan
siyasa da saursansu. Dagane da amfani da harshe an yi ƙoƙarin nazartan wasu muhimman al’amura da suka
shafi karin magana saye da sara an fito da su da ma’anar su da yadda mata suka
fi ta’ammali da su. A ƙarshe an zayyana nau’in maganar mata tsofaffi da
mata matasa a wajen sarrafa harshe. Ana fatan wannan takarda ta zama mai amfani
ga manazarta da masana wajen yin bayanin abubuwa da ke tabbatar da mizanin
ma’aunin sarrafa harshe a bakin mata. Haka kuma zai zama kundi na sarrafa
harshen mata a ɗakunan karatu.
Manazarta
Abubakar, A. (2006). Matsayin
nazarin harshen Hausa a yau, Algaita. The Journal of Current Research
in Hausa Studies. Ɓol. 1 No. 12 – 15.
Adamu, F.L (2001). My wife’s tongue deliɓers more punishing blows than Muhammad Ali’s first bargaining
power in Nigerian Hausa society. Chester Academy Press.
Amfani, H.A. (2011). Hausa language and
Hausa people: Yesterday, today and tomorrow, One Day Symposium. Ahmadu
Bello Uniɓersity.
Bilkisu, Y. (1999). Hausa Fulani women. The
state of struggle. In Catherine Coles and Beɓerly Mark Hausa
women in the 20th century. Wisconsin Press.
Bunza, M.A. (2013). Don me ake karatun
Hausa? Harsunan Nigeria Ɓol. ƊƊIII.
Gusau, S. M. (1994). Dubar alkunya: nazarin
ma’anarta da nasonta a waƙoƙin makaɗan baka. Sashen Harsunan Nijeriya. Jami’ar Bayero.
Hudson, R. A. (1996). Cambridge books in
linguistics. Sociolinguistics second edition. Cambridge Uniɓersity Press.
Laboɓ, W. (1982). The
study of language use social conteɗt sociolinguists. Harmones Worth Penijuine 1972. Pride &
Holmes.
Muhammad, Y.M. (2011) . Hausa a
yau. Ahmadu Bello Uniɓersity Press.
Rabi, G. (2010). Kunya adon matan Hausawa. Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies Ɓol. 1 No. 3. 20 – 30.
Wardhaugh, R. (2010). An introduction to
sociolonguistics, siɗ edition. Wiley - Black Publication.
Yakasai, A. S. (2009). Harshe a bakIn
maza da mata, wariya ko bambanci. Himma Journal of Contemporary
hausa Studies, Ɓol 1 No. 1.
Yakasai, A. S. (2007). Dangantakar harshe da
al’umma: Nazarin halaye da ɗabi’un magana a al’ummar
Hausawa. Maƙalar da aka gabatar a Taron ƙarawa Juna Sani. Sashen
Harsunan Asiya da na Afirka. Jami’ar Koyan Harsunan Waje ta Beijing 06-06-2007.
Yakasai, A. S. (2012). Jagoran ilimin
walwalar harshe. Garkuwa Media Serɓices.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.