Ticker

6/recent/ticker-posts

Bambanci Tsakanin Wakokin Siyasa na Karni Na 20 da na Karni Na 21

Citation: Abdullahi Haruna IMAM da Shamsuddeen ISMA’IL (2022). Bambanci Tsakanin Waƙoƙin Siyasa na Ƙarni Na 20 da na Ƙarni Na 21. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Ɓol. 10, Number 1. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State Uniɓersity, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660

BAMBANCI TSAKANIN WAƘOƘIN SIYASA NA ƘARNI NA 20 DA NA ƘARNI NA 21

Na

Shamsuddeen ISMA’IL

Abdllahi Haruna IMAM

Abstract

Hausa poems have been one of the major weapons for stimulating politics in Northern Nigeria. These poems are termed as political poems used for campaign. This paper is an attempt to compare the 20th and 21st centuries Hausa political poems where different poetic features served as bedrock to the analysis. The paper is a complete library research in which different literary works such the collection of poems and recorded poems serve as our sources of data. The work is based on Birniwa (1987)’s model of approach which shows that this class of Hausa poems have been in used for political propaganda since 1956-1983. The paper reveals that the two generations of poems (20th and 21st centuries) are similar but slightly different in terms of their themes, structure, and style and language proficiency.

Gabatarwa

Tun wajen ƙarni na sha bakwai (17) Turawa suka fara zuwa ƙasashen Hausa da niyyar binciken ƙasa, da sanin kogunan da suka ratsa Afirka. Daga baya suka dinga zuwa saboda sha’anin ciniki. A ƙarshe dai farkon ƙarni na ishirin, Turawan Faransa da na Ingila suka karɓe mulkin ƙasashen Hausa daga hannun sarakunan Hausawa. Su waɗannan Turawa, sun canza tsarin mulkin waɗannan ƙasashe, da irin nasu tsarin mulkin. Ban da tsarin mulki kuma, Turawa sun kawo wa Hausawa wata sabuwar hanyar karatu da rubutu irin nasu. A hankali har Hausawa suka koyi yadda za su rubuta Hausa ba baƙaƙen Turanci, wato rubutun boko. Haka kuma Turawa sun kawo wa Hausawa wasu sababbin kayayyakin fasaha da kimiyya, kamar su jirgin sama da jirgin ƙasa, da mota da basukur, da keken ɗinki da su wayar Magana (telephone). Duk waɗannan abubuwa sun yi tasiri wajen rubuta waƙoƙin ƙarni na ishirin. Wani abin da ya kawo canji wajen rubuta waƙoƙin ƙarni na ishirin shi ne, yadda tunanin Bature ya yi tasiri a kan Bahaushe. Kafin zuwan Turawa, duk sha’anin Bahaushe ya tafi kan sha’anin addini ne. Yadda zai kiyaye addininsa a zamaninsa na duniya, da kuma yadda zai samu tsira gobe ƙiyama. A wannan lokaci Bahaushe bai da wani tunani a kan yadda zai kyautata rayuwar duniya, domin bai ɗauki duniya wurin zaman jin daɗi ba. Shi a wurinsa, duniya wuri neman jin daɗin zaman lahira ne kawai. Wannan shi ya sa duk waƙoƙin da Bahaushe zai rubuta kafin zuwan Turawa, zai rubuta su ne kan sha’anin da ya shafi addini. Jamhuriya ta huɗu wadda kusan ita ce ta fi ƙawatuwa da rubutatun waƙoƙin siyasa, kuma a daidai wannan lokaci ne ƙarni na ishirin da waƙoƙinsa suka zo ƙarshe, an samar da rubutattun waƙoƙi masu yawan gaske, wanda Allah ne kaɗai ya san adadinsu. A zangon farko na wannan jamhuriya wanda ya gudana daga shekarar 1999-2003, jam’iyyun P.D.P da A.P.P su ne jam’iyyun da suka yi fice a wannan ƙasa. A wannan zangon farko an samar da rubutattun waƙoƙi ga waɗannan jam’iyyu na P.D.P da A.P.P.

Waƙoƙin Siyasar Ƙarni Na Ishirin (Ƙ.20)

Birniwa, (1987) ya bayyana yadda ake amfani da waƙoƙi don yin farfagandar zaɓe da neman goyon bayan jama’a tun shekarar 1956-1983. An kuma raba wannan kundi zuwa gida biyu, kashin farko ya ƙunshi nazarin waƙoƙin siyasar farko, waɗanda aka samar a shekarar 1940-1966, waɗannan waƙoƙin suna nuni ne a kan ra’ayin riƙau ta fuskar addinin Musulunci daga jam’iyyar N.P.C sai kuma wasu waƙoƙi masu ra’ayin kawo sauyi bisa tafarkin addinin Musulunci daga jam’iyyar N.E.P.U. Sai kuma sashe na biyu wanda ya ƙunshi yadda aka gina waƙoƙin zamanin siyasa ta biyu tun daga shekarar 1978-1983. Manazarcin ya bayyana yadda jam’iyyar N.P.N wadda ita ce ta gaji jam’iyyar N.P.C ta canza bisa ra’ayinta na riƙau bisa ga sassauƙan ra’ayin addini ta fuskar siyasa. A ɓangaren jam’iyyar ceton al’umma kuma wato jam’iyyar P.R.P wadda kuma ita ce ta gaji N.E.P.U tare da manufofinta, tana nan bisa aƙidar nan ta kawo sauyi ba tare da wani bayyanannen canji ba. A jamhuriya ta farko jam’iyyun N.P.C da N.E.P.U su ne suka samu gindin zama a wannan yanki, an kuma samu rubutattun waƙoƙi da marubuta suka yi na tallata jam’iyu ko aibanta abokan adawarsu. Marubuta irin su Sa’du Zungur, Gambo Hawaja, Mudi Sipikin, Lawal Maiturare, Aƙilu Aliyu da Yusufu Kantu da dai sauransu duk sun bayar da gudummowa ta wannan hanya, misali: Gambo Hawaja da Aƙilu Aliyu duk sun yi rubutattun waƙoƙi na jam’iyyar N.E.P.U, wato jam’iyyar adawa, a lokacin, cikin waƙoƙin suke caccakar jam’iyyar N.P.C, ga abin da Gambo Hawaja ke cewa a cikin baiti na goma da na goma sha ɗaya:

Albarkacin Manzonka zan yabi jam’iyya,

Mai son tunɓuke zaluman Nijeriya.

Ita jam’iyar N.E.P.U ta ɗau anniya,

Sai ta ga bayan zalumai mashaya giya.

Shi kuwa Aƙilu Aliyu ya aibata jam’iyyar N.P.C a cikin waƙarsa baiti na biyu, inda yake cewa:

Kuzo talakawa in baku,

Abin da yake amfaninku,

Mazanku da mata taronku,

Ku zaɓi sawaba ce taku,

Ku yada zalama N.P.C.

A can gaba kuma, a baiti na goma sha ɗaya ya ƙara da cewa:

Mu karɓi nasihar nan tamu,

Mu zaɓi talakawa namu,

Waɗanda suke jin tausanmu,

Saboda suka kai kakarmu,

A wargaza mulkin N.P.C.

A jamhuriya ta biyu kuwa, jam’iyyar N.P.N da P.R.P da G.N.P.P su ne jam’iyyun da suka yi tashe a wannan yanki, su ma waɗannan jam’iyyu sun samu marubuta waƙoƙi da suka rubuta waƙoƙi na tallatawa ko kuma na kushe wata jam’iyya, kamar yadda Isah Bunguɗu yake aibata jam’iyyar N.P.N mai mulki a wancan lokaci, a cikin waƙarsa da yake yi wa jam’iyyarsa ta P.R.P, ga yadda yake nuna ƙiyayyarsa ga jam’iyar N.P.N a baiti na sha tara:

N.P.N ba ni sha’awarki,

Ba na sha’awar aƙidarki,

Ba na son komai na mulkinki,

Ban yarda a baki mulki ba.

Shi kuwa Malam Muhammadu Ɗunɗaye a waƙarsa mai taken “’yan santsi kun zama ƙaya” ya yabi jam’iyyar N.P.N, inda yake cewa:

Jama’a yau gara ku gane,

N.P.N alheri ne,

Don Alhaji Shehu mutum ne,

Kuma shi mai kyan asali ne,

Kuma N.P.N ba maita.

N.P.N goshi jirgi,

Ita ta wuce ai mata gigi,

Kada ma ka sake kai wargi,

N.P.N ba ta zagi,

Domin ta tsare girmanta.

Ita ma dai jamhuriya ta uku ko da ba ta yi tsawo rai ba, jam’iyyun da suka yi zamani a wannan lokaci su ne jam’iyyar N.R.C da S.D.P su ma an samu marubuta waƙoƙi da suka rubuta waƙoƙi a kan waɗannan jam’iyyu, sai dai saboda taƙaitaccen lokaci, wannan tafiya ba a samu fitattun waƙoƙi da yawa ba, domin waƙoƙin da za a iya samu akasari waƙoƙin baka ne, ba rubutattu ba amma duk da haka, wani marubuci mai suna Garba Gashuwa ya samar da wata rubutacciyar waƙa da ta haɗe jam’iyyun biyu kamar yadda baitin amshin waƙar ya nuna:

Allah kiyaye jam’iyyu biyu da an kai bana,

Ya taimaki jama’armu ba zasu kure ba.

Bayan rugujewar wancan tsari a jamhuriya ta uku sai kuma gwamnatin marigayi Janar Sani Abaca ta sake aza tubalin wani zango na jamhuriya ta uku inda a wannan lokaci jam’iyyun U.N.C.P da D.P.N da C.N.C da G.D.M da N.C.P.N suka kutso fagen, jam’iyyun U.N.C.P da D.P.N su ne suka yi zarra, to a wannan karo ma an samar da rubutattun waƙoƙi ga waɗannan jam’iyyu, misali jam’iyyar U.N.C.P wadda kusan za a iya cewa ita ce take da rinjaye an yi waƙoƙi domin tallata ta, kamar waƙar Malam Garba Gwandu inda yake bayyana manufofin jam’iyyar, ga abin da yake cewa a wani baiti na waƙarsa:

U.N.C.P fatinmu na shirin ƙwarai ƙauyukka,

Birane su zama irin ƙwarai.

Abinci za shi lirwanta har sutura ƙwarai,

Mu zama har da zama lafiya to ji kai,

Zo yi musafaha kar ka yarda da ruɗuwa.

Shi kuwa Alhaji Aminu Ibrahim Ɗandago, shi ma ya waƙe jam’iyyar U.N.C.P inda ya tabbatar da anniyarsa ta nema wa jam’iyyar magoya baya, ga abin da yake cewa a wani baitin waƙar:

Ni jam’iyya mai Kwando,

Ranar zaɓe zan zaɓa,

Nai alƙawari ran zaɓe,

Kowa na gane shi a raɓe,

Zan masa ƙaimi yai zaɓe.

Ɗan’illela (2012)

Waƙoƙin Siyasa Na Ƙarni Na Ishirin Da Ɗaya (Ƙ.21)

Jamhuriya ta huɗu wadda kusan ita ce ta fi ƙawatuwa da rubutatun waƙoƙin siyasa, kuma a daidai wannan lokaci ne ƙarni na ishirin da waƙoƙinsa suka zo ƙarshe, an samar da rubutattun waƙoƙi masu yawan gaske, wanda Allah ne kaɗai ya san adadinsu. A zangon farko na wannan jamhuriya wanda ya gudana daga shekarar 1999-2003, jam’iyyun P.D.P da A.P.P su ne jam’iyyun da suka yi fice a wannan ƙasa. A wannan zangon farko an samar da rubutattun waƙoƙi ga waɗannan jam’iyyu na P.D.P da A.P.P.

Alhaji Ibarhim Aminu Ɗandago da Muhammadu Ɗanmusa na daga cikin jerin waɗanda suka samar da fitattun waƙoƙin tallata jam’iyyar A.P.P a lokacin.

Alhaji Aminu Ɗandago shi ya samar da sananniyar waƙar nan da ta mamaye ƙasar nan baki ɗaya, ta jam’iyyar A.P.P, wadda ke da amshi kamar haka:

Ba ma shakka cikin ƙasa ita ce ja gaba,

A.P.P jam’iyyar mutanen Nijeriya.

Shi kuma Muhammadu Ɗanmusa ya samar da wata waƙa mai taken:

A.P.P zan zaɓa,

Don ta kare hakkin talakawa.

Ta ɓangaren jam’iyyar P.D.P kuwa, ita ma marubuta kamar irin su Haruna Aliyu Ningi ya rubuta wa jam’iyyarsa ta P.D.P waƙoƙi guda biyu, sun yi matuƙar fice a wannan ƙasa musamman a lokacin yaƙin neman zaɓe. Waƙar farko tana da amshi kamar haka:

P.D.P jam’iyya ta,

Abar so a zukata,

Mutanen Nijeriya ku taso mu riƙe ta.

Da kuma waƙarsa mai amshi kamar haka:

P.D.P muke so ku zo, ga jam’iyya mu sa ta a zuciya

Al’ummar Nijeriya.

Zango na uku na jamhuriya ta huɗu kuwa ya soma ne a shekarar 2007 ya kuma ƙare a shekarar 2011. Wannan ne ya samar da jam’iyyun masu yawa a wannan ƙasa, kamar irin su A.N.P.P, P.D.P, D.P.P, C.P.C da yake a wannan lokaci jam’iyun A.N.P.P da P.D.P suna da marubuta waƙoƙinsu da suke da su tun farko, marubuta waƙoƙin siyasa sun yo ca, gun waƙe sababbin jam’iyyu, kamar irin jam’iyyar C.P.C da D.P.P. Fitattu daga ciki sun haɗa da Auwwal Gwammaja da S.Y. Rigacukum da makamantansu.

Auwal Gwammaja ya samar da fitattu waƙoƙi biyu na jam’iyyar D.P.P waɗanda ke ƙunshe da jan hankalin jama’a da bayyana manufofin jam’iya zuwa ga jama’a, waƙar farko tana da amshi kamar haka:

Mu mun yi na’am da maraba,

Da saukar jam’iyyar nan,

D.P.P ta burge ni,

Yau ita ni zan zaɓa,

Don na yaba kyan halinta.

Sai kuma waƙa ta biyu mai amshi kamar haka:

Mu ba gaba muka zo ba,

Alheri mu muka kawo,

D.P.P alheri ce,

Kowar rasa ta a je mishi jaje.

Sai waƙar S.Y Rigacukum wadda ya yi wa jam’iyyarsa ta C.P.C mai amshi kamar haka: 

Mu mun koma jam’iyyar Buhari,

Mai alƙalamin da bai rubita ƙarya,

C.P.C taimako ga kowa.

Waƙoƙin da aka samar na jam’iyyun siyasun wannan ƙarni na ishirin da ɗaya sun kasance da ire-iren waɗannan fuskoki da aka ambata, ma’ana wasu daga cikin rubutattun waƙoƙin an gina su ne da manufar koɗawa da wasa jam’iyyu, yayin da wasu marubuta waƙoƙin suna yi wa wasu muhimman mutane ko kuma ‘yan takarar jam’iyyu.

Su dai waɗannan waƙoƙin na koɗawa da kambama jam’iyyu akan yi ƙoƙarin wasa jam’iyya tare da fifita jam’iyya a kan sauran jam’iyyu. Su kuwa rubutattun waƙoƙin da ake yi wa wasu shuwagabanni ko ‘yan takara, akan yi ƙoƙarin kamanta adalcinsu da riƙon amanarsu da kwatanta gaskiyarsu, da kuma siffanta su da kyawawan halaye da mutunci da dattaku tare da bayyana wa masu zaɓe alfanun da ke tattare da zaɓen waɗannan shugabanni.

Jigon Waƙoƙin Ƙarni Na 20 Da Na Ƙarni Na 21

Yahaya (2016), ya nuna jigo shi ne saƙo ko manufa ko bayani ko ruhin da waƙa ta ƙunsa wanda kuma shi ne abin da waƙar ke son isarwa ga mai sauraro ko mai karatu ko mai nazari. A nan za a yi ƙoƙarin bayyana jigogin waƙoƙin ƙarni na ishirin (20) da na ishirin da ɗaya (21).

Zuwan Turawan mulkin mallaka ya yi sanadiyyar wasu daga cikin Hausawa suka fara tunani a kan sha’anin duniya. Irin wannan tunani shi ya kawo wasu marubuta da yawa a ƙarni na ishirin, suka rubuta waƙoƙi a kan wani jigo na sha’anin duniya, kamar siyasa ko wasu baƙin abubuwa, kamar mota, basukur da sauransu.

Wani marubucin waƙa da ya fara kawo canji a cikin waƙoƙin ƙarni na ishirin, shi ne, Sarkin Zazzau Aliyu Ɗansidi, ƙasaitaccen malami ne, masani kuma mai aiki da sani. Ya rubuta waƙoƙi da yawa kan sha’anin addini, kamar waƙarsa ta Mu Sha Falala. Ya kuma rubuta wasu waƙoƙi kan sha’anin duniya, kamar waƙarsa ta Nazmu Amir Za-zak. An ce ita wannan waƙa ya rubuta ta ne a lokacin da hanyar jirgi ƙasa ya iso Kano. Domin murnar wanna abu, sai aka kira babban taron dukkannin sarakunan Arewacin Nijeriya a Kano. Gwamna Janar Lugard shi ya jagoranci wannan taro, to bayan gama wannan taro da Sarkin Zazzau ya koma gida ya tsara wannan waƙa, wadda a cikin ta ya bayyana yadda ya zo Kano daga Zariya da yawan sarakunan da suka zo taro, da abubuwan sha’awa da sarakuna suka zo da su, da kuma abubuwan mamki da ya gani a Kano, da sunayen unguwannin birnin Kano, da kuma labarin wata sukuwar dawaki da aka yi a taron da kuma waɗanda suka ci sukuwar. Ita wannan waƙa kusan duniya ce tsantsa babu abin da ya haɗa jigonta da addini. Kusan kuma wannan waƙa ita ce farkon rubutacciyar waƙar da aka yi ba kan sha’anin addini ba, tun bayan wucewar jihadin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo.

Wani misali, wani mawaƙi da ya biyo bayan Sarkin Zazzau shi ne Alhaji Aliyu Namangi. Shi kuwa wani makaho ne malami, taƙiyi, mutumen Zariya ya rubuta waƙoƙi da yawa kan sha’anin addini, musamman waƙarsa da fi fice a duniya ta Imfiraji mai juzu’i ɗaya zuwa tara. Ya rubuta wasu waƙoƙi guda biyu masu ɗauke da jigon duniya wato, waƙar basukur da waƙar ƙazama. Gaba ɗaya dai, daga shigowar ƙarni na ishirin sai jigon waƙa ya fara canzawa, daga waƙoƙi masu jigon addini tsagwaronsu, zuwa waƙoƙi masu jigon addini da duniya.

A farkon ƙarni na ishirin yawancin waƙoƙin addini sun kasance ne, ko dai yabon waliyai ko malamai, misalin waɗannan waƙoƙi su ne waƙoƙin Gangar Wa’azu da Waƙoƙin Bagauda ta Kano da waƙar Mu Sha Falala ta Sarkin Zazzau Aliyu Ɗansidi da sauransu. Waƙoƙin yabo a farkon ƙarni na ishirin su ne, waƙar Imfiraji ta ɗaya da waƙar Tusamma Aibatul Fuƙara na Aliyu Namangi da waƙar yabon Shehu Tijjani wadda Shehu Atiku Kano ya yi, da kuma wasu waƙoƙi da yawa da aka yi don yabon Annabi Muhammadu (S.A.W).

An samu wanzuwar rubutattun waƙoƙin siyasa a ƙasar nan tun farkon samuwar jam’iyyun siyasa, wato tun daga jamhuriya ta farko har zuwa yau. Yin amfani da waƙoƙin siyasa a wanan ƙasa na ɗaya daga cikin matakan da jam’iyyu ke ɗauka na tallata manufofinsu da kuma ‘yan takararsu zuwa ga jama’a masu zaɓe domin neman goyon bayansu.

Su kuwa waƙoƙin ƙarni na 21 sun sha bamban da na ƙarni na 20 ta fuskar jigo. Manyan jigogin da suka yi fice a cikin waƙoƙin wannan ƙarni na 21 su ne jigon soyayya da yabon Annabi da kuma na siyasa, wannan ya samu ne sakamakon shigowar finafinan Hausa inda aka samu mutane da yawa suka riƙa rubuta waƙa ana sawa a cikin fina-finai, domin ƙara masu armashi. Mawaƙa irin su Mudassir Ƙasim da Sadi Sidi Sharifai da Maryam A. Baba da Yakubu Muhammad da Yusuf Ayagi sun bayar da gudummowa wajen samar da waƙoƙin fina-finan Hausa. Misali: Yakubu Muhammad ya rubuta waƙa mai suna “Oh! Dizan-Dizan” a cikin wani fim mai suna NADAMA inda shi da Rabi Mustafa ke rerawa, Ali Nuhu da Abida Muhammad ke bibiyan waƙar (mamin) wato suke bin sautin faifan. Ga yanda waƙar take:

Soyayya da shi nake,

Tun asali da ni yake,

Na kama ku kun fake,

Kin biya ta ƙarƙashin ƙasa kina sheɗana.

Zubi Da Tsarin Rubutattun Waƙoƙin Ƙarni Na Ishirin (Ƙ.20) Da Na Ƙarni Na Ishirin Da Ɗaya (Ƙ.21)

A nan za a yi ƙoƙarin kawo bambance-bambancen da ke tsakanin waƙoƙin ƙarni na ishirin (20) da kuma ƙarni na ishirin da ɗaya (21) kamar haka:

Marubuta waƙoƙin ƙarni na ishirin yawancin su malamai ne na addini ko da sun yi boko za a samu sun yi karatun fiƙihu a gida. Misali irin Sa’adu Zungur, mahardacin Alƙur’ani ne. Haka ma marubuci Malam Aƙilu Aliyu malami ne na addini da ajami yake rubuce-rubucen waƙoƙinsa da sauransu.

Marubuta waƙoƙin wannan ƙarni na ishirin da ɗaya suna amfani da kayan kiɗa baƙi, ko amshi, ko taɓi da rawa da karɓa kamar yadda Kabiru kilasik ke yi, wanda ya saɓawa rubutacciyar waƙa, wanda marubuta waƙoƙin ƙarni na ishirin ba su amfani da waɗannan kayan kiɗa da amshi a waƙa, sai ɗan abin da ba a rasa ba.

Marubuta waƙoƙin ƙarni na ishirin da ɗaya suna zuwa wani ɗaki da ake rera waƙa (studio) suna rera waƙa daga su sai makaɗan sutudiyo da ‘yan amshi, su ba shi kiɗa, su daidaita masa waƙa da kiɗa, saɓanin marubuta waƙoƙin ƙarni na ishirin, wanda tun daga jamhuriya ta farko har zuwa ta biyu sai dai su rera waƙoƙinsu wurin yaƙin neman zaɓe ko wani dandali da suke zama.

Mawaƙan ƙarni na ishirin da ɗaya kamar maroƙa suke, waƙa suke ba jam’iyya ba, sun fi mayar da hankali wurin yi wa ‘yan takara waƙa, ko kuma idan ya nemi wani abu bai samu ba sai ya koma wata jam’iyya, misali irin Aminu Ibrahim Ɗandago ya yiwa ɗantakar jam’iyyar DPP Alhaji Abubakar Gari Malam na jihar Kebbi waƙa a lokaci guda kuma ya yi wa Aliyu Magatarda Wamakko na jam’iyyar PDP waƙa a shekara ta 2007, saɓanin marubuta waƙoƙin ƙarni na ishirin ‘ya’yan jam’iyya ne masu aƙidarta. Misali kamar Shekara Sa’adu ko Muhammadu Giɗaɗo ko Lawan Maiturare ko Gambo Hawaja, jam’iyya kawai suke yi wa waƙa ba yantakara ba.

Haka ma, mawaƙan ƙarni na 20 sai buƙatar yin waƙar ya taso suke tsara waƙa, su kuwa mawaƙan ƙarni na 21 ko ba a hanya su yin waƙar ba za su tsara su rera domin kawai a san da su ko don samun abin duniya

Ana samun wasu daga cikin marubuta waƙoƙin ƙarni na 21 sun zama jemagu, kowa suna yi wa waƙa, da ɗan jam’iyyarsu da wanda ba ɗan jam’iyyarsu ba, wanda ba a samun haka a cikin mawaƙan ƙarni na 20.

Kwaɗayi da neman abin duniya ya yi wa marubuta waƙoƙin ƙarni na 21 yawa, saɓanin marubuta waƙoƙin ƙarni na 20.

Marubuta waƙoƙin ƙarni na 21 sun mayar da waƙa sana’a kuma abin dogaro, saɓanin mawaƙan ƙarni na 20.

ƙarni na 21 ana amfani da salon barbaranyayawa. Sai ka ga mawaƙi ya rubuta waƙa kowane baiti yana ɗauke da layuka goma ko ma fiye da haka.

ƙarni na 21 aka samu rubutattun waƙoƙi da salon karɓa-karɓa a cikin waƙa, kuma kusan a ce a cikin kowane baitin waƙa, kamar yadda Kabiru Kilassic ke yi. Amma a ƙarni na 20 mutum guda ke waƙarsa har ya ƙare.

Ana samun luguden nassi a cikin waƙoƙin ƙarni na 20, amma mafi yawan waƙoƙin ƙarni na 21 ba a samun wani abu mai kama da haka.

Mawaƙan ƙarni na 20 ba su kiran sunayen mutane suna zagi, sai dai su yi zambo da habaici, amma mawaƙan ƙarni na 21 suna kiran sunan mutum ƙarara, kamar yadda Aminu Dumbulun ya yi a cikin waƙarsa ta sai an canza.

Mawaƙan ƙarni na ishirin suna bin ƙa’idojin rubutacciyar waƙa, ta hanyar yi la’akari da fara waƙa da rufewa da marufi da yawan layuka da da samar da jigo.

Mawaƙan ƙarni na ishirin da ɗaya ba yanboko ne zalla ba, wasu daga cikinsu ma ko bokon ba su yi ba, fasaha ce kawai ta waƙa suke da ita wajen waƙa. Idan har sun yi karatun addini to ba zai kai irin mawaƙan ƙarni na ishirin ba.

Mawaƙan ƙarni na ishirin da ɗaya ba su damu da buɗa waƙa da addu’a kamar mawaƙan ƙarni na ishirin ba.

Salon Sarrafa Harshe

Idan aka ce salo, ya ƙunshi abubuwa da ake so kowace waƙa ta same su. Daga ciki akwai salon sarrafa harshe. Ga ta yadda waƙoƙin ƙarni na 20 da na ƙarni na 21 suka sha bamban.

Mawaƙan ƙarni na 20 sun naƙalci harsuna biyu ko ma fiye da hakan. Misali yadda Sa’adu Zungur yake ɗaukar nassi na Alƙur’ani ko Hadisi ko Fiƙihu ya sarrafa shi cikin waƙa ba a cika samun haka ba a cikin waƙoƙin ƙarni na 21 ba. Haka shi ma Malam Aƙilu Aliyu da Shekara Sa’adu suke yi da sauransu.

Mawaƙan ƙarni na 20 ba su cika aron kalmomi da sarrafa su daga harshen Larabci ba sai dai harshen Turanci

Ƙoƙarin zaƙulo tsofaffin kalmomi a juya su cikin hikimar waƙa da fito da manufar harshe.

Su kuwa waƙoƙin ƙarni na 21 waƙoƙi ne da ake gudanar da su a wannan zamani wanda salon su ya sha bamban da sauran rubutattun waƙoƙi ta fuskar aiwatarwa da wannan ya faru ne sakamakon shigowar fina-finan Hausa

Kamanci Da Bambancin Waƙoƙin Ƙarni Na 20 Da Na 21

Waɗannan rukunin mawaƙa sun sha bamban ta wajen jigo da zubi da tsari da salo. Haka ma, wuraren da suka yi kama da juna.

Sun yi kama ta wajen shirya waƙa don isar da saƙon jam’iyya ko ɗantakara.

Sun yi kama ta wajen ƙafiya. Misali a waƙar Malam Gambo Hawaja wanda mawaƙin siyasa ne na ƙarni na 20 da kuma waƙar Aminu Ibrahim Ɗandago mawaƙin siyasa na ƙarni na 21. A cikin waƙar Malam Gambo Hawaja “Waƙar NEPU Sawaba Maƙiya Turawa” ga misali a baitin farko na waƙar:

Ta’ala ka ban taimako kan mu,

Ka maishe mu kayin magautan mu,

Ka kawo sawaba ƙasashen mu

Ka sa talakawa su zaɓe mu

Ka maishe mu ‘ya’ya kamar kowa

A wannan baiti na waƙa da ya gabata Malam Gambo Hawaja ya samar mata da ƙafiya guda biyu, ƙafiya ta ciki da kuma ƙafiya ta waje. Kowane baiti yana da ɗango biyar, ɗango huɗu na farko suke ɗauke da ƙafiyar ciki wanda ɗango na biyar ke ɗauke da ƙafiyar waje, ƙafiyar ciki a wannan baiti ita ce, Ma, sai kuma ƙafiyar waje ita ce Wa, wannan ƙafiyar ta waje kowane baiti na waƙar tun daga farko har ƙarewa da ita za a yi amfani, ita kuma ƙafiyar ciki takan canja daga baiti zuwa baiti. Sai misali a cikin waƙar Aminu Ibrahim Ɗandago ta “Adon gaskiya”:

Bismillahi Jalla gwani na,

Haliƙi mai dare mai rana,

Bani iko ka gyara shiri na,

In yi waƙa ga zakin fama.

Duk waɗannan misalai da aka kawo sun yi kama ta fuska ƙafiya, kowace waƙa daga ciki tana ɗauke da ƙafiya ta ciki da ta waje.

Dukkanninsu da sigar waƙa suke gabatar da jigoginsu. Misali, waƙar Auwalu Isah Bunguɗu wanda mawaƙi ne na ƙarni na 20 a cikin waƙar da ya yi wa Malam Aminu Kano da kuma waƙar Aminu Ibrahin Ɗandago wanda ya rera waƙar “Adon Gaskiya” wadda ya yi wa ɗan takarar gwamnan jihar Sakkwato a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a shekara ta 2007. Duk waɗannan waƙoƙin jigonsu na tallata ɗan takara ne, ba jam’iyya ba, ga misali daga cikin waƙar Awwalu Isa Bunguɗu da ya yi wa Malam Aminu Kano:

Ni na bi Aminu Kano masoyi na,

Tawa siyasa nan na koyi

Ka Musulunci nan nake yi

Don haka bani biyar mashayi

Don ni ba zan sha giya ba.

Sannu aminu da fama

Ni dai yau murna nake ma

Yanzu duk ƙasa ta yaba ma

Dubi Imodu yana yaba ma

Bai san ƙoshin lafiya ba.

Sai misali na biyu daga cikin waƙar Aminu Ɗandago waƙar “Adon Gaskiya”:

Sarkin yamma albishirinka,

Sakkwatawa suna bayanka

Sun kasance suna ra’ayinka

Sun yada hauni sun riƙe dama.

A wani baiti kuma yana cewa:

Sakkwatawa ku bar tababa,

Ali wallahi shi ne a gaba,

Dole maƙiyinka sai ya tuba,

In ya ƙi ya je ya taka kunama.

Waɗannan waƙoƙi da aka ba da misalai da su, waƙoƙi ne da aka samar a lokuta mabambanta, amma kuma duk sigar jigo ɗaya suke ɗauke da shi wato jigon tallata ɗan takara.

Kammalawa

Wannan nazari ya yi dubi ne game da waƙoƙin ƙarni na 20 da jigoginsu da ƙarni na 21 da jigoginsu, kuma wannan nazari ya taɓo bayani akan waƙoƙin siyasa na ƙarni na 20 zuwa ƙarni na 21 tun daga jamhuriya ta farko har zuwa wannan jamhuriyar da muke ciki, tare da misalai. Haka kuma a cikin wannan bincike an kawo bambance-bambance da ke tsakanin waƙoƙin ƙarni na 20 da ƙarni na 21.

Manazarta

Ɗanillela, A. (2010), Rubtattun waƙoƙin siyasa: Nazari a kan jihohi Sakkwato da Kebbi da Jihar Zamfara. [Kundin Digiri Na Biyu]. Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sokoto.

Birniwa, H. A. (1987), Conserɓatism and dissent: A comparatiɓe study on N.P.C/N.P.N And N.E.P.U/P.R.P., Hausa political ɓerse from circa 1946-1984. [Kundin Digiri Na Uku]. Sashen Harsunan Nijeriya. Jami’ar Usman Ɗanfodiyo, Sakkwato.

Yahya, A. B. (2016). Salo asirin waƙa. Guaranty Printers.

 Yobe Journal

Post a Comment

0 Comments