Ticker

6/recent/ticker-posts

Dabarar Bayar Da Labari: Nuna Kawaicin Mawallafiya A Wasu Littattafan Kagaggun Labaran Hausa Na Balaraba Ramat Yakubu

Citation: Prof. Balarabe Zulyadaini and Yusufu Suleiman Ph.D (2022). Dabarar Bayar Da Labari: Nuna Kawaicin Mawallafiya A Wasu Littattafan Ƙagaggun Labaran Hausa Na Balaraba Ramat Yakubu. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 10, Number 1. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660

DABARAR BAYAR DA LABARI: NUNA KAWAICIN MAWALLAFIYA A WASU LITTATTAFAN ƘAGAGGUN LABARAN HAUSA NA BALARABA RAMAT YAKUBU

Na

Prof. Balarabe ZULYADAINI

Yusufu SULEIMAN Ph.D

Tsakure

A wannan binciken an yi ƙoƙarin fito da wata dabarar bayar da labari da Hajiya Balaraba Ramat Yakubu ta yi amfani da ita, wajen nuna kawaici a cikin littattafan Budurwar Zuciya da Alhaki Kuykuyo Ne da kuma Matar Uba Jaraba. A cikin binciken an gano dalilan da suka saka aka sami kawaicin mawallafiyar a cikin labaran waɗanda suka haɗa da: jaddada labari, da rage nisa tsakanin mai karatu da mawallafiya, da kuma ƙyale mai karatu ya zantar da hukunci da kansa, dangane da wasu maganganu da aka fara, amma ba a ƙarasa su ba, a cikin labari. 

Gabatarwa

Yawancin marubuta ƙagaggun labaran Hausa akan same su da nuna kawaici a lokacin da suke rubuta ƙagaggun labarai, musamman waɗanda suke rubutu cikin harshen Hausa. Wannan ba ya rasa nasaba da yadda al’adun Bahaushe na jin kunya da kawaici suka tasiri a cikin rayuwarsa. Kowa ya san Bahaushen mutum wajen kawaici, musamman domin ya kare mutuncinsa da al’ummarsa. Shi kawaici yakan yi wa mai yin sa rana, domin mai yin sa akan ji kunyarsa a kan abubuwa da yawa. Idan ma ba domin jin kunya ba, ai yakan taimaka wajen taƙaita aukuwar fitintinu a tsakanin al’umma.

Ma’anar Kawaici

 Kawaici kalma ce da ake amfani da ita domin a bayyana kaucewa daga barin wani abu bisa wasu dalilai. An bayyana ma’anar kawaici ta hanyoyi guda biyu kamar yadda aka nuna a Ƙamusun Hausa cewa, “(i) Alkunya ko kau-da-kai da kuma (ii) haƙuri ko shiru-shiru,” (CNHN, 2006, sh. 241).

Shi kuma Mukhtar, (2004, sh. 53) ya bayyana ma’anar kawaicin mawallafi da cewa:

“Abin da ake nufi da kawaicin mawallafi shi ne, a cikin labari inda shi mawallafin yakan yi shiru da zance sannan ya bar mai karatu tare da wani tauraro wanda zai faɗi labarin kai tsaye, a kan abin da ya shafi shi tauraro ɗin. A wani lokacin kuma kawaicin mawallafi yakan bayyana idan ya yi shiru da wani zance a cikin labarin ya ƙi faɗa ko ya ƙƙarasawa, ko ya ƙi fara labarin da wannan zancen, domin dai kawai ya bar mai karatu ya cikasa da kansa.”

Daga waɗannan ma’anoni guda biyu, za a iya cewa a ma’ana ta adabi, kalmar kawaici na nufin kawar da kai daga barin wani zance ko al’amari saboda wasu daliliai. Wannan ya nuna cewa lallai a cikin ƙagaggen labari ana samun yadda mawallafi ke barin wani zance domin ya nuna kawaicinsa. Hausawa sukan ce “ruwa ba ya tsami banza.” Wato a duk lokacin da aka sami kawaicin mawallafi ba a rasa dalili. Wannan shi ne abin da za a duba nan gaba, sannan a fito da wasu misalai na yadda mawallafiyar littattafan ta nuna kawaicinta.

Dalilan Da Kan Sa A Sami Kawaicin Mawallafa

 Kamar yadda aka bayyana a sama, lallai mawallafin ƙagaggen labari yakan nuna kawaici a cikin labari. Wannan ya nuna cewa ita ma wannan mawallafiyar (Balaraba Ramat Yakubu), ba a bar ta a baya ba wajen nuna irin wannan kawaici. Haka zalika takan nuna kawaicin ne saboda wasu dalilai na aiki da dabarun bayar da labari kamar yadda yake a cikin bayanin da ke biye.

Domin Jaddada Labari

 Kalmar jaddada na nufin “Ƙarfafa abu, musamman magana,” (C.N.H.N, 2006, sh. 210). A cikin aikin bayar da labari, wasu mawallafan kan nuna kawaici domin jaddada labari. Wannan yakan faru ne a lokacin da mawallafi ya kauce wa bayar da labari na kai tsaye daga bakinsa. Wato yakan ƙyale ɗaya daga cikin taurarin ne ya bayar da labarinsa da kansa domin ya sami jaddada dangane da labarin, (Mukhtar, 2004, sh.53).

 A cikin littafin Budurwar Zuciya, an sami kawaicin mawallafiyar domin a nuna jaddadawa game da labarin. Wato a lokacin da Alhaji Usman ya kai matansa unguwar Kurnar Asabe, inda ya gina sabon gida, sannan ya ce Kyauta ta ɗauki gini mai ɗakuna biyu da falo a tsakiya. Ita kuma Asama’u aka bar mata ɗaki ɗaya da falo kawai. Domin a nuna jaddadawa a cikin labarin, sai mawallafiyar ta miƙa wa ɗaya daga cikin taurarin, wato Asama’u, ragamar bayar da labarin, inda take cewa:

“Malam ni ba na son wannan ɗakin. Yaya ni mai ‘ya’ya biyar za ka ba ni ɗaki ɗaya da falo, ita mai ‘ya’ya uku za ka ba ta ɗaki biyu har da falo da banɗaki. Wato ni ba mace ba ce, ko kuwa ta fi ni ne? In haka ne, to ni ka bar ni a wannan gidan, ita ka tare da ita a sabon gidan.” (Yakubu, 1987, sh. 5).

 A nan an sami jaddadawa dangane da labarin domin Asama’u ce da bakinta take bayyana matsayarta game da rabon ɗakunan da Alhaji Usman ya yi. To a nan mai karatu ya ji daga bakin tauraruwar cikin labarin, kuma wadda abin ya shafa kai tsaye. Idan da a ce mawallafiyar ce ta ba da labarin abin day a faru tsakanin Alhaji Usman da Asama’u, da ba a sami jaddadawar da ake tsammani ba.

 Idan aka duba cikin littafin Alhaki Kuykuyo Ne mawallafiyar ta nuna kawaici domin samun jaddadawa a cikin labarin. An sami haka ne a lokacin da ake rikici tsakanin Rabi da kishiyarta Delu da kuma mijinsu Alhaji Abdu. A lokacin da mawallafiyar take bayar da labarin, sai kuma ta saki labarin a hannun taurarin domin a sami jaddadawa game da labarin, inda Rabi take cewa:

“Ni na wuce banza a banza.” Ta miƙe a tsaye ta ci gaba da cewa, “’Yar iska ragowar ‘yan gwangwani. Kin samu ya rufa miki asiri, ya auro ki. Shegiya komaɗaɗɗiyar wofi. Ai shi ne ya ɗaure miki gindi, don haka kike ɗaukar mutane banza. To na gaji wallahi. Idan kika ƙara yi mini wata magana, ubanki za ki ci a gidan nan.” (Yakubu, 1990, sh. 34).

 A nan ma mai karatu ya ji daga bakin taurauwar da abin ya shafa kai tsaye ne, ba daga bakin mawallafiyar ba. Wannan ya nuna cewa lallai mawallafiyar ta nuna kawaici a cikin labarin domin a sami jaddadawa dangane da labarin. Ita kuka Rabi da abin ya shafa kai tsaye, ta ba wa maikaratu labarin kanta da kanta yadda ta nuna cewa ita ba banza ce ba a gidan Alhaji Abdu.

 Idan kuma aka duba labarin cikin littafin Matar Uba Jaraba, za a sake samun yadda mawallafiyar ta nuna kawaici a cikin labarin domin a sami irin wannan jaddadawa da ake magana a kanta. A lokacin da aka dawo da Daso daga asibiti, bayan likita ya tabbatar musu da cewa ciwon Daso ba na asibitinsu ba ne. Ana riƙe da Daso, tana tafiya, tana surutai har ta yi tuntuɓe da mesar ban ruwan filawa. Daga nan sai ta yi tangal-tangal za ta faɗi, sai Ladidi ta yi sauri ta kama ta, ita kuma sai ta ce:

“Kada ki sake riƙe ni, kin ƙwace mini fada a gurin mijina sai na rama…. zan koma gurin malam…. Hussaini ɗin ma sai na saka shi uwa duniya, kamar yadda na ɓatar da Hassan ɗin naku…. Shi ma sai na ɓatar da shi.” (Yakubu, 2006, sh. 123).

 Idan aka lura a nan za a fahimci cewa mawallafiyar ta yi kawaici yayin da ta bar tauraruwar take bayyana kanta da kanta. Daso ce ke bayyana wa Sa’idu da Ladidi irin abubuwan da ta aikata da kanta. Kasancewar bayanan sun fito daga bakin wadda abin ya shafa kai tsaye, sai aka sami irin jaddadawar da ake tsammani. Da mawallafiyar ba ta saki ragamar bayar da labarin a hannun tauraruwar ba, ai ka ga da jaddadawar ba ta samu kammar yadda ya kamata ba. Wato a nan ta bayyana abubuwan da suka faru da kuma irin hanyoyin da ta bi har aka sami aukuwar wasu munanan abubuwa kamar mutuwar Ummi da yadda Hassan ya shiga uwa duniya. Saboda haka a nan mawallafiyar ta bar mai karatu ya ji daga bakin wadda abin ya shafa.

Rage Nisa Tsakanin Mai Karatu Da Mawallafiya

 A cikin harkar karanta ƙagaggen labari akan sami yadda mai karatu ke tarar da mawallafi ya kauce daga aikin bayar da labarin. Shi mawallafin yakan yi haka ne domin ya rage nisan da ke tsakaninsa da mai karatu. Don haka a nan sai shi mawallafin ya jawo mai bayar da labari daga cikin fage ya haɗa shi da mai karatu. Shi kansa tauraron da ke bayar da labarin, kan sami rakiyar mawallafin. Abin lura a nan shi ne, wani lokaci idan mai karatu na jin labari daga bakin mai bayar da labari daga cikin fage, sai mawallafi ya sako maganarsa domin yi wa mai ba da labari daga cikin fage rakiya, (Mukhtar, 2004, sh. 54-56).

 A wasu lokutan mawallafiyarwaɗannan littattafan ƙagaggun labaran Hausa da ake magana a kansu, kan koma gefe ɗaya, ta bar mai karatu tare da mai bayar da labari daga cikin fage. Ba shakka takan yi haka ne domin ta rage irin nisan da ke tsakaninta da mai karatun. Akwai wasu misalai daga littattafan Budurwar Zuciya da Alhaki Kuykuyo Neda Matar Uba Jaraba na yadda mawallafiyar ta sakar wa mai ba da labari daga cikin fage. A cikin littafin Budurwar Zuciya an sami misali kamar haka:

“Sai Alhaji ya ce a’a kada ya tafi. Yana son ya yi shawara da shi. Shi ke nan ya sake zama. Alhaji ya ce da shi, “Yanzu yaya ka ga zan yi da yaran nan? Abin nasu fa ya yi yawa. Har ma ni na rasa abin da zan ce.” (Yakubu, 1987, sh. 31).

 Idan kuma aka duba cikin littafi Alhaki Kuykuyo Ne akwai wani misalin kamar haka:

“An fi minti goma sha biyar kafin Alhaji Abdu ya fito wurin masu sallama da shi. Ya fita kuwa a murtuke, fuskarsa a ɗaure kamar sun zo roƙon gafara a gunsa. Suka dai kanne, suka rabu da shi. Bayan sun gama gaisawa, sai Alhaji Bello yace da Alhaji Abdu, “Ɗazu ne Malam Shehu ya je gidana, ya gaya mani wata maganar da ban ji daɗinta ba. Don a kan faɗan mata, ai bai yi daidai a yi saki ba.”(Yakubu, 1990, sh. 38).

 Haka zalika idan aka sake duba labarin cikin littafin Matar Uba Jaraba an sake kawo wani misali na yadda mawallafiyar ta saki ragamar ba da labarin a hannun wani tauraro domin a rage nisan da ke tsakaninta da mai karatu kamar haka:

“Nan da nan malaman nan suka sami gangara a gurinta yayin da jarinta ya fara yin baya. Sai ta gaya musu, sai su ce, “Ai Ladidi ce take yi miki sammu, ai ƙara dagewa za mu yi.”(Yakubu,2006, sh. 52).

 Idan aka duba waɗannan misalai daban-daban guda uku, za a gane cewa mawallafiyar ceke yi wa taurari rakiya a cikin labaran. Daga nan kuma sai ta saki ragamar bayar da labaran a hannun taurarin. Wannan ya nuna cewa a lokacin da take yi wa taurao rakiya, tana rage irin nisan da ke tsakaninta da mai karatu ne. Wato tana nuna wa mai karatu cewa tana nan kusa da shi, ba ta yi nisa ba.

Daga waɗannan misalai za a gane cewa mai bayar da labari daga bayan fage kan yi shiru a wani lokaci, sannan ya ƙyale tauraro ya yi magana da bakinsa domin ya kusantar da shi ga mai karatu. Saboda haka a nan akan bar mai karatu ya ji kalaman daga bakin shi tauraron kai tsaye ba tare da wani ya shiga tsakani ba.

Ƙyale Mai Karatu Domin Zantar Da Hukunci Da Kansa

 Wani lokaci a cikin ƙagaggen labari akan sami ra’ayin mawallafi da na mai ba da labari ya zama iri ɗaya. Idan haka ta kasance, za a iya duba dangane da sirrin sadarwa wanda ke tsakanin mawallafi da mai karatu. Wannan ya nuna cewa irin wannan sadarwa kan faru ne ta bayan fage, wanda shi mai ba da labari daga cikin fage bai san abin da ke akwai ba, tsakanin mai karatu da mawallafi. Irin wannan ta fi faruwa musamman idan an bar mai karatu da wani tarƙoƙo a labarin kuma ana buƙatar ya warware abin da kansa. Haka kuma zai iya kasancewa ba tare da mawallafi ya faɗi ra’ayin da bakinsa ba. (Mukhtar, 2004, sh. 56).

 Idan aka duba za a ga cewa ƙyale mai karatu ya kwance ƙullin labari da kansa zai taimaka wajen bayyana ra’ayinsa game da labarin da kuma ra’ayinsa game da mawallafin shi kansa. An sami irin wannan kawaici na mawallafiyar a labarin cikin littafin Budurwar Zuciya, a lokacin da Ummi ta je Kantin Kwari domin yin magana da saurayinta da na ƙawarta Hadiza, wato Alhaji Ahmed da Alhaji Ahmadu. A nan ne Ummi ke bayyana saƙo ga wani mutum inda take cewa: “To, don Allah in sun zo, ka ce da su, Ummi ta yi musu waya, kuma ta ce….” (Yakubu, 1987, sh. 58).

 A nan an bar mai karatu ya yi tunanin sauran zancen da ita Ummi ba ta kawo ba. Wannan ya nuna cewa lallai akwai wani tarƙoƙo da ake so mai karatu ya warware da kansa. To, ai ka ga a nan rashin ƙarasa maganar yana nufin cewa an bar mai karatu ya yi ƙiyasi da kansa domin ya kawo cikon zancen da ya rage.

 Idan kuma aka duba cikin littafin Alhaki Kuykuyo Ne an sami irin wannan kawaici na mawallafiyar domin mai karatu ya yi hukunci da kansa dangane da zancen Alhaji Abdu na ƙwace Ladidi daga hannun Rabi domin ya ba wa Delu, inda ya fara da cewa: “Inna kin ga ita tana zaune babu kowa a gabanta, kuma a gaskiya in kin lura, za ki ga cewar, Ladidi wahala take sha a wurin….” (Yakubu, 1990, sh. 31).

 Wannan ya nuna cewa akwai sauran zance, don haka ana buƙatar mai karatu ya yi hukunci da kansa wajen fito da ra’ayinsa game abin da ya rage da ba a faɗa ba. Hukuncin da mai karatu ya yanke game da sauran zancen, shi ne zai kasance ra’ayinsa dangane da labarin. Wannan wata dabara ce ta bayar da labari domin a nuna yadda mawallafiyar ta yi kawaici a cikin labarin.

 Har ila yau an sake samun kawaicin mawallafiya domin ƙyale mai karatu ya yi hukunci da kansa game da zancen da aka fara amma ba a ƙarasa ba. A nan akwai Bilkisu ‘yar Alhaji Abdu, lokacin da take bayyana wa mahaifiyarta Rabi dangane da haɗuwar da ta yi da mahaifinta Alhaji Abdu, inda take cewa: “Wallahi ya gan ni. Abin da sai da muka haɗa ido da shi san….” (Yakubu, 1990, sh. 90).

 A cikin wannan zance an rage wani ɓangare, don haka ana buƙatar mai karatu ya kawo abin da yake jin cewa shi ne ya rage. A nan ma an yi kawaicin ne domin a ba wa mai karatu dammar yanke hukunci da kansa, ya fito da ra’ayinsa dangane da labarin.

 Wasu misalan shafukan da aka sami kawaicin mawallafiya don ƙyale mai karatu ya yi hukunci da kansa a cikin littafin Alhaki Kuykuyo Ne sun haɗa da:

“Ki yi haƙuri Hajiya, don na ga dare ya yi ne a lokacin shi….” Shf na 66

“Ke fa ba ki da kunya. Ki dake ta, kuma ki ce za ki yi wa mutane surutun banza me kike nufi ne? Ko….” Shf na 130

“Ba sai ka rama mata ba, da ita ‘yar mutane, ni ‘yar jakai, da ma ai kai ka ɗaure….” Shf na 130

“Alhaji Abdu ai sai haƙuri. Rumfarka kam, duk wannan layin ta ƙone. Wurin ma ba a iya isa, domin….” Shf na 140

“Delu, Delu ai na tsiyace. Delu rumfata da kayan ciki da kuma kuɗina wajen naira dubu sittin duk sun ƙone, motar tawa ita ma an sace. Yanda nake ɗin nan shi ken an Delu na….” Shf na 144

“Allahu Akbar in ji mai kiran sallah. Yau ni kam ai ban san abin da zan….” Shf na 149

“Ai Baba tun da nake aure ban taɓa samun matar arziki irin Saudatu ba, tun da ta zo nan gidan ban taɓa yi mata kasshedi sau biyu ba, duk abin da na ce ba na so to shi ke nan ta….” Shf na 151 

“Ai madalla ma Baba, Allah ya ƙara masa. Wallahi ni ba zan je asibiti don na gan shi….” Shf na 152

“Saude ce ta ce a kawo mani wannan kayan har da….” Shf na 156

“To tsaya mana ki ji ai maganar ba ta haka ba ce. Rabi ki tsaya….” Shf na 160

“Ka san yanzu likita ya zo ya ce ka daina ɓata ranka. Masu irin wannan ciwon ba a so su riƙa yawan….” Shf na 167

“Kome ya same ni ma, ai alhakinku ne. Alhaki kwikwiyo ne….” Shf na 167

“Yanzu ba ga shi ku ɗin ne a wurina ba. Naka ai komi lalacewarsa, shi ne naka. Don Allah don Annabi ku yafe mani. Ko da mutuwa zan yin a sami sauƙin wata azabar. Don Allah ku yafe….” Shf na 167

 Dukkan waɗannan misalan an tsakuro su ne daga shafuka daban-daban domin a nuna cewa akwai su da dama a cikin labarin. Kowane daga cikinsu idan an duba, za a ga cewa yana buƙatar mai karatu ya yi hukunci wajen kawo cikon zancen da ba a ƙarasa ba.

 An sake samun irin wannan kawaici na mawallafiyar a cikin littafin Matar Uba Jarabadomin a ƙyale mai karatu ya yi hukunci da kansa. Wannan ya faru ne a lokacin da Alhaji Sani yake tunanin yadda zai yi da yaron da ya tsinta, wato Hassan, inda yake cewa:

“To, wannan yaron yaya zan yi da shi? Ina zan kai shi? Duk inda ma na kai shi, cewa za a yi sato shi na yi. Tun da Kurmi za ni, sai kawai na tafi da shi tun da ba ya iya tuna komai, sai na canza masa suna. Tun da ni Allah bai ba ni haihuwa ba sai in riƙe shi kamar ni na haife shi, kuma….” (Yakubu, 2006, sh. 73).

 Alhaji Sani ya fara bayanin yadda zai yi da yaron da ya tsinta, domin yana tunanin cewa duk inda ya kai shi za a gane cewa ba ɗansa ne ba. Bayan yanke shawarar tafiya Kurmi da shi kuma ya riƙe shi a matsayin ɗansa, sai kuma ya yanke sauran zancen. A nan ana buƙatar mai karatu ya yi tunanin sauran zancen da Alhaji bai ƙarasa ba. To, ai ka ga a nan ma an bar shi mai karatun da wani tarƙoƙon da ake so ya warware da kansa.

Har ila yau a cikin littafinMatar Uba Jaraba, an sake samun irin wannan kawaici na mawallafiyar domin ta ƙyale mai karatu ya yi hukunci da kansa, a lokacin da Barmo ya raka Aminu Fanshekara, kumayake cewa:

“Ai ina da wata matsala ce, don Alhaji nawa yana asibiti tun jiya, to mun zo nan garinsu Fanshekara ni da Aminu, don mu gaya musu, shi kuma Aminu ya yi nan. Wai ya gane makarantar, shi ne ya bar ni a nan a tsaye ina….” (Yakubu, 2006, sh. 145).

 Wani lokaci akan sami kawaicin da ake yi wanda mai karatu ba zai sha wahalar yanke hukunci a kansa ba. Idan aka duba bayanin da Barmo ya yi, sannan kuma ya yanke sauran zancen da bai ƙarasa ba, za a gane yana so ne ya bayyana cewa yana jiran Aminu. Saboda haka ashe ana iya samun kawaici mai sauƙin yanke hukunci.

 Akwai misalai da dama a cikin labarin da ke nuna cewa akwai kawaicin da mawallafiya ta yi domin ta ƙyale mai karatu ya yi hukunci da kansa waɗanda suka haɗa da:

“Wallahi Abba na je Fanshekara neman dangin uwata domin….” (Yakubu, 2006, sh. 156).

“Ranka ya daɗe, a gaskiya dai to….” Shf na 39

“Ni dai na gaya muku rance-rancen nan naku ya yi yawa don….” Shf na 101

“In na je gida zan gaya wa Ummi cewar an ga wani mai kama….” Shf na 106

“Ni ma zan je na gan shi da safe, ni ai zan gane shi in….” Shf na 110

“Wallahi Abba na je Fanshekara neman sanin dangin uwata domin….” Shf na 156

“Aminu, ka je neman dangin…. Barmo kai ka ba shi wannan shawarar? Aminu ba na gaya….” Shf na 156

“Aminu ni kake gaya wa haka? Barmo dubi Aminu. Barmo….” Shf na 156

“Kai ne wannan yaron Aminu. Kai ba ɗana ba ne, ba ni na haife ka ba. Tsintarka na yi. Tsoron rabuwa da kai ne yake sawa kullum in ka yi maganar dangin uwarka, sai hankalina ya tashi, ba na son kowa ya san cewar ba ni na haife ka ba. Aminu ba na son na rabu da kai…. Aminu….” Shf na 166.

 Idan aka duba cikin littatafan da aka nazarta, za a ga cewa lallai mawallafiyar ta yi amfani da wannan dabara ce domin ta fito da maganganu mabambanta manufa. Haka kuma kawaicin na mawallafiyar zai ba da dama wa mai nazari ya fahimci cewa mawallafa sukan yi amfani da kawaici domin kawar da kansu daga wasu abubuwan da ke faruwa a cikin labarai kamar yadda aka gani. Dukkan maganganun da aka kawo a matsayin misalai an kawo su ne domin a nuna cewa akan yanke zantuka domin a kawar da kai, ko jin kunya ko kuma domin a nuna tsoro. Nuna tsoro ba laifi ba ne domin kowane ɗan’adam an halicce shi da tsoro tare da shi.

Kammalawa

 Daga waɗannan misalai da aka gani, za a fahimci cewa mawallafiyar ta yi kawaicin ne domin ta ba wa mai karatu damar yanke hukunci a kan waɗannan zantuka ko wani tarƙoƙon da ba a warware shi ba. Saboda haka wannan ma wata dabara ce da mawallafa ke amfani da ita wajen bayar da labari domin isar da saƙo ga mai karatu. An gano cewa mawallafiyar littattafan Budurwar Zuciya da Alhaki Kuykuyo Ne da Matar Uba Jaraba, ta yi amfani da wannan dabara ta kawaici domin barin mai karatu ya yi hukunci da kansa dangane da duk wata magana da aka fara, sannan ba a ƙarasa ba aka katse ta. Wannan zai ba shi damar faɗaɗa da kuma zurfafa tunaninsa dangane da al’amuran da suka faru a cikin labaran da aka nazarta.

Manazarta

C.N.H.N. (2006). Ƙamusun Hausa. Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya. Jami’ar Bayero.

Mukhtar, I. (1987). Bitar nazarce - nazarcen salo a cikin rubutu. Taron Ƙara wa Juna Sani, Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero.

Mukhtar, I. (1990). A stylistic study of Sulaiman Ibrahim Katsina’s Hausa, Noɓels. [Ph.D. Thesis]. Department of Nigerian Laguages, Bayero Uniɓersity, Kano.

Mukhtar, I. (1993). Yanayin ƙagaggun labarai na Hausa. Nazari A Kan Harshe Da Adabi Da Al’adu. Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Mukhtar, I. (2001). Al’amuran dubawa cikin fasalin nazarin ƙagaggen littafi. Algaita Journal of Current Research in Hausa Studies. Ɓol. 1No. 1

Mukhtar, I. (2004). Jagoran nazarin ƙagaggun labarai (Tsari na biyu). Benchmark Publishers

Mukhtar, I. (2010). Introduction to stylistic theories, practice, and criticisms. Country side Publishers.

Suleiman, Y. (2005). Nazarin Dabarun Bayar Da Labari A Littattafan Dare Ɗaya Da Budurwar Zuciya. [Kundin digiri na biyu],.Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Suleiman, Y. (2019). Dabarun Bayar Da Labarai A Wasu Littatafan Balaraba Ramat Yakubu. [Ph.D Thesis]. Depertment of Nigerian Languages. Usmanu Ɗanfodiyo UniɓersitySokoto.

Yakubu, B. R. (1987). Budurwar zuciya, Gaskiya Corporation.

Yakubu, B. R. (1990). Alhaki kwikwiyo ne, Gaskiya Corporation.

Yakubu, B. R. (2006).Matar uba jaraba. Ramat General Enterprises.

 Yobe Journal

Post a Comment

0 Comments