Goyon baya a yaƙi yana babi ne na "wala'i da bara'i". Wato babin jiɓinta; soyayya da taimako da nuna goyon baya ga wanda ya cancanci hakan, wato "Wala'i" kenan, da kuma akasin haka, wato a barranta daga wanda ya cancanci hakan, wannan shi ne "Bara'i".
To shi "Wala'i"
ana yinsa ne ga Muminai zallah. Shi ya sa Allah ya ce:
﴿وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ
وَٱلۡمُؤۡمِنَـٰتُ بَعۡضُهُمۡ أَوۡلِیَاۤءُ بَعۡضࣲۚ﴾ [التوبة ٧١]
{Muminai maza da muminai
mata sashensu majiɓinta sashe ne (wato masu son
juna ne, da taimakon juna)}.
Shi kuma "Bara'i"
asali ana yinsa ne ga kafirai, sawa'un kafiran asali, ko munafukai da zindiƙai.
Sai kuma sauran masu saɓon
Allah, na fasiƙanci ko bidi'a, su ma
ana barranta daga gare su, amma bai kai na kafirai ba.
Da wannan za mu fahimci
cewa; kwata-kwata Musulmi ba zai goyi bayan kafirai ba. Don haka a wannan yaƙin da yake gudana a yanzu, bai halasta
Musulmi ya goyi bayan Amerka da Izraila ba.
To amma Iran kuma fa, shin
za a goyi bayanta, tun da Rafidha suna cewa; su ma Musulmai ne?
To, ita Iran ba za a goyi
bayanta ba, saboda dalilai guda biyu:
1- Saboda Rafidha ƴan Shi'a suna da bidi'o'i na kafirci.
Wato su ba Muminai ba ne, saboda Aƙidunsu
na kafirci, kuma su ba kafiran asali ba ne.
To bisa ƙa'ida; duk wanda ba Mumini ba ne, kuma
ba kafiri ɗan asali ba ne, to munafuki ne zindiƙi.
Don haka dukkan ƴan bidi'a masu Aƙidu na kafirci, zindiƙai ne. Zindiƙi kuwa, hukuncinsa hukuncin munafuki ne.
Ibnu Taimiyya ya ce:
"أَهْلُ
الْبِدَعِ فِيهِمْ الْمُنَافِقُ الزِّنْدِيقُ، فَهَذَا كَافِرٌ، وَيَكْثُرُ مِثْلُ
هَذَا فِي الرَّافِضَةِ وَالْجَهْمِيَّة، فَإِنَّ رُؤَسَاءَهُمْ كَانُوا مُنَافِقِينَ زَنَادِقَةً. وَأَوَّلُ
مَنْ ابْتَدَعَ الرَّفْضَ كَانَ مُنَافِقًا. وَكَذَلِكَ التَّجَهُّمُ فَإِنَّ
أَصْلَهُ زَنْدَقَةٌ وَنِفَاقٌ. وَلِهَذَا كَانَ الزَّنَادِقَةُ الْمُنَافِقُونَ
مِنْ الْقَرَامِطَةِ الْبَاطِنِيَّةِ الْمُتَفَلْسِفَةِ وَأَمْثَالِهِمْ
يَمِيلُونَ إلَى الرَّافِضَةِ وَالْجَهْمِيَّة لِقُرْبِهِمْ مِنْهُمْ".
مجموع
الفتاوى (٣/ ٣٥٣)
Ma'ana; a cikin ƴan bidi'a akwai zindiƙai munafukai. To waɗannan
kafirai ne. Kuma sun fi yawa a cikin Rafidha ƴan
Shi'a. Shugabanninsu duka zindiƙai
ne munafukai.
To su kuma munafukai ba a yi
musu "wala'i" da soyayya, su ya su suke ƙaunar junansu, kamar yadda Muminai suke
jiɓintar
junansu, kamar yadda Ayar da ta gabata ta nuna haka. Don haka su ma munafukai
masoya sashe ne, Allah ya ce:
﴿ٱلۡمُنَـٰفِقُونَ
وَٱلۡمُنَـٰفِقَـٰتُ بَعۡضُهُم مِّنۢ بَعۡضࣲۚ یَأۡمُرُونَ بِٱلۡمُنكَرِ وَیَنۡهَوۡنَ
عَنِ ٱلۡمَعۡرُوفِ﴾ [التوبة ٦٧]
{Munafukai maza da munafukai
mata sashensu daga sashe ne (wato sashensu majiɓinta
sashe ne)}.
Ibnul Jauziy ya ce:
"وقالَ
مُقاتِلٌ: بَعْضُهم أوْلِياءُ بَعْضٍ، (يَأْمُرُونَ بِالمُنْكَرِ) وهو الكُفْرُ،
﴿وَيَنْهَوْنَ عَنِ المَعْرُوفِ﴾ وهو الإيمانُ".
Don haka Mumini ba zai jiɓinci
zindiƙi munafuki ba, ya nuna masa ƙauna, har ya goya masa baya a yaƙi. Don haka ba za a goya wa Iran baya
ba, a yaƙin da take yi, saboda gomnatin Iran
gomnatin Rafidha ce, su kuma zindiƙai
ne masu bidi'o'i na kafirci.
2- Saboda su Rafidha maƙiya Musulmai ne, suna adawa da su, suna
cutar da Musulmai. A jiya mun kawo maganganun Ibnu Taimiyya a kan haka. Kuma
abin da suka yi wa al'ummar Musulmi, a ƙasashen
Larabawa, a wannan zamani babban shaida ne a kan baƙar adawarsu ga Musulmi. Kai, abin da
yake faruwa a yanzu haka, yadda Iran take ta kai hare-hare kan ƙasashen yankin Gulf, babbar hujja ce a
kan shegen mungun nufinsu a kan Musulmai. Shi ya sa ko kwanan nan Abduljabbar
ya tona musu asiri. To haka suke a kowace ƙasa
ta Musulmai, ɓarna da neman tayar da fitina, da ɗaukar
nauyin aiyukan ta'addanci, da kafa ƙungiyoyin
tayar da ƙayar baya, da
renonsu, shi ne aikinsu. Ka je ƙasashen
Larabawa ka tambayi irin ɓarna da ta'addancin Iran, ka
sha labari.
Da ma Allah ya tsoratar da
mu game da munafukai, inda ya ce:
﴿هُمُ
ٱلۡعَدُوُّ فَٱحۡذَرۡهُمۡۚ قَـٰتَلَهُمُ ٱللَّهُۖ أَنَّىٰ یُؤۡفَكُونَ ٤﴾
[المنافقون ٤]
{Su ne maƙiyanku, don haka ku kiyaye su}.
Kuma Allah ya hana Muminai
jiɓintar
maƙiyansu, inda ya ce:
﴿یَـٰۤأَیُّهَا
ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ لَا تَتَّخِذُوا۟ عَدُوِّی وَعَدُوَّكُمۡ أَوۡلِیَاۤءَ﴾
[الممتحنة ١]
{Ya ku waɗanda
suka yi imani, kada ku riƙi maƙiyina kuma maƙiyinku a matsayin masoya}.
Saboda haka, ba za a goyi
bayan Iran ba, saboda maƙiya
Musulmai ne, masu cutar da su.
To amma da a ce: Iran ba ta
cutar da Musulmi, kawai dai matsalarta ita ce Aƙidunta
na kafirci, to idan aka lura aka ga cewa; goyon bayanta a wannan yaƙi shi ne Maslaha, saboda kusacinsu da
Musulmai, sai a goya musu baya, kamar yadda Annabi (saw) da Sahabbansa suka so
Rum su yi nasara a kan Farisa, saboda Rumawa sun fi kusa da Musulmai. Sun fi ƙaranci ɓarna
a kan Farisawa. Inda Allah ya ce:
﴿غُلِبَتِ
الرُّومُ ٢ فِي أَدْنَى الْأَرْضِ وَهُم مِّن بَعْدِ غَلَبِهِمْ سَيَغْلِبُونَ ٣
فِي بِضْعِ سِنِينَ ۗ لِلَّهِ الْأَمْرُ مِن قَبْلُ وَمِن بَعْدُ ۚ وَيَوْمَئِذٍ
يَفْرَحُ الْمُؤْمِنُونَ ٤ بِنَصْرِ اللَّهِ ۚ يَنصُرُ مَن يَشَاءُ ۖ وَهُوَ
الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ٥﴾ [الروم ٢-٥]
Amma Iran, bayan Aƙidun kafircin, sun haɗa da
cutar da Musulmai, kamar yadda ya gabata a jiya. Don haka ba su cancanci goyon
bayan Muminai ba, saboda maƙiya
ne, masu cutarwa.
Akwai wasu mutane da suke
ganin dole a goyi bayan Iran, har suke kafa hujja da wasu maganganu na Ibnu
Taimiyya a kan haka. To insha Allahu gobe za mu ɗauke
su mu warware shubuhohin masu kafa hujja da su, mu nuna wa mutane cewa; ana
kafa hujja da su ne ba a muhallinsu ba.
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.