Ticker

6/recent/ticker-posts

Matsayar Ibnu Taimiyya A Kan Goyon Bayan Iran

Ko shakka babu, duk wanda ya san Ibnu Taimiyya to lallai ya san Malami ne wanda ya cancanci kirarin da ake yi masa da cewa:

"رجل كل العصور".

Wato shi ɗan kowane zamani ne, saboda yadda a kowane zamani, kai ka ce: Ibnu Taimiyya a zamanin ya rayu, har zuwa wannan zamani da muke ciki, kai ka ce a wannan zamanin yake rayuwa tare da mu. Saboda yadda maganganunsa suka zama fitila, mai haska hanyoyin warware matsalolin kowane zamani.

To amma duk da haka maganganun nasa gamammu ne, wato za su zama dalilai ne a kan sababbin matsaloli da suke faruwa, amma ba maganganu ne ayyanannu a kan ayyanannu ba.

Misali; idan muka ɗauki yaƙin da Iran take yi a yanzu, ba za mu ce: ga matsayar Ibnu Taimiyya a kan Iran ba, ko yaƙin Iran, saboda asali Ibnu Taimiyya bai san Allah zai halicci wata ƙasa mai suna Iran a doron Duniya ba. Sai dai Ibnu Taimiyya yana da ɗaruruwan maganganu a kan Aƙidar Iran, da mabiya Aƙidar, wato Rafidha ƴan Shi'a, mabiya Aƙidar Rafidhanci.

Saboda haka ba za a ce: Matsayar Ibnu Taimiyya a kan yaƙin Iran da Amerka da Izra'ila ba, sai dai a ce: Matsayar Ibnu Taimiyya a kan Rafidha ƴan Shi'a, da Aƙidar Rafidhanci, Aƙidar Iran.

Bayan haka, akwai wata matsala da ake samu wajen masu kafa hujja da maganar Ibnu Taimiyya a kan ra'ayoyinsu da "mawaƙif" nasu, ita ce; ana samun ƙarancin fahimtar matsayar Ibnu Taimiyya, saboda kasancewarsa kogi ne maras iyaka, wanda hakan ya sa maƙiyansa da masoyansa suna ɗaukar maganganunsa suna ajiye su ba a muhallinsu ba, saboda rashin sanin dukkan maganganun nasa, ko rashin fahimtarsu. Wannan ya sa ƴan ta'adda, Khawarijawan zamani, suke ɗaukar maganarsa, su kafa hujja da ita a kan ta'addancinsu, alhali Ibnu Taimiyya ya fi kowa yaƙar ta'addanci. Sai maƙiyansa su riƙe su ce; ƴan ta'adda daga Ibnu Taimiyya suka ɗauki tunanin ta'addanci, alhali Ibnu Taimiyya ya fi kowa yaƙar tunanin ta'addanci. Shi ya sa masu husuma da shi a zamaninsa, ba su taɓa tuhumarsa da ta'addanci ba. An ɗaure shi a kurkuku har sau bakwai (7), amma duk ciki babu ɗauri ɗaya da aka yi masa bisa tuhumar ta'addanci.

Saboda haka kafin ka ce matsayar Ibnu Taimiyya a kan kaza ita ce kaza, akwai jan aiki a gabanka, na tattara dukkan maganganunsa, da kuma fahimtarsu a dunƙule, fahimta ingantacciya.

To, a wannan yaƙi da ake yi tsakanin Iran da Amerka/Izraila, mun ga wasu suna kafa hujja da wasu maganganu na Ibnu Taimiyya, a kan cewa; dole a goyi bayan Iran!

Alhali idan aka kalli maganganun da kyau, za a ga cewa; maganganun ana ajiye su ba a muhallinsu ba. Don shi Ibnu Taimiyya yana magana ne a kan matsayin kafiri mai dangantuwa ga Muslunci, tsakaninsa da kafiri ɗan asali. Ko shakka babu, zindiƙi munafuki wanda a zahiri ya nuna shi Musulmi ne, ya yi imani da Annabi (saw) da Addinin Muslunci, ya fi kafirin da bai taɓa yarda da Annabi (saw) da Addinin Muslunci ba.

To amma wannan hukunci ne gamamme, sakakke. Dole sai an lura da maganganun da za su keɓance su, da waɗanda za su ƙayyade su.

Don haka, idan an samu ɓangarori guda biyu, masu cutar da Muslunci da Musulmai, ɓangaren kafirai na asali, da kuma ɓangaren zibdiƙai munafukai, masu Aƙidu na kafirci, to dole hukuncin zai banbanta da wancan gamammen hukunci, kuma sakakke. Don haka, a wajen "wala'i" da goyon baya, dole a lura da maganar cutar da Musulmai, da adawa da su. Duk maƙiyin musulmai, mai cutar da su, to bai cancanci samun goyon bayansu ba.

Waɗannan Rafidha ƴan Shi'a, a tsawon Tarihi, sun fi Yahuɗawa da Nasara cutar da Musulmai, kamar yadda Ibnu Taimiyya ya sha faɗan haka a wurare da yawa. Daga ciki ya ce game da Rafidha:

"إنهم إذا كان لهم قوة وعدد في مكان، كانوا عدوا للمسلمين مجتمعين، يعادونهم أعظم من عداوة التتر بكثير.

ولهذا يخبر أهل الشرق القادمون من تلك البلاد: أن الرافضة أضر على المسلمين من التتر، وقد أفسدوا ملك التتر وميلوه إليهم، وهم يختارون دولته وظهوره، فكيف يجوز أن يكون في عسكر المسلمين من هو أشد عداوة وضررا على المسلمين من التتر؟!".

جامع المسائل لابن تيمية (٧/ ٢١٠)

Ma'ana; duk girman adawa da ta'addancin Tatar a kan Musulmai, to Rafidha sun fi tsananin ƙiyayyar Musulmi da cutar da su fiye da Tatar.

Ya sake cewa:

"إن جهاد العدو الخارجين عن شريعة الإسلام ليكون الدين كله لله، وحتى تكون كلمة الله هي العليا من أفضل الأعمال الشرعية.

وسعي المسلمين في قهر التتار والنصارى والروافض من أعظم الطاعات والعبادات، فإن هؤلاء محاربون لله ورسوله، خارجون عن شريعة الله وسبيله".

جامع المسائل لابن تيمية (٧/ ٤٣٦)

Ma'ana; Rafidha ƴan Shi'a suna cikin maƙiya Musulmai waɗanda ya wajaba a yaƙe su, a murƙushe su.

Yana magana a kan wajabcin yaƙar Khawarijawa, sai ya ce:

"والرافضة شر من هؤلاء؛ فإنهم يعاونون اليهود والنصارى، وعاونوهم مع هلاوون لما قدم إلى بغداد، فأعانوه على قتل بيت النبوة العباسيين وغيرهم من المؤمنين، وأعانوا اليهود والنصارى بالشام نوبة هلاوون وقازان، وغير ذلك، ولا ريب أن ضررهم على المسلمين أعظم من ضرر التتر".

جامع المسائل لابن تيمية (٧/ ٤٣٨)

Ma'ana; Rafidha ƴan Shi'a sun fi Khawarijawa sharri da cutar da Musulmai. Don haka, idan ya wajaba a yaƙi Khawarijawa ƴan ta'adda, to Rafidha su suka fi cancantar a yaƙe su.

A wani wajen ya ce:

"وَقَدْ علِمَ أَنَّهُ كَانَ بِسَاحِلِ الشَّامِ جَبَلٌ كَبِيرٌ، فِيهِ أُلُوفٌ مِنَ الرَّافِضَةِ يَسْفِكُونَ دِمَاءَ النَّاسِ، وَيَأْخُذُونَ أَمْوَالَهُمْ، وَقَتَلُوا خَلْقًا عَظِيمًا وَأَخَذُوا أَمْوَالَهُمْ، وَلَمَّا انْكَسَرَ الْمُسْلِمُونَ سَنَةَ غَازَانَ، أَخَذُوا الْخَيْلَ وَالسِّلَاحَ وَالْأَسْرَى وَبَاعُوهُمْ لِلْكُفَّارِ النَّصَارَى بِقُبْرُصَ، وَأَخَذُوا مَنْ مَرَّ بِهِمْ مِنَ الْجُنْدِ، وَكَانُوا أَضَرَّ عَلَى  الْمُسْلِمِينَ مِنْ جَمِيعِ الْأَعْدَاءِ، وَحَمَلَ بَعْضُ أُمَرَائِهِمْ رَايَةَ النَّصَارَى، وَقَالُوا لَهُ: أَيُّمَا خَيْرٌ: الْمُسْلِمُونَ أَوِ النَّصَارَى؟ فَقَالَ: بَلِ النَّصَارَى. فَقَالُوا لَهُ: مَعَ مَنْ تُحْشَرُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ؟ فَقَالَ: مَعَ النَّصَارَى".

منهاج السنة (٥/ ١٥٨ - ١٥٩)

Ma'ana; bayan Ibnu Taimiyya ya ambaci misalai na ta'addancin Rafidha, sai ya tabbatar da cewa; sun fi duk wani maƙiyin Musulmai cutar da Musulmai. Kuma suna son kafirai, suna taimakonsu a kan Musulmai.

Don haka idan ya tabbata cewa; Ibnu Taimiyya yana ɗaukar Rafidha a matsayin maƙiya Musulmai fiye da kowa, kuma mafiya cutar da su, to shin ya halasta Musulmi ya jiɓince su?

Alhali Allah ya ce:

﴿یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ لَا تَتَّخِذُوا۟ عَدُوِّی وَعَدُوَّكُمۡ أَوۡلِیَاۤءَ﴾ [الممتحنة ١]

{Ya ku waɗanda suka yi imani, kada ku riƙi maƙiyina kuma maƙiyinku, a matsayin majiɓinta}.

Ashe kenan, duk wasu maƙiyan Musulmai, ba abin ka goya musu baya ba ne.

To idan dai Muminai ba za su riƙi maƙiyansu majiɓinta ba, kuma ga Ibnu Taimiyya ya tabbatar Rafidha maƙiya Musulmai ne, me ya sa za ka goyi bayan Iran, a yaƙinsu tsakaninsu da kafirai?!

Ni dai ban ga dalili ba. Don haka ba na goyon bayan Iran, kamar yadda ba na goyon bayan Amerka da Izraila.

Allah ya sa su rusa junansu.

Saboda haka matsayar Ibnu Taimiyya game da Rafidha, ita ce yana ɗaukarsu ne a matsayin maƙiya Musulmai, kuma mafiya sharri, mafiya cutar da Musulmai cikin dukkan maƙiya Musulmai. Don haka tun da Iran Rafidha ƴan Shi'a ne, maƙiya Musulmai, to ba za a jiɓince su, har a goyi bayansu a yaƙinsu da kafirai ba.

Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)

 Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

Post a Comment

0 Comments