Waɗannan baituka sun kasance tahamisi na Waƙar Sanarwar Birnin Sirti (Hasken Haɗin Kan Afirka).
TAHMISIN WAƘAR SANARWAR BIRNIN SIRTI (HASKEN HAƊIN KAN AFIRKA)
Rubutawa
Farfesa A.B. Yahya
(09/09/1999)
***
Tahmisi
Usman Nagado
(II)
(06/0CT/2025)
Da sunanka Allah nake tutiya,
Ka sa mini haske cikin
zuciya,
Na tsara ƙasidar ƙasar
Libiya,
Ina gode Allah Gwani Mai
niya,
Da Yas sanya niz zo cikin
Libiya.
Akwai Larabawa da halin
ƙwarai,
Suna san mutane da tarba
ƙwarai,
Akwai natsuwa nan da kwanci
na rai,
Zamana a Sabha da sihha
sarai,
Cikin ƴanuwana lumui lafiya.
Madalla da shugaban ƙwarai
Gaddafi,
Fa laya a yau ta yi kyawun
rufi,
Ga mai son ya san shekarar da
na tafi,
Taran tara tis'a ka yo
lissafi,
Wa tisuna ga alfu Miladiya.
Ina can a Sabha ina shan
gara,
In tsoma biyar ga ruwana na
gora,
Ina can zamana ina Lakcara,
Ina kay yi Bayero nij ji
kira,
Muhammad na Shaibani yac ce
tsaya.
Na ce mai ina Sabha ai
har-ila-yau,
Ka diba garin naku ya yo
fayau,
Taho nan ka daina zama
sakayau,
Garin Sirti an buɗe ƙofa ga
yau,
Ta ƴantar da ƴaƴa na
Ifriƙiya.
Ka sa ni murna cikin zuciya,
Alla sa dai shi ɗore mu yo
moriya,
Muhammad na Shaibani yai
magiya,
Mabuɗinta Ƙaid Muammar jiya,
Ka ambato wannan cikin
ƙafiya.
Don Sha'iri kakke na gaskata,
Ka waƙe Mu'ammar sadaukin
fita,
Yaƙi na ƴanci fa ba kunyata,
Yana yin shi gwarzonmu na
tabbata,
Sabilinmu bardenmu bai
togiya.
Ƴanci a yau ya tsayar
hasumiya,
A birnin birane na Ifriƙiya,
Tun dai da Gaddafi yai
jiniya,
Muna gode Ƙahharu Mai tamaya,
Da Yab ba mu Gaddafi
Ifriƙiya.
Gaddafi ya yi kira ƴan'uwa,
Kowa ya yafe mu yo affuwa,
Mu ƙara haɗin kai da ma
shaƙuwa,
Ku zo ƴan'uwa dum mu yo
gaisuwa,
Wurin Ƙa’idi namu mai
gaskiya.
Mu ƙara hazaƙa mu zamto gaba,
Mu ƴanto ƙasashen Afrika
haba,
Burinsa ke nan mu bar
rarraba,
Muradinsa Gaddafi ai ci gaba,
Wadata da yanci ga Ifriƙiya.
Dukan farfaganda mu tuttunkuɗe,
Mu rege mu tsehe mu yo tankaɗe,
Mu tsaishe muradanmu ko ba daɗe,
Bukatarsa kullum ya zan mun
haɗe,
Muna tare jiddun kamar
tsintsiya.
Haba ɗiyan Afirika mu
wawwattsake,
Ya ce zuciyarmu mu dai
tsalkake,
Ga yau ga Mu'ammar ƙwarai ya
dake,
Mutuncinmu girmammu duy ya
fake,
Ga yau babu zulmu bale to
tsiya.
Mu zauna da juna a lami lumi,
Afirka a yau mun haɗo
gangami,
Ba ma raga wa dukan zalumi,
Mu rayu da ƴancinmu ba
ƙuƙumi,
Aminci ya wanzu kaza lafiya.
Sai mun yi himma fa mun
yunƙura,
Mu zauna da ƴancinmu ba
takura,
Ga wa za a samo fa wannan
dabara,
Muammar tunaninsa shi yag
gira,
Muallim jawabinsa ne iggiya.
Ina ne zumunta take yaɗuwa,
Ina ad da kishi da san
ƙaruwa,
Ina ad da mulkin nagarta
kuwa,
Ina ad da rizƙu da son
ƴan'uwa,
Ina ne da baiwa ga mai
tambaya.
Ina Ɗanmu'abba ina Zabiya,
Ku shelanta wannan cikin
duniya,
Ina nan a Sabha ina tambaya,
Wace ta fa aljanna nan
duniya,
Mufakkir ya gano ta Ifriƙiya.
Kun ban gari ne fa ko kun
tuna,
Idan babu amsa fa kun
dangana,
Ku bi ni da sannu ina
zayyana,
A can Sirti hasken ga yab
bayyana,
Ga yau kuma ya game dun
nahiya.
Hasken fa ya zarce hasken
subahi,
Mun samu ni'ima ƙwarai
wallahi,
Alhamdu mui godiya gun Ilahi,
Zama wanga shi ag garin
fatahi,
Mahaifar karimi na Ifriƙiya.
Haskensa ya game duk duniya,
Ya sa Afirkanmu tai lafiya,
Yau Sirti ta haifi mai
gaskiya,
Imamimmu Gaddafi mai anniya,
Cikin Sirti ka ƴanto
Ifriƙiya.
Ka shelanta ƴanci ga duk
duniya,
Ka ce ƴan Afrika mu ɗau
aniya,
Mu zo kai ma ƴanci a nan
tushiya,
Kiran ga da kay yi ka san mun
jiya,
Faɗi naka ne mu ka yi sat ɗaya.
Fuskar Afrikanmu ta yi kyan
dibi,
Tsarin da kas sa mu yai kyan
zubi,
Da ɗaiɗai da ɗaiɗanmu ai
bi-da-bi,
Tafarkin da kas sa mu shi za
mu bi,
Kana gaba dahir mu kai aliya.
A da ayyukanmu suna karkace,
Nasara su watso dukan
tarkace,
Ga yau nahiyarmu fa mun
taskace,
Ga yau ba mu tsoro bale wai a
ce,
Mu zauna da raki kamar
mujiya.
Sadaukin Afirka ga yau mun biɗai,
Ya watse magabtanmu shi shi
kaɗai,
Ƙwarai ba musu ai da ɗaiɗai
da ɗai,
Magabtammu mun san su ko can
daɗai,
Da kura da shaho da ko
mikiya.
Ga yau mun fahimce ka mun
gaskata,
Muna yin bara'a ga tsarin ɓata,
Ɓarayinmu fuskar su ta
jirkita,
Da ɓera da kolon ga sun
firgita,
Rashinka ka sanya su yin murɗiya.
Gwarzo Mu'ammar fa tun da ya
furta,
Mun daina yarda da gayyar
macuta,
Yau arziƙinmu ga ku ya
haramta,
Ga yau kam ina suke dus sun
shata,
Kana tsaye zaki na Ifriƙiya.
Muna nan a tare ma'an
rai-da-rai,
Hana musu ɓarna su gungun
birai,
Gaddafi taso da himmar
ƙwarai,
Fatattaki gungun macuta ɓarai,
Hana musu rinto na Ifriƙiya.
Mu taso mu kange dukan
rawuka,
Da yunwa talauci mu bar
basuka,
Mu'ammar fa ka san su domin
haka,
Ka kwankwatse kanun dukan
karnuka,
Da su ne akan cuci nan
nahiya.
Suna sa siyasa muna rarraba,
Suna bamu bashi na tsintsar
riba,
Su kwashe arziƙi suna ci
gaba,
Sunai mana hila da son ci
gaba,
Su ja mu su jefa cikin
rijiya.
Abdalla Bayeronmu ne Farfesa,
Asalinta waƙar ya tsara bisa,
Sharrin Nasara ya yo fallasa,
Muradinsu saishe mu har duƙ
ƙasa,
Muna bauta Turai da Shaiɗaniya.
Da TAHAMISI Usman Nagado na
iso,
Hijira tana ZAMTASHUN na
hammaso,
Ar ku ja jiki tun da mun
burguso,
Fa kaiconsu bardenmu ai ya
iso,
Niƙatau
Muammar da ke gaskiya.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.