𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum mallam. Mace ce ta tashi aure, sai wanda za ta aure ya tambayeta ita budurwa ce, toh mallam gaskiya dai ba cikakkiyar budurwa ba ce. toh mallam ya kamata ta faɗa mishi gaskiya ko kuwa a'a? Kuma idan matar aure ta yi zina shin lallai sai ta tona asirin kanta ga mijinta sannan yafiyarsa gareta za ta karɓu ga Ubangiji??
SHIN ZAN IYA FAƊA WA SAURAYINA KO MIJINA
CEWA NA TAƁA
AIKATA ZINA?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam
Warahmatullahi Wabarkatuhu.
Bazata gaya masa ba. Domin
babu Maslaha idan ta gaya masa. Koda bai Aureta ba, sai kuma yaje yana yaɗawa
a Cikin mutane. Kuma Nasan ma zaiyi wahala ya Aureta.
Batun mijinta kuma wannan
akwai wata ƙa'ida ta Fiƙhu suka ce wai Tunkuɗe ɓarna
shi ake gabatarwa memakon a janyo maslaha, DAR'UL MAFSADA MUƘADDAMUN ALA JALBUL MASLAHA kin ga anan
gayawa mijin naki cewa kinyi zina yayafe miki wannan babu shakka maslaha ne, to
amma kuma bakida tabbacin cewa mijin zai hakura yayafe miki kuma yaci gaba da
zama dake bayan kin gaya masa, kekanki zaki riƙa
tunanin infa kika gayamai kinyi zina ze iya cewa ya sake ki, wanda sakin
shikuma ɓarna
ce, bayan sakin kuma waɗanda basu san kinyi wannan
zinan ba duk sesun sani musamman iyayenki kuma hakan bazai musu daɗi ba
kema kuma mutuncinki zai zube kin ga wannan duk ɓarna
ce, sannan kuma kin tonama kanki asiri bayan Allah ya rufa miki wannan shima
duk ɓarna
ne.
Dan haka malamai suka ce
wacce tasamu kanta a cikin irin wannan halin to kawai taroƙi mijin yayafe mata dukkan laifukan da
ta yi masa waɗanda ta sani da wanda bata saniba, amma
karta kuskura ta gaya mishi cewa ga abin da ta yi saboda karta buɗe ƙofar waɗancan
ɓarnace
ɓarnacenda
zasu iya biyo baya.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.