𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mace ce tana son aure sosai to kuma lokacin auren bai zoba seya zamana kowani lokaci tunanin ta na aurene ko mijin da zata aura kuma malam har a cikin sallah tana shagala da wannan tunanin tana son abata shawarar da zata rage wannan tunanin takuma dena yinsa a cikin sallah Allah yasaka da alkhairi🙏🙏🙏
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Toh Shawarar da zan ba ta Shi
ne ta Ci gaba da yin Addu'a Sa'annan ta Sanya Niyyar yin Aure a Ranta, Sa'annan
duk abun da Allah ya Jinkirtawa Bawan sa, toh ki Sani Cewa Wannan Abun Yana
Zama Alkhairi ne ga Bawa. yin gaggawar Aure a wannan zamanin Kuskure ne sosai
ga Mace domin halin wasu Mazan yanzu sai Allah kawai, ayi Auren ki wata 2 kaɗai
Amma a sati 1 ko 2 ki gane cewa kin yi Kuskuren Auren wannan Mijin kin ga ai
akwai matsala gara jinkirin.
Don Haka ta ci gaba da yin
Addu'a kullum sannan ta Rika Sanya Addu'oin a Cikin ibadar ta, Allah ya kawo
Mata Miji Nagari Mai Addini, Amma ta rage Yawan Tunanin Haka idan har tana
cikin yin ibadar Allah ne, toh ta Cire komai a Cikin Ranta ta Kusanto da Imanin
ta da Dukkan Hankalin ta zuwa gurin ibadar ta, kada ta Rika tuna Komai Sai tuna
Allah da Makomar ta.
Matukar tana tuna Haka
Sa'annan tana yawaita yin Addu'oin domin Allah ya kawo mata Mijin Auren, toh In
Sha Allah Mijin ta Yana Nan tafe zata gan shi.
Duk yadda ta kai ga Son yin
Auren idan Lokacin yin Auren ta Bai Yi ba, toh Mijin nata wato Wadda zai Aure
ta ba zai taɓa zuwa ba, Amma matukar Lokacin ta ya yi
toh In Sha Allah zatayi Auren ta, Kuma Jinkirin da Allah ya yi mata Babu Auren
zai Zama Alkhairi ne gare ta. Dafatan kin gane Koh?
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.