Sabani tsakanin Ahlus Sunna da 'Yan Bidi'a; Sufayensu da Ash'arawansu da Khawarijawansu da Rafidhawansu, ba sabani ne wanda yake da halasci ba, wanda ijtihadi zai iya shiga cikinsa, a'a, sabani ne na Manhaji, tsakanin Manhajoji guda biyu masu kishiyantar juna, wanda yake hukunta daya yana kan gaskiya, daya kuma yana kan bata.
- Manhajin Ahlus Sunna ya ginu ne
a kan Bin Wahayin da Allah ya saukar wa Manzonsa (saw) na Alkur'ani da Sunna,
bisa fahimtar Sahabbai da sauran magabatan al'umma.
- A lokacin da Manhajin Sufaye ya
ginu a kan Kashfi, da gabatar da shi a kan Wahayi.
- Manhajin Asha'ira ya ginu a kan
Hankali, da gabatar da shi a kan Wahayi.
- Manhajin Khawarijawa ya ginu a
kan bataccen Addini ta hanyar Bin Alkur'ani ba bisa fahimtar Salaf da Manyan
Malaman Al'umma da aka musu shaida ba.
- Manhajin Rafidha ya ginu a kan
tatsuniyoyi daga Limamansu, da gabatar da su a kan Wahayi.
A bisa hakika duk Manhajin da ba
shi da alaka ta kai tsaye da abin da Manzon Allah (saw) ya bar Sahabbansa a
kansa to batacce ne, kuma bata ne.
Saboda haka masu kokarin yin
sako-sako da sabanin da ke tsakanin Ahlus Sunna da Sufaye, ya kamata su koma su
san Manhajin na Ahlus Sunna, kuma su san Manhajin Sufayen, kafin su fara yin
magana.
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.