Ahlus Sunna su ne mabiya Annabi (saw). Su suka yi imani da shi, suke sonsa, suke girmama shi, suke binsa, suke yi masa ɗa'a, suke riƙo da Sunnarsa, suke shagaltuwa da Hadisansa, suke ɗaukar Addini daga gare su, shi ya sa ake danganta su ga Sunnarsa.
Saɓanin
ƴan
bidi'a, ba sa binsa, ba sa riƙo da Sunnarsa, sai dai raya sonsa, ba
tare da karɓa daga
gare shi ba.
Saboda haka mabiya Sunnar Annabi
(saw) su ne masoya Annabi (saw) na gaskiya, su ne masu girmama shi girmamawa ta
gaskiya.
Wannan ya sa hatta wajen kore wa
Annabi (saw) haƙƙin Allah dole ne a duba haƙƙin Annabi (saw) na girmamawa da Allah ya
wajabta mana. Saboda Annabi (saw) mutum ne mai girman matsayi. Shi ya sa Allah
ya yi umurnin a girmama shi:
﴿لِّتُؤۡمِنُوا۟
بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَتُعَزِّرُوهُ وَتُوَقِّرُوهُۚ وَتُسَبِّحُوهُ بُكۡرَةࣰ وَأَصِیلًا﴾
[الفتح ٩]
Ibnu Jarir ya ce:
"فأما التوقير: فهو التعظيم والإجلال والتفخيم".
تفسير
الطبري (٢٢/ ٢٠٨)
Allah ya koyar da mu yi masa
ladabi da girmama shi, a cikin Ayoyi biyar ɗin
farko na Suratu al-Hujrat; daga ciki, ya hana ɗaga
murya a wurinsa:
﴿یَـٰۤأَیُّهَا
ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ لَا تَرۡفَعُوۤا۟ أَصۡوَ ٰتَكُمۡ
فَوۡقَ صَوۡتِ ٱلنَّبِیِّ وَلَا تَجۡهَرُوا۟ لَهُۥ بِٱلۡقَوۡلِ كَجَهۡرِ بَعۡضِكُمۡ
لِبَعۡضٍ أَن تَحۡبَطَ أَعۡمَـٰلُكُمۡ وَأَنتُمۡ لَا تَشۡعُرُونَ﴾ [الحجرات ٢]
Ya haɗa umurni da yin Imani da shi tare da imani da
Allah:
﴿یَـٰۤأَیُّهَا
ٱلَّذِینَ ءَامَنُوۤا۟ ءَامِنُوا۟ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ﴾ [النساء ١٣٦]
Ya haɗa yi masa ɗa'a
tare da ɗa'a ma Allah:
﴿یَـٰۤأَیُّهَا
ٱلَّذِینَ ءَامَنُوۤا۟ أَطِیعُوا۟ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ وَلَا تَوَلَّوۡا۟ عَنۡهُ وَأَنتُمۡ
تَسۡمَعُونَ﴾ [الأنفال ٢٠]
A wani wajen ya ce:
﴿مَّن
یُطِعِ ٱلرَّسُولَ فَقَدۡ أَطَاعَ ٱللَّهَۖ ﴾ [النساء ٨٠]
Ya haɗa sonsa tare da son Allah:
﴿
أَحَبَّ إِلَیۡكُم مِّنَ ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَجِهَادࣲ فِی سَبِیلِهِۦ فَتَرَبَّصُوا۟
حَتَّىٰ یَأۡتِیَ ٱللَّهُ بِأَمۡرِهِۦۗ وَٱللَّهُ لَا یَهۡدِی ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡفَـٰسِقِینَ﴾
[التوبة ٢٤]
Saboda haka kuskure ne a samu
Ahlus Sunna suna sakaci wurin girmama Annabi (saw), saboda girman matsayinsa,
da yadda suke girmama Sunnarsa.
Yana da kyau mu koma ga Salaf mu
ga yadda suke girmama Annabi (saw).
- Urwatu bn Mas'ud ya ce: Na je
wurin sarakuna, na je wurin Qaisar da Kisra da Najashiy, amma Wallahi ban taɓa ganin wani Sarki da
mutanensa suke girmama shi kamar yadda Sahabban Annabi Muhammad (saw) suke
girmama shi ba...
Idan yana magana za su yi kasa da
sautinsu. Ba sa iya ƙura masa ido saboda girmamawa.
- Sahabbai idan suna zaune a
gaban Annabi (saw) suna nitsuwa matuƙa, kai ka ce tsuntsaye ne a kawunansu.
- Idan suna zaune a gaban Annabi
(saw) ba sa ɗaga kai
gare shi, saboda girmamawa.
Don haka idan ka bibiyi Manhajin
Salaf wajen girmama Annabi (saw) za ka fahimcin kuskuren da wasu suke yi, na
rashin ladabi wa Annabi (saw) da sunan kare Tauhidi.
Shaikhul Islami daga cikin abin
da ya faɗa, na abin da
Alƙali
Iyadh ya naƙalto
daga Malik a kan matsayin Annabi (saw), a "Ashafa":
"...أَنَّ حُرْمَةَ النَّبِيِّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ
وَسَلَّمَ بَعْدَ مَوْتِهِ وَتَوْقِيرَهُ وَتَعْظِيمَهُ لَازِمٌ؛ كَمَا كَانَ حَالَ
حَيَاتِه. وكَذَلِكَ عِنْدَ ذِكْرِهِ، وَذِكْر حَدِيثِهِ وَسُنَّتِهِ وَسَمَاعِ اسْمِهِ".
الفتاوى
(١/ ٢٢٦)
"...Lallai kare alfarmar
Annabi (saw) bayan wafatinsa, da daraja shi, da girmama shi dole ne, kamar
yadda lamarin yake a halin rayuwarsa. Haka nan dole a girmama shi wajen
ambatonsa, da ambaton Hadisinsa da Sunnarsa, da jin sunansa".
Sai ya kawo misalai daga Salaf:
- Ayyub al-Sukhtayaniy, idan an
ambaci Annabi (saw) kuka yake yi, saboda girmama Annabi (saw) da kwarjinin da
yake yi masa.
- Haka Ibnu al-Munkadir.
- Haka Amir bn Abdullah bn
Zubair.
- Haka Safwan bn Sulaim.
- Malik, idan an ambaci Annabi
(saw) sunkiyar da kai yake, fiskarsa ta canza.
- Haka Ja'afaru al-Sadiq.
- Haka Ibnul Qasim.
- Al-Zuhriy, idan aka ambaci
Annabi (saw), yana kaɗuwa
sosai.
Haka Shaikhul Islami ya nakalto
daga Alƙali
Iyadh, daga Malik.
Saboda haka, abin da wasu suke
yi, da sunan Tauhidi, ko raddi ga Sufaye, suna haɗa
sunan Annabi (saw) da sunayen wasu shehunai, suna siffanta su da sunaye na
kaskantarwa, ko salon magana wacce babu girmama Annabi (saw) a ciki, wannan abu
ne da ya saɓa girmama
shi (saw), ko da kuwa da sunan Tauhidi aka yi. Saboda Allah ya hana yi wa
Annabi (saw) magana kamar yadda za mu yi ma waninsa:
﴿لَّا
تَجۡعَلُوا۟ دُعَاۤءَ ٱلرَّسُولِ بَیۡنَكُمۡ كَدُعَاۤءِ بَعۡضِكُم بَعۡضࣰاۚ﴾ [النور
٦٣]
Saboda haka duk Tauhidin da babu
girmama Annabi (saw) a haɗe
da shi to ba ingantaccen Tauhidi ba ne.
Don haka a maganar Tauhidi dole a
duba girmama Manzon Allah (saw).
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.