Citation: Maimota, A.S & Kabir, J. (2024). Dabarun Bayar Da Labarin Wasu Al’adun Hausawa A Bakin Makaɗa Dankwairo: Nazarin Wakar Ba Takura Kaurin Gaba. Algaita Journal of Current Research in Hausa Studies. Vol. 17, No. 1, December, 2024. Pg. 65-76
DABARUN BAYAR DA LABARIN WASU AL’ADUN HAUSAWA A BAKIN MAKAƊA ƊANƘWAIRO: NAZARIN WAƘAR BA TAKURA KAURIN
GABA
Na
Aishatu Shehu Maimota
+2348066054705
maimotaisha@gmail.com
Da
Hauwa Rabi’u Ɗanbappa
+2348035452399
Hauwadanbappa200@yahoo.com
Tsakure
Adabin Hausa hanya ce ta bayyana rayuwar
al’ummar Hausawa, kama daga al’adu da tarihi da yanayin zamantakewa. Wannan Maƙala ta bibiyi yadda Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya yi dabara ya
bayar da labarin abin da ya shafi masarautar garin Kano a waƙarsa mai suna “Batakura
Kaurin Gaba”. Makaɗin ya bayyana yadda
ake gudanar da hawan salla a wannan masarauta. Takardar ta gano yadda wannan
mawaƙi ya saƙa basirarsa ya bayyana
yadda ƙasaita ta mulkin sarkin Kano Alhaji Ado
Bayero take, da yadda yake gudanar da haye-hayen salla, tare da yanayin
kwalliyarsa da wuraren da yake ziyarta a yayin wannan hawa. A ɓangare ɗaya wannan maƙala ta yi fashin baƙi kan ɗiyoyin wannan waƙa. A yayin wannan fashin
baƙi an bayyana ma’ana da amfanin wasu kayayyaki na
al’adar wannan masarauta da mawaƙin ya zayyano. Haka
zalika takardar ta yi ƙarin haske kan wasu
abubuwa da Ɗanƙwairo ya bayyana a
wannan waƙa. An gudanar da wannan bincike ta hanyar
duba da ra’i da Gusau (2015) ya samar. Masanin ya bayyana daga cikin dabaru da
ake gudanar da tarke adabi akwai inda ake ‘tarken al’adu a wasu sassan adabi’
da kuma ‘tarken fashin baƙi’, duba da haka ya sa
wannan maƙala ta bibiyi al’adu da aka zayyano na
masarautar Kano a wannan waƙa mai suna
‘Batakura Ƙaurin Gaba’, tare da yin fashin baƙi a kan ɗiyoyin waƙar. Wannan bincike ya
gano cewa masarautar Kano ta keɓanta da wasu al’adu da ita kaɗai take gudanarwa
a ƙasar Hausa. Haka zalika wannan masarauta
tana da wasu kayayyaki na sarauta waɗanda su ma ita kaɗai ta keɓanta da su.
Kalmomin Bincike: waƙar baka, Bayar da
labari, al’adu, fashin baƙi.
1.1 Gabatarwa
Mawaƙan Hausa na da dabarar bayar da labari a waƙoƙinsu inda suke bayyana labari na wani abu da ya faru ko yake
zuciyarsu cikin waƙa. Iri waɗan nan waƙoƙi su ne da Turanci ake kira da narratiɓe poetry. Masana irin su Hess sun bayyana waɗannan waƙoƙi da cewa waƙoƙi ne da suke bayyana wani cikakken labari na wani abu da
yake ɗauke da
wata manufa. Irin wannan dabara makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya bi ya bayar da labarin wasu abubuwa da suka shafi
masarautar Kano a zamanin mulkin marigayi sarkin Kano Alhaji Ado Bayero. Haka
zalika Hess ya bayyana cewa za a iya raba ire-iren waɗannan waƙoƙi zuwa kashi huɗu, ciki har da abin da ya kira ‘epic’, wato
‘kandamin labari’. Waƙa mai ɗauke da kandamin labari waƙa ce da take ɗauke da labari mai tsawo wanda zai iya zama tarihi. Wannan takarda
ta bibiyi yadda Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya bayar da labarin hawan ƙaramar salla a masarautar Kano. A ya yin bayar da wannan labari ya
fito da wasu al’adu da wannan masarauta take da su, ire-iren waɗannan al’adu wannan maƙala ta binciko a wannan waƙa tare da yin fashin baƙi a kai. An gudanar da wannan nazari ne ta duba da ra’i da Gusau
(2015) ya samar. Masanin ya bayyana yadda ake tarken adabin Hausa, daga cikin
dabaru da ake gudanar da tarken akwai inda ake ‘tarken al’adu a wasu sassan
adabi’ da kuma ‘tarken fashin baƙi.
An kasa wannan maƙala zuwa kashi uku,
kashi na farko gabatarwa ce tare da taƙaitacen tarihi makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun da bayanin
waƙar ‘Batakura Ƙaurin Gaba’. Kashi na
biyu kuma an yi bita kan ma’anonin al’ada da waƙar baka tare da taƙaitaccen bayanin ra’in
tarken al’adu a wasu sassan adabi da kuma tarken fashin baƙi. Sai kashi na uku inda
aka kasa shi gida biyu, an fara da bayyana haye-hayen salla da ake gudanarwa a
masarautar Kano. A ɓangare na biyu kuma aka
kawo al’adun da Ɗanƙwairo ya kawo a wannan waƙa tare da yin fashin baƙi wato bayani a kan waɗannan al’adu.
1.2 Taƙaitaccen Bayanin Waƙar ‘Ba takura Kaurin
Gaba’
Waƙar Ba takura kaurin gaba
tana daga cikin waƙoƙin sarakuna da Ɗanƙwairo ya yi wa marigayi
sarkin Kano Alhaji Ado Bayero wanda ya yi mulki daga shekarar 1963-2014. Ya yi
wannan waƙa ne tsakanin shekarar 1975 zuwa 1978, domin makaɗa Ɗanƙwairo ya nuna ya yi
wannan waƙa ne a lokacin mulkin gwamnan Kano Kanal Sani Bello,
kamar yadda ya bayyana a waƙar inda ya ce:
... Nan yaz zo ya sabka,
Gwamnan Kano Sani Bello.
yas sauko suka gaisa....
waƙar tana da ɗiya 27 kamar yadda suka
zo a Gusau (2019)
1.2.2 Bitar Ma’anar Al’ada
Magaji (2002) ya bayyana
al’ada kamar haka: “Al’ada ita ce hanyoyin da al’umma take bi domin gudanar da
rayuwarta waɗanda suka
haɗa da
abinci da sutura da muhalli da gine-gine da sadarwa da sauran muhimman abubuwa
na wannan al’umma.”
Haka kuma, an bayyana
al’ada da cewa “…hanya ce da al’umma take gudanar da rayuwarta ta yau da kullum
ta fuskar tsarin zamantakewa da abinci da muhalli da tufafi da gine-gine da
bukukuwa da ma dukkanin wasu abubuwa da suka shafi al’umma da rayuwarsu ta yau
da kullum.” (Mu’azu, 2013:1)
2.1 Taƙaitaccen Bayanin Ra’in
Tarken Adabin Hausa
Gusau (2015) ya bayyana yadda tarken
adabin Hausa ya samu da cewa;
Hausawa sun sami hanyar yi wa adabinsu
tarke bayan da suka iya rubutu da karatu na haruffan Romanci wato karatun boko.
Kafa makarantun boko da Turawa suka yi wa Hausawa da samar da hukumomi kamar
hukumar fassara (1929) DA Hukumar Talifi (1933) da Gaskiya Corporation , Tudun
Jukun Zariya (195) da Hukumar Yaƙi d Jahilci (1953) da
Hukumar NORLA, wato Samar da Adabi (1954-1960) da Kamfanin Gasiya (1960-1966)
da Kamfanin NNPC (Oktoba, 1966) sun taimaka wajen samar da ayyukan adabin
Hausa. (Gusau, 2015:11)
Gusau ((2015) ya ƙara da cewa:
Ayyukan tarke na adabin Hausa, musamman
daga ‘yan ƙasa Hausawa, da sauran masu sha’awar adabin Hausa sun
ci gaba da ƙaruwa suna bunƙasa. Daga cikin dabaru
na tarke da aka mai da hankali a kansu sun haɗa da:
§
Tarken
gargajiya
§
Tarken ƙagaggen labari
§
Tarken
al’adu a cikin wasu sassan adabi
§
Tarke
na fiɗa ko sharhi
§
Tarken
fashin baƙi
§
Tarken ƙalailaice adabi
§
Tarken
adabin baka
§
Tarken
sigogin adabi
§
da
sauransu (Gusau, 2015:13)
A taƙaice a wannan littafi
Gusau ya yi bayani dangane da ayyuka da masana tun daga Turawa zuwa Hausawa
‘yan ƙasa suka gabatar waɗanda za su zama jagora ga mai nazari ko tarken adabin
Hausa. Domin samun cikakken bayani a duba Gusau (2015:11-19)
3.0 Bayar da Labari da Fashin Baƙi kan Wasu Al’adu a Waƙar Ba Takura Kaurin Gaba
Makaɗa Musa Ɗnƙwairo Maradun a waƙarsa ta ‘Batakura Kaurin
Gaba’ ya bayar da labarin yadda ake gudanar da hawan salla a masarautar Kano, a
ya yin bayar da wannan labari ya fito da wasu al’adu da suka keɓanta da masarautar
Kanon. A wannan kashi an fito da yadda ya bayar da wannan labari tare da
bayyana waɗannan al’adu tare da yi
musu fashin baƙi wato ƙarin bayani.
3.1 Hawan Salla a Waƙar ‘Ba Takura Kaurin
Gaba’
Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun ya bayyana
ire-iren hawa guda huɗu da sarki Ado Bayero ya
gudanar a bikin ƙaramar salla ƙarama. Ya yi bayanin
yadda ya gudanar da waɗannan hawa.
3.1.1 Hawan Idi
Hawan Idi hawa ne da ake gudanarwa
ranar ɗaya ga salla wato, 1 ga
watan shawwal bayan an kammala azumin watan ramalana. Hawan idi shine hawa na
farko a bukuwan salla.
Makaɗa Musa Ɗanƙwairo cikin gwanancewa
ta iya waƙa ya zayyanoo hoton wannan hawa ta yadda ko da mutum
bai taɓa halartar kallon wannan
hawa ba zai habarto ya ya yake. Ya fara da zayyano tun daga fitowar sarkin daga
gida inda ya fita ta ƙofar mata zuwa filin masallacin idi, inda ya ce:
Jagora: Ni Alhaji Musa Ɗanƙwairo
Na tahi Kano na yi salla
Nig ga hawan sarkin Kano
Da zai fita zai je idi
Ta Ƙofar Mata ya fita.
Bisa al’ada sarki kan tafi sallar idi
a ƙafa sai ya dawo a doki, duk da makaɗa Musa Ɗanƙwairo bai fito ya
bayyana sarki ya tafi a ƙasa ba amma ya bayyana da zai dawo ya hau doki, ya
dawo ta Ƙofar Wambai, sannan ya faɗi cewa da zai koma gida ya shiga ta Ƙofar Arewa. Ga yadda ya
zayyano:
Sarki ya hau doki
Ya shiga Ƙofar Wambai
-------------------------------
Ya shiga nan Ƙofar Arewa
Haka zalika makaɗa Musa Ɗanƙwairo cikin hikima da
fasaha ya zayyana hoton irin shigar da sarki ya yi a ranar salla inda mai
sauraro zai iya hasaso yanayin shigar sarkin a zuciyarsa:
Jagora: Bakan Dabo na ga hannunai
Ga kwarinsa ya rataya
Da anka sabko idi
Ya dogara shi yay yi huɗuba.
A ɓangare ɗaya makaɗin ya zayyano yadda hakiman sarki da bayinsa suka fito
domin raka sarki, in da ya ce:
Daudu: Hakiman sarkin Kano,
Su talatin da shidda ne,
‘Y/Amshi: Ga layin ‘yansanda,
Ga layin ‘yandoka,
Ga samarin sarki ‘yan baka,
Ga layin zagaigai,
Ga dawakin zage,
Ga raƙumi, farin doki,
An ka haɗa su wuri ɗai,
Kuma ga Shamaki Ɗanrimi
Manyan bayin sarki.......
Bayan ya gama zayyano waɗannan sai kuma ya
bayyana yadda sarki a kan hanyarsa ta dawowa ya tsaya a Gwauron Dutse inda
gwamna na wannan lokaci ke tsaye yana dakon zuwan sarki, sarki ya tsaya sun
gaisa har gwamnan ya yaba wa sarki bisa irin hidimar da yake wa talakawansa.
Jagora: Har ya za ka Gwauron Dutsi
Nan yaz zo ya sabka
Gwamnan Kano Sani Bello
Yas sakko suka gaisa...
Makaɗa Ɗanƙwairo bai tsaya a nan ba
sai da ya labarto mana cewa bayan gaisawa da gwamna, sarki ya shiga Ƙofar Arewa ya tsaya ya
yi wa talakawa jawabin salla tare da yi musu nasiha. Inda ya ce:
Jagora: Ya shiga nan Ƙofar Arewa,
Ya gode wa Allah,
Ya gode wa Rasulillahi,
An ƙare azumi lahiya,
An ƙare salla lahiya,
Kowa ya zo ya sauka,
Ya ce musu kowa ya zo ya sauka,
A so Allah da zumunta,
‘Yan’uwa a so Allah da zumunta.
3.1.2 Hawan Daushe
Hawan Daushe shi ne hawa na biyu a jerin
hawan salla, ana gudanar da shi ne ranar biyu ga salla wato kashegarin idi.
Kamar yadda tarihi ya bayyana hawan Daushe ya samu ne a lokacin da sarki ya
sami labarin wani babban bawansa Daushe ba shi da lafiya,bai samu hawan idi ba.
Da sarki ya tambayeshi sai yace ba shi da lafiya, da yamma ta yi sai Sarki ya
sa aka buga kugen hawa aka hau sarki ya je Babban ɗaki ya gai da mahaifiyarsa daga nan suka kewaya wasu
unguwanni domin gaisawa da talakawansa. Bayan an sauka Sarki yace da Daushe
wannan hawa na ka ne. Daga nan aka samu sunan hawan ake cewa hawan Daushe.ganin
bai zo fada ba da yamma da ya zo shi. Tun daga wannan lokaci ya zama cikin
jerin hawan salla, sai ya zamana a ranar sarki kan tafi babban ɗaki, wato gidan
mahaifiyarsa ya gaishe ta. A wannan rana da safe sarki kan zauna a fada da ya
karɓi gaisuwar hakimai da
wasu rukunan jama’a, sai kuma ya shiga gida, da an yi sallar la’asar sai ya hau
doki a fita hawan Daushe, ya je ya gai da mahaifiyarsa daga nan ya biyo ta wasu
unguwanni na nan cikin gari ya gaisa da talakawansa. Makaɗa Ɗanƙwairo ya zayyana wannan
zama na fada da hawan Daushe da ake gudanarwa a wannan rana. In da ya ce:
Jagora: Da azzahar tak kama,
Sarki ya yi hawan daushe,
Ya
tafi babban ɗaki,
Ya
zo ya yi ziyara,
Ya
dawo ya sauka....
3.1.3 Hawan Nassarawa:
Hawan Nassarawa hawa ne na uku a jerin
hawan sallar Kano. Ana gudanar das hi da safe ranar uku da salla, inda sarki
kan fita da wuri. Sarki na fara sauka a gidansa na Nassarawa ya je ya kai
ziyara kabarin iyayensa da kakanninsa sarakuna da aka binne a wannan gida. Daga
nan sai ya ƙara hawa ya tafi gidan gwamna su gaisa sai kuma ya
biyo ta unguwoyi da suke yankin nassarawa ya ga talakawansa su gan shi.
Cikin hikima da gwanancewa makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya zayyano yadda
hawan Nassarawa ya kasance da yadda yake kai ziyarar ban girma ga gwammna da
sauran wurare da yake zuwa a yankin nassarawa wato, wajen gari. Ga yadda ya ce:
Jagora: Da salla tak kwana biyu,
Sarki
yay yi hawan Nasarawa,
Ya
tafi can Nasarawa,
Sai
ya zarce gidan Gwamna,
Sunka
gaisa da Gwamna
Sai
yah hau dokinai
Ya
dawo ƙofar Nassarawa,
Sai
yaɗ ɗau hanyar banki,
Mutanen
da suke banki,
Sun
yi layi a kan titi,
Suna
gaisuwa ga sarki,
Allah
sa ka yi jinkiri,
Ka
kai bisa bisa Madi,
Alhaji
ka kai bisa Madi, amin,
Das
sabon gari ya zaka Fage,
Mutanen
da suke Fage,
Sun
yi layi a kan titi,
Suna
gaisuwa ga Sarki,
Allah
sa ka yi jinkiri,
Ka
kai bisa Madi,
Alhaji
ka kai bisa Madi, amin,
Daf
Fage yas shigo birni,
Mutanen
da suke birni,
Sun
yi a kan titi,
Suna
gaisuwa ga sarki.....
3.1.4 Hawan Fanisau
Hawan Fanisau shi ne hawa na huɗu kuma hawa na ƙarshe a jerin hawan
salla a Kano. Ana gudanar da wannan hawa ne ranar biyar ga salla. Sarki kan
fita da safe ya tafi gidansa na Fanisau ya yini sai bayan la’asar ya dawo.
Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya bayyana
tarihin gidan sarautar Fanisau inda ya ce sarkin Kano Usman ne ya gina shi. Ga
yadda ya ce:
Da salla tak kwana biyar,
Sarki ya yi hawan Fanisau,
Fanisau gidan sarauta ne,
Tun lokacin Sarki Usuman,
Shi nag gina shi,
Daudu: Na ji tun lokacin Sarksi Usuman
‘Y/Amshi:Shi nag gina shi,...
3.2 Wasu Al’adu na Masarautar Kano a Waƙar ‘Batakura Kaurin
Gaba’
Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun, ya fito
da wasu al’adu na masarautar Kano a wannan waƙa da ya yi wa marigayi
sarkin Kano Alhaji Ado Bayero. Ya fito da al’adu da suka shafi suture da kayan
ado na sarki, haka ya fito da al’adu da suka shafi sufuri. A ɓangare ɗaya makaɗa ya fito da sunayen
wasu sarautu na bayin sarki.
3.2.1 Suturu da Kayan adon Sarki
A waƙar Batakura ƙaurin gaba, makaɗa Ɗanƙwairo ya bayyana
nau’ikan suturu da kayan ado na fada, kama daga waɗanda sarki yake amfani da su da na yaran sarki da na
bayinsa. Ya bayyana su kamar haka:
Sarki mai kyautar riguna,
Sarki mai kyautar wanduna,
Sarki mai kyautar kuftoci,
Sarki mai kyautar alkyabba,
Sarki mai kyautar rawuna,...
sai kuma:
...Da zai fita zai je idi,
Bakan Dabo na ga hannunai,
Ga kwarinai ya rataya,..
Akwai kuma inda ya ce:
Daudu: Ƙwairo tafiya ƙarin ilmi
Na ga ƙawa birnin Kano,
Na ga hawan bayin sarki,
Kuma na ga hawan yaran sarki,
Kowane hakimi yai ado,
‘Y/Amshi: Da yaranai sun tunjum,
Su
ko kayan doki,
Daga alkashafa, sai tunjumi,
Sai tumbas mai tsada...
Riguna da wanduna suturu ne na Hausawa,
amma akwai nau’ikan na fada duk da Ɗanƙwairo bai fito ya
bayyana ba, suna da riguna kama daga asake da saƙi da sauransu. Wanduna
kuma akwai masu kamun ƙafa da buje da sauransu. Kufta riga ce da ake yi
wa ɗinkin hannu. An sami
kufta daga ƙasashen Larabawa musamman na Magrib irinsu Maroko da
Aljeriya da Tunisiya da sauransu, sarakuna da hakimai da sauran mutanen fada
suna amfani da kuftoci somin ado. Ko a ɗinki kuftocin fada sun fita daban, domin ana yi musu
aiki mai yawa da zare na musamman. Alkyabba kuma riga ce doguwa mara hannu mai
buɗaɗɗen gaba mai aiki sosai,
sanna tana da hula a jikinta da ake kira ƙoƙuwa, ana yafa ta a kan
riga. Ita ma alkyabba an same ta ne daga ƙasashen Larabawa amma
sarakunan Hausa sun fi amfani da ita. Haka kuma sarki da hakimai ne kaɗai suke saka alkyabba,
sai kuma wasu manyan bayin sarki kamar Shamaki da Ɗanrimi da Sallama da
sauransu, waɗanda su ma ba koyaushe
suke saka wa ba sai lokutan bikin salla ko wani biki.
Rawani kuma abin naɗi ne da sarakuna da
hakimai da sauran mutanen fada suke amfani da su. Rawuna iri-iri ne kuma suna
zuwa a launuka daban-daban, akwai nau’ikan rawuna na ‘ya’yan sarki, akwai na
malamai da na bayin sarki. Shi rawani ana naɗa shi ne a ka. Rawuna akwai harsa fara da masu launi,
akwai wanda ake kira kuskus da akwai dan Sakkwato wanda ake kira ɗan Sardauna, akwai ɗankura wanda ake cewa
shuni.
“Bakan Dabo” da “Kwari”,kayan kwalliya ne
da sarakunan Kano ne kaɗai suke da shi.
Sarakunan Kano sun gaji wannan kwari da baka ne daga kakansu sarki Ibrahim
Dabo, wanda shi ne sarkin Kano na biyu na daular Fulani. Duk wani sarki na Kano
yana rataya wannan kwari na Dabo sannan ya dogara bakan kamar sanda. Amma ba
kodayaushe sarki ke amfani da kwari da bakan Dabo ba sai lokacin sallar
idi ƙarama da babba, sai kuma ko ranar juma’a idan za a buɗe masallaci. Yawanci ba
a ganin kwarin saboda idan sarki ya rataya yana ɗora babbar riga da alkyabba a kai, sai dai bakan da
yake dogarawa ake gani.
Idan aka ce ‘tunjum’, a fada ana nuni ne
da wata kwalliya ko shiga wadda yawanci manyan bayin sarki masu zama a gefensa
suke yi.haka zalika yaran hakimai ma suna wannan shiga. Shiga ce da ake yi
bayan an saka manyan riguna sai a zuba hamilu a yi ɗamara a naɗa rawani ɗan’kura. Wannan shiga
cikin ɗamara ake ce wa an yi
‘tunjum.’ Ko yara masu bin angwaye yayin hawan angwanci cikinsu akan sami waɗanda za su kasance a
gefen ango sun yi irin wannan shiga.
‘Alkashafa’ kayan ado ne na doki ne da ake
sa wa a ƙirjin doki mai kyalli tana da nauyi saboda akwai
’yan ƙarafuna masu kyalli a jiki. Amma yanzu ba a cika
amfani da ita ba ana amfani da ‘yan ƙirji marasa nauyi, sai
dai suna da zubin alkashafa ɗin.
‘Tunjimi’ ana kiransa ‘tunjima’ ita ma
kayan ado ne da ake sa wa a gaban doki a kan goshinsa. Asali tunjima ta da
tana ɗauke da ƙulaƙulai na ƙarfe yadda idan doki ya
girgiza kansa za a ji suna ƙara. Amma yanzu ana yin
tunjima da ƙulaƙulai na ƙyalli ba na ƙarfe ba, yadda ko doki
ya girgiza kansa ba za a ji wannan ƙara ba.
Tumbas shi kuma sirdi ne amma na azurfa,
yana da tsada ƙwarai ta yadda ba kowa ke iya mallakarsa ba,
kasancewarsa azurfa.
3.2.2 Sufuri
A kan abin da ya shafi sufuri ma, Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya kawo kayan hawa
na gargajiya kamar doki wanda ya ambace shi a wurare da dama, sai kuma raƙumi. Misali shi inda aka
ce:
‘Y/Amshi: Mai nasara ya mirɗo.
Ga layin ‘yansanda,
Ga
layin ‘yan doka,
Ga
samarin Sarki ‘yan baka,
Ga
layin zagaigai,
Ga dawaki
zage,
Ga raƙumi, farin doki,..
‘Dawakin zage’ dawakai ne na sarki da suke
gaban sarki waɗanda ake yi musu shiri
da ƙawa kamar za a yi amfani da su saboda shirin ko ta
kwana. Asali da sarakuna suna dogon zango idan za a tafi yaƙi ko fasa haraji, kuma
suna wannan tafiya ne a kan dawakai, saboda haka ake tafiya da wasu dawakan ko
da doki zai kasa ko kuma zai gaji a wannan lokaci sarki kan caccanza doki. Haka
kuma ana lulluɓes waɗannan dawaki saboda
girmama Sarki ba za a bar shimfiɗarsa a buɗe ba, ko da zai hau doki sai an kare saboda komai na
sarki a al’ada ana buƙatar sirri da girmamawa.
Raƙumi kuma a masarautar
Kano suna sa shi a gaba ne domin tuna yadda sarkin Kano Alu Maisango ya yaƙi Damagarawa a kan raƙumi. Sarkin Kano Alu ya
yi bad da kama alokacin wannan yaƙin, domin ya yi shiga
irin ta buzaye ya hau raƙumi maimakon doki. An ce a wannan yaƙin ya yi wa
Damagarawa ɓarna sosai. Kuma shi
wannan raƙumi kodayaushe yana gaban ‘yan baka ne wato suna biye
das hi a baya, hakan alama c eta nasara.
Farin doki, doki ne na ƙawa da sarki yake amfani
da shi ranar idi ko hawan juma’a. Amma kuma da alfadari ne a wurin farin doki,
tarhi ya nuna a zamanin sarkin Kano Abdullahi Bayero ana amfani da alfadarin
ne, ana zaton sarki Abdullahi Bayero ya kawo wannan alfadari ne daga gabas,
daga baya ne sarakuna da suka biyo suka maye gurbin alfadarin da farin doki,
wato bayan mutuwar wannan alfadari.
3.2.3 Wasu Sarautu da Muƙamai na Bayin Sarki
A wannan waƙa ‘Batakura kaurin gaba’
Makaɗa Ɗanƙwairo ya ambato wasu
yaran sarki da wasu manyan bayinsa. A wurin da ya ce:
‘Y/Amshi: Mai nasara ya mirɗo.
Ga layin ‘yansanda,
Ga
layin ‘yan doka,
Ga
samarin Sarki ‘yan baka,
Ga
layin zagaigai,
Ga
dawaki zage,
Ga
raƙumi, farin doki,
Anka
haɗa su wuri ɗai,
Kuma
ga Shamaki da Ɗanrimi,
Manyan
bayin sarkin Kano
‘Yan baka a masarautar Kano mayaƙa ne waɗanda suke gaban sarki,
suna kasancewa a gaba ne domin zama kariya ga sarki, kuma suna ɗauke da kwari dab aka
suna saka riga ‘yar shara da wando da hula haɓar kada launi baƙi da shuɗi. ‘Yan baka na jere da
sauran jami’an tsaro na masarautar Kano, kamar ‘yan bindiga da sauransu., ‘yan
baka ma’aikata ne da suke ƙarƙashin gidan Sallaman Kano.
Zagaigai su ne zagage da suke gaban sarki,
su suna riƙe da wasu abubuwa masu muhimmanci da sarki zai yi
amfani da su a gaba, irin su talha da butoci, waɗannan butoci an ce wasu na ɗauke da fura wasu ruwa.
Ana kiran shugaban zagage babban zagi, shi babban zagi jagora ne ga sarki, wato
inda ya taka ya cire ƙafa nan sarki zai taka ko dokinsa. Bayan babban zagi
wanda shi ne sarkin zagage, akwai galadiman zagi da sauransu.
Shamaki shi ne babban bawan sarki, domin
duk sauran bayin sarki irin su Ɗanrimi da sallama da
kilishi suna ƙarƙashinsa ne. Shamaki shi ne tsani tsakanin sarki da
hakimai da bayin sarki. Haka zalika duk wani abu da zai wakana a fada sai da
hannun, shi ne yake shigar da hakimai gaban sarki, haka zalika duka wani gandu
na sarki da dawakansa suna ƙarƙashin kulawar shamaki.
Akwai ayyuka da dama na fada da shamaki ke gudanarwa. A taƙaice shamaki kamar wani
hakimi ne a tsakanin bayin sarki domin yana da alkyabba da yake yafawa a wasu
lokuta, musamman lokacin bukukuwa. Haka kuma yana da hakimansa, akwai ciroman
shamaki da turakin shamaki da makaman shamaki da sauransu. A lokacin hawan doki
kodayaushe a cikin giwar sarki shamaki yana daga grfen damar sarki. Ana yi wa
shamaki kirari
Ɗanrimi yana daga cikin
manyan bayin sarki. Za a iya cewa shi ke bin Shamaki a muƙami, domin akwai wasu
abubuwa da Ɗanrimi yake gudanarwa idan shamaki baya nan. Haka kuma
shima Ɗanrimi yana da wasu ayyuka da shi kaɗai yake gudanarwa. Daga
cikin ayyukansa akwai kasancewa daga gefen hagun sarki a cikin giwar sarki,
wato idan ana hawa. A zamanin da Ɗanrimi ke kula da
ganuwar cikin birni, haka kuma daga dogon gida zuwa ƙofar Arewa duk wanda ya
rasu shi yake kula da harkar jana’izarsa. Ɗanrimi yana da hakimansa
irinsu Makaman Ɗanrimi da Galadiman Ɗanrimi da Ɗansarai da Turakin Ɗanrimi da sauransu. Shi
ma Ɗanrimi kamar Shamaki yana saka alkyabba a lokutan
hawa.
4.0 Kammalawa
wannan maƙala ta kalli yadda makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya yi wa Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero waƙa. A wannan waƙa mawaƙin ya wassafa yadda ake gudanar da hawan salla a masarautar Kano ta yadda wanda bai taɓa halartar hawan ba zai ga kamar hoton hawan aka jiye masa. Haka kuma takardar ta bibiyi wasu al’adu da makaɗin ya kawo na wannan masarauta tare da yi fashin baki wato bayani a kan waɗannan al’adu. Daga ƙarshe takardar ta gano lallai masarautar Kano tana da wasu al’adu waɗanda ita kaɗai ta keɓanta das u. Ire-iren waɗannan al’adu akwai na hawan idi wanda duk masarautun ƙasar Hausa ke gudanarwa akwai hawan Daushe wanda masarautar Kano ked a hawa mai wannan suna, haka hawan Nassarawa da na Fanisau. A ɓangare ɗaya binciken ya gano masarautar Kano kaɗai ked a bakan Dabo da kwarinsa, haka zalika a ɓanagaren sufuri akwai wasu abubuwa na tarihi da wannan masarauta kaɗai ke da su, irin su raƙumi da dawakin zage. Takardar ta kuma gano har yanzu masarautar Kano na riƙo da waɗannan al’adu nata da ta gada tuntuni.
Manazarta
Gusau, S. M. (2015) Mazhabobin
Ra’i da Tarke a Adabi da Al’adu na Hausa.
Kano: Century Research and Publishing
Limited.
Gusau, S. M. (2019) Diwanin Waƙoƙin Baka Juzu’i na Huɗu. Wasu Waƙoƙin
Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun
(1909-1991) Sarkin Kiɗan Sarkin
Maradun Jihar Zamfara. Kano: Century
Research and Publishing Limited.
Hess, G. R (2020) “Narratiɓe Poetry: Types,
History, and use.”
Khalil,
N. W (2006) Bayi a Gidan Dabo Tarihin Shamakin Kaano Inuwa Ɗan Sarkin Zage
Amfani da Sauran Manyan Bayin Sarki (1819-2006 AD). Kano: Gidan Dabino.
Magaji,
A. (1982) “Tasirin Adabin Baka A kan Rubutattun Ƙagaggun Labarai.” Kundin
Digiri na
Biyu. Kano: Jami’ar Bayero.
Mu’azu, A. (2010) Jirwayen Baƙin Al’adu na Nesa a Ƙagaggun Labaran Soyayya na Hausa. Cikin Harshe 4 Journal
of African Languages, pg 80-103, Zaria:A.B.U.
Muhammed, D. (1990) Hausa
Metalanguage (Kamus na Keɓaɓɓun Kalmomi)
Volume I. Ibadan: University Press.
Mutanen da aka Tattauna
Shamakin Kano Alhaji Wada
Alhaji Usman Kofar Kudu
Garkuwan Sallama Ali
Wakilin Turakin Dogarai Halifa Aminu
Hajiya Ummi Wada maiɗakin Shamakin Kano
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.