𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum Wa
Rahmatul Laah. Mijin da matar shi ta gano cewa da kuɗaɗen
sata ne yake ciyar da ita, mene ne matsayinta a wurin Ubangiji?
NA GANO CEWA DA KUƊIN HARAM NE MIJINA YAKE CIYAR DA MU
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa
Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.
Abu ne sananne a cikin
dokokin shari’a cewa, haram ne musulmi ya ciyar da kansa da haram, haka ma
haram ne ya ciyar da duk wanda haƙƙin
ciyar da shi ya ke rataye a wuyansa da haram. Domin hatsarin da ke tattare da
hakan tun daga nan duniya, kafin zuwa makoma Lahira.
A cikin hadisi Abu-Hurairah (Radiyal
Laahu Anhu) wanda Al-Imaam Muslim ya fitar da shi a cikin sahihin littafinsa (2393):
ثُمَّ ذَكَرَ الرَّجُلَ يُطِيلُ السَّفَرَ أَشْعَثَ أَغْبَرَ، يَمُدُّ يَدَيْهِ إِلَى السَّمَاءِ، يَا رَبِّ، يَا رَبِّ، وَمَطْعَمُهُ حَرَامٌ، وَمَشْرَبُهُ حَرَامٌ، وَمَلْبَسُهُ حَرَامٌ، وَغُذِيَ بِالْحَرَامِ
Sai kuma Annabi (Sallal
Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ambaci wani mutum wanda ya yi doguwar
tafiya, mai yamutsattsen gashin kai mai cike da ƙura,
yana miƙe hannuwansa zuwa sama, yana addu’a da cewa: Ya Ubangijina! Ya
Ubangijina! Amma kuma ya kasance abincin sa haram ne, abin shan sa ma haram ne,
tufafinsa ma haram ne, sannan kuma da haram aka rene shi… Shi ne Annabi (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
فَأَنَّى يُسْتَجَابُ لِذَلِكَ؟
To, ta yaya za a amsa masa?
Wannan dalili ne mai ƙarfi kuma a fili ƙarara kan cewa: Cin haram yana daga
cikin abubuwan da suke hana amsar addu’a a
nan duniya, ko da kuwa mutum yaro ne wanda ba shi da kansa ne ya samo haram ɗin
ya ci ba! Musamman idan shi kuma a bayan ya girma sai ya ɗora
daga inda mai ciyar da shi ɗin ya tsaya.
A Lahira kuma akwai alƙawarin shiga wuta ga mai cin haram,
saboda riwayar da ta ce:
«إِنَّهُ لَا يَرْبُو لَحْمٌ نَبَتَ مِنْ سُحْتٍ، إِلَّا كَانَتِ النَّارُ أَوْلَى بِهِ»
Babu wata tsokar naman da za
ta ginu daga haram, face Wuta ce ta cancance shi. (At-Tirmiziy: 614, kuma
Al-Albaaniy ya sahhaha shi).
Allaah Ta’aala ya kiyaye.
Daga ƙarshe muna bayar da shawarar cewa:
Wajibi ne irin wannan mijin ki yi masa nasiha a cikin hikima da kyakkyawan wa’azi, domin ya tuba ga
Allaah, ya mayar wa da waɗanda ya zalunta haƙƙoƙinsu, ko ya nemo yafiyarsu kafin
rasuwarsu ko rasuwarsa. Kuma lallai ya bar wannan sana’ar da yake yi, ya sauya
wacce ta fi ta alheri, gare shi da iyalinsa a duniya da makoma lahira.
Allaah ya datar da mu ga
aikata ayyukan na-gari.
Wal Laahu A’lam
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
+2348021117734
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.