In an fadi abin da Allah da Manzonsa (saw) suka fada, cewa: "Allah yana sama, ya daukaka a saman Al-arshinsa", sai 'Yan Bidi'a su ce:
Subhanallahi!
Ai ya yi wa Allah guri, ya sanya
makani ga Allah. Allah ba shi da guri, ba shi da makani.
Haba Malam!
To wa ya ce maka Allah ba shi da
guri, ba shi da makani?!
Mu dai a iya saninmu babu inda
Allah ya ce ba shi da guri da makani, haka Annabinsa (saw) bai kore masa guri
da makani ba. Amma Allah da Manzon nasa (saw) sun ce: Allah yana sama, ya
daukaka a saman Al-arshinsa.
To in wannan kake nufi da guri,
to Allah ya tabbatar ma kansa wannan din, amma bai kira shi da guri ko makani
ba.
Saboda haka wannar shubuha ce
maras ma'ana.
Imam Ibnu Abdilbarr Al-Malikiy ya
ce:
وأما
احتجاجهم لو كان في مكان لأشبه المخلوقات لأن ما أحاطت به الأمكنة واحتوته مخلوق فشيء
لا يلزم ولا معنى له لأنه عز وجل ليس كمثله شيء من خلقه ولا يقاس بشيء من بريته لا
يدرك بقياس ولا يقاس بالناس لا إله إلا هو كان قبل كل شيء ثم خلق الأمكنة والسموات
والأرض وما بينهما وهو الباقي بعد كل شيء وخالق كل شيء لا شريك له وقد قال المسلمون
وكل ذي عقل أنه لا يعقل كائن لا في مكان منا وما ليس في مكان فهو عدم
التمهيد
لما في الموطأ من المعاني والأسانيد (7/ 135)
"Amma kafa hujja da 'Yan
Bidi'a suke yi da cewa; da a ce Allah a wani guri yake da ya yi kama da
halittu, saboda duk abin da gurare suka kewaye shi kuma suka kunshe shi to shi
abin halitta ne, to wannan ba dole ba ne, kuma wannar magana ba ta da wata
ma'ana, saboda shi Allah babu wani abu da yake kama da shi a cikin halittarsa,
kuma ba a auna shi da wani abu na halittunsa, shi ba a saninsa ta hanyar aunawa
(Qiyasi da kwatance), ba a auna shi da mutane, babu abin bauta bisa cancanta
sai shi kadai, ya kasance tun kafin komai, sa'annan ya halicci guraren da
sammai da kassai da abin da ke tsakaninsu, kuma shi ne mai wanzuwa bayan komai,
kuma shi ne mahaliccin komai, ba shi da abokin tarayya. Kuma Musulmai da dukkan
wani mai hankali ya san cewa; hankali bai san wani abu da ya kasance ba a wani
guri ba daga cikinmu, kuma duk abin da ba ya wani guri to babu shi".
Saboda haka, kokarin kore
daukakar Allah a saman dukkan halittunsa da saman Al-arshinsa kokari ne na nuna
cewa; babu Allah. Saboda a hankalce ba zai yuwu a ce Allah yana ko'ina ba,
kamar yadda ba zai yiwu a ce Allah ba ya ko'ina ba. Allah yana sama, ya daukaka
a saman Al'arshinsa saman dukkan halittunsa.
~ Dr. Aliyu Muh'd Sani
30 July, 2018
Allah ya saukar da Alkur'ani ne a
matsayin littafi mai bayani kuma shiriya ga mutane, kuma littafin da ya kunshi
ilimin sanin Allah da siffofinsa da sanin girmansa da kamalarsa, da bayanin
Addininsa da Shari'arsa, shi ya sa ya zama littafi ne:
القرآن
الذي هو حجة الله على عباده والذي هو خير الكلام وأصدقه وأحسنه وأفصحه وهو الذي هدى
الله به عباده وجعله شفاء لما في الصدور وهدى ورحمة للمؤمنين ولم ينزل كتاب من السماء
أهدى منه ولا أحسن ولا أكمل
الصواعق
المرسلة في الرد على الجهمية والمعطلة (1/ 239)
"Alkur'ani wanda shi ne
hujjar Allah a kan bayinsa, wanda shi ne mafi alherin magana kuma mafi
gaskiyarta, kuma mafi kyaunta mafi fasaharta, kuma shi ne wanda Allah ya
shiryar da bayinsa da shi, ya sanya shi waraka ga abin da ke cikin zukata, kuma
shiriya da rahama ga Muminai. Allah bai saukar da littafi daga sama da ya kai
shi shiriya da kyau da kamala kamarsa ba".
Shi ya sa Alkur'ani ya sanar da
mu cewa:
1- Allah yana sama, ya daukaka a
saman Al'arshinsa.
2- Kuma yana da fiska.
3- Yana da hanaye biyu.
4- Yana magana.
5- Yana fushi.
A Sunna kuma:
6- Allah yana da kafa.
7- Yana dariya.
Da sauran siffofin Allah na
kamala, sawa'un na zati ne ko na aiki, siffofi da suka dace da girmansa, kuma
ba shi da makamanci a cikinsu, kuma shi ya san kamanninsu.
Amma abin mamaki sai ga 'Yan
Bidi'a suna siffanta Ahlus Sunna mabiya Salaf da cewa; su MUSHABBIHA ne, -wai-
suna TASHBIHI suna siffanta Allah da siffofin mutum, don kawai suna tabbatar da
siffofin da Allah ya tabattar ma kansa a cikin Alkur'ani, ko Annabinsa (saw) ya
tabbatar masa a cikin Sunna. Don kawai su suna kore su, saboda sun saba ma
ra'ayinsu.
Duk da cewa; su ma a tsakaninsu
kowace kungiya tana kiran 'yar uwarta da sunan "Mushabbiha" din.
'Yan Falsafa da yake ba sa
tabbatar da hakikanin samuwar Allah, suna kiran Mu'utazilawa da sunan
"Mushabbiha", don suna tabbatar ma Allah sifar "Al-qidam".
Mu'utazilawa kuma suna kiran
Asha'ira da Maturidiyya da sunan "Mushabbiha" da yake suna tabbatar
da siffofi 7 ko 8.
Su kuma Asha'ira suna kiran Ahlus
Sunna mabiya Salaf da sunan "Mushabbiha" saboda Salaf suna tabbatar
da dukkan siffofin da Allah ya tabbatar ma kansa a Alkur'ani, ko Manzonsa ya
tabbatar masa a cikin Hadisai tabbatattu.
To wasu daga cikinsu Hadisan
kawai suke jefawa a bola, su yi Tawilin Alkur'ani, amma abin mamaki har sai da
ya kai ga wasu daga cikinsu sun yi magana ta zindiqanci inda wani ya ce:
الأخذ
بظواهر الكتاب والسنة من أصول الكفر
حاشية
الصاوي على تفسير الجلالين (3/ 9)
"Riko da zahirin Alkur'ani
da Sunna yana cikin ginshikan kafirci".
Haka wani ma ya ce:
إن أصول
الكفر ستة... التمسك في أصول العقائد بمجرد ظواهر الكتاب والسنة من غير عَرْضٍ على
البراهين العقلية والقواطع الشرعية
حاشيه
الدسوقي على أم البراهين (ص: 252)
"Lallai ginshikan kafirci
guda shida ne... (na shida) riko da zahirin Alkur'ani da Sunna a Babin Aqeeda
ba tare da auna su a kan hankali -wai- da dalilan Shari'a ba".
Don haka ka ga su wadannan hatta
Alkur'anin ma kafirci yake koyarwa a ganinsu. Ba don komai suka fadi haka ba
sai don su ba za su iya bin Alkur'anin ba, hankula da ra'ayoyinsu kawai za su
bi, don haka duk abin da ya saba ma hankulansu a cikin Alkur'ani kafirci ne.
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.