𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam Musulmi zai iya auren ahlul kitab tana addininta yana Musuluncinsa?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
To ɗan'uwa
Allah maɗaukaki
ya halatta auren kamammu daga cikin ahlul-kitabi, wato Yahudu ko Nasara, kamar
yadda ya yi bayanin hakan a cikin suratul Ma'ida a aya mai lamba ta 5:
الْيَوْمَ أُحِلَّ لَكُمُ الطَّيِّبَاتُ وَطَعَامُ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ حِلٌّ لَّكُمْ وَطَعَامُكُمْ حِلٌّ لَّهُمْ وَالْمُحْصَنَاتُ مِنَ الْمُؤْمِنَاتِ وَالْمُحْصَنَاتُ مِنَ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ مِن قَبْلِكُمْ إِذَا آتَيْتُمُوهُنَّ أُجُورَهُنَّ مُحْصِنِينَ غَيْرَ مُسَافِحِينَ وَلَا مُتَّخِذِي أَخْدَانٍ وَمَن يَكْفُرْ بِالْإِيمَانِ فَقَدْ حَبِطَ عَمَلُهُ وَهُوَ فِي الْآخِرَةِ مِنَ الْخَاسِرِينَ
A yau an halatta muku
abũbuwa mãsu dãɗi kuma abincin waɗanda
aka bai wa Littãfi halal ne a gare ku, kuma abincinku halal ne a gare su, da
mãtã mãsu kãmun kai daga muminai da mãtã 'yã'ya daga waɗanda
aka bai wa Littãfi a gabãninku idan kun je musu da sadãkõkinsu, kuna mãsu yin
aure, ba masu yin zina ba, kuma bã mãsu riƙon
abõkai ba. Kuma wanda ya kãfirta da ĩmãni to, lalle ne aikinsa yã ɓãci,
kuma shĩ, a cikin Lãhira, yanã daga mãsu hasãra.
Kuma an samu wasu daga cikin
sahabai, sun aure su kamar Usman ɗan
Affan - halifa na uku a musulunci- ya auri Banasariya, haka Dalhatu ɗan
Ubaidillah ya auri Banasariya, sannan Shi ma Huzaifa masanin sirrin Annabi
Sallallahu Alaihi Wasallam ya auri Bayahudiya, Allah ya kara musu yarda. Duba:
Ahkamu-ahlizzimah 2\794.
Saidai malaman wannan
zamanin suna cewa, abin da ya fi shi ne rashin auren Ahlul-kitab a halin yanzu,
saboda yadda zamani ya canza, domin da yawa idan mijinsu musulmi ya mutu yaran
suna zama Kirista, kai wani lokacin ko da sakinta ya yi za ta iya guduwa da
yaran, sannan zai yi wuya ka samu waɗanda
ba su taɓa
zina ba acikinsu.
Wasu kasashen kuma idan za
ka auri Kirista daga cikinsu dole sai ka yarda da dokokin kasarsu, a lokuta da
yawa kuma za ka samu dokokin sun Saɓawa
ka'idojin musulunci.
Allah ne mafi sani.
Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.