Wato fa so ake a rena wa Ahlus Sunna hankali, a tilasta su suna kallon Annabi (saw) ta irin yadda Sufaye suke kallonsa. Dole su koma yin magana game da Annabi (saw) irin yadda Sufaye suke yi.
Sai ta yadda Sufaye suke so Ahlus
Sunna zai faɗi magana
game da Annabi (saw)!
Alhali yana daga cikin manyan
abubuwan da suka raba tsakanin Ahlus Sunna da Sufaye akwai guluwwi a haƙƙin
Annabi (saw).
Yaya za a zo ana hukunta mu da
"muhallin niza'i", abin da a kansa muke saɓani da su?!
Idan mun ce:
- Ba a neman taimakon Annabi
(saw),
- Ba a neman agajinsa,
- Ba a tawassuli da shi, ko
darajarsa, ko alfarmatsa, ko, ko,, ko,,,
Sai a ce: mun yi "su'ul
adabi" wa Annabi (saw)!
Alhali aikata ɗaya daga cikin waɗannan yana warware Addinin
da Annabi (saw) ya zo da shi, na Tauhidi; kaɗaita
Allah da bauta!
Idan mun ce: Annabi (saw) ya
mutu, sai a ce: mun yi "su'ul adabi", alhali har cikin Alƙur'ani
an ce Annabi (saw) ya mutu!
Sayyidina Abubakar (ra) ya ce:
Annabi (saw) ya mutu!
Sahabbai masu yawa sun ce: Annabi
(saw) ya mutu!
Idan mun ce: Annabi (saw) ba shi
da siffa kaza, da siffa kaza, saboda dabbobi ma suna da siffar, ko Arna suna da
ita, sai a ce: mun yi "su'ul adabi", alhali kore siffar muke yi,
saboda ba ta tabbata gare shi ba, kuma ko ta tabbata ba "khususiyyarsa"
ba ce!
Ta yaya za a zo ana hukunta Ahlus
Sunna da Aƙidar
ƴan
bidi'a, na guluwwi a haƙƙin Annabi (saw), abin da a kansa Ahlus Sunna suke husuma da
su?!
Don haka ba Sufaye ne za su nuna
mana yadda za mu yi magana game da Annabi (saw) ba.
Mu mun fi su sanin Annabi (saw)!
Mun fi su sonsa!
Mun fi su girmama shi!
Mu mabiyansa!
Shi ya sa muke riƙo da
Sunnarsa, muke aiki da Hadisansa!
Mu a wajenmu, Sufaye ba su san
Annabi (saw) ba!
Ba sa binsa!
Ba sa girmama shi!
Suna guluwwi a haƙƙinsa,
wanda hakan ya sa suka wayi gari cikin masu yi masa jafa'i!
Suna dai raya sonsa kawai, amma
ba soyayyar a ƙasa!
✍ Dr.
Aliyu Muh'd Sani (H)
Ta'addancin Makiya a kan Ibnu
Taimiyya
A gaskiya za ka dade ba ka ga
zalunci da ta'addanci irin na makiya Ibnu Taimiyya ba.
Ibnu Sayyidin Nas ya yi tarjama
wa Ibnu Taimiyya, Ibnu Hajar ya nakalto ta a cikin littafinsa
"al-Durar", sai ya ba da labarin cewa:
Ibnu Taimiyya sha-kundum ne a
ilimi, don kuwa ya yi fintinkau ga malaman kowane fanni na ilimi, wanda hakan
ya sa Malaman zamaninsa suke yi masa hasada, inda ya ce:
((برز في
كل فن على أبناء جنسه، ولم تر عين من رآه مثله، ولا رأت عينه مثل نفسه، كان يتكلم في
التفسير فيحضر مجلسه الجم الغفير ويردون من بحره العذب النمير يرتعون من ريع فضله في
روضة وغدير إلى أن دب إليه من أهل بلده داء الحسد وألب أهل النظر منهم على ما ينتقد
عليه من أمور المعتقد...)).
الدرر
الكامنة في أعيان المائة الثامنة (1/ 183 - 184)
((Ibnu Taimiyya ya yi fice a
kowane fanni na ilimi, har ya tsere wa Malaman zamaninsa. Duk wanda ya taba
ganinsa to idonsa bai taba ganin wani mutum kamarsa ba. Kai, hatta shi kansa
Ibnu Taimiyyan, idonsa bai taba ganin kamarsa ba. Ya kasance yana yin darasin
Tafsirin Alkur'ani, dandazon mutane masu yawan gaske suna halartan majalisin
nasa, suna sha daga tekun iliminsa mai dadi mai amfani, suna kiwo a gonar baiwa
da Allah ya yi masa na ilimi, a dausayi da kududdufi, har sai da cutar hasada
ta silalo ta kulli zukutan Malaman garinsu, sai kuwa Malaman suka tunzura
mutane a kansa, A KAN MAS'ALOLIN AKIDA da suke sabani da shi a kansu…)).
To tun daga nan suka kafa masa
kahon zuka, sai cutarwa kala-kala, mugunta iri-iri, suka rinka jifansa da
ja'iran tuhumomi daban-daban, suna yanke hukunce-hukunce a kansa, wasu suka
jefe shi da Bidi'a, wasu suka kafirta shi. Ba don ya saba Alkur'ani ko Sunna ko
hanyar Salaf ba, a'a, don ya saba Bidi'o'insu na Sufanci da Ash'ariyyanci.
Ai ba su tsaya a nan ba, sai da
suka fara shige da fice wajen sarakuna suna kai kararsa. Suka tunzura 'yan daba
a kansa suka cutar da shi. Har aka kama shi aka jefa shi kurkuku, aka daure
shi. Malaman nan ba su tsaya a nan ba – da ma su ne Alkalan -, suka yi ta
kokarin halasta jininsa da yanke hukuncin kisa a kansa. Amma daga karshe Allah
ya maida kaidinsu da makircinsu kansu.
Haka ya yi ta fama tsawon
rayuwarsa, daga wannar fitina zuwa waccar. Har karshe wani Alkali daga cikin
masu husuma da shi ya daure shi, wanda a cikin kurkukun Allah ya karbi
rayuwarsa. Allah ya kara haskaka kabarinsa, ya sa dausayin gidan Aljanna ne.
Wannan shi ne irin ta'addancin da
makiya Ibnu Taimiyya suka yi a kansa, suka bidi'antar da shi ba tare da hakki
ba, suka kafirta shi ba bisa hujja ba. Amma tun wancan lokacin har zuwa yau,
makiyansa suna ta kururuwa, suna sukarsa da cewa; yana kafirta Musulmi, alhali
ya fi kowa nisantar kafirta Musulmi, da hani a kan haka ba bisa hujja ba. Shi
ya sa ya ce:
((أني دائما
- ومن جالسني يعلم ذلك مني - أني من أعظم الناس نهيا عن أن ينسب معين إلى تكفير وتفسيق
ومعصية، إلا إذا علم أنه قد قامت عليه الحجة الرسالية التي من خالفها كان كافرا تارة
وفاسقا أخرى وعاصيا أخرى وإني أقرر أن الله قد غفر لهذه الأمة خطأها: وذلك يعم الخطأ
في المسائل الخبرية القولية والمسائل العملية)).
مجموع
الفتاوى (3/ 229)
((Lallai ni a kullum - kuma duk
wanda ya zauna da ni ya san haka daga gare ni - ina cikin wadanda suka fi kowa
hani a kan kafirta Mutum Musulmi ayyananne, ko fasikantar da shi, ko danganta
shi ga sabo, sai dai idan hujjar Shari'a ta tsayu a kansa, hujjar da duk wanda
ya saba mata to ya zama kafiri, ko fasiki ko mai sabo. Kuma ni ina tabbatar da
cewa; Allah ya gafarta ma wannar al'umma kuskurenta, kuma wannan ya shafi
kowane irin kuskure, sawa'un a Mas'aloli na Akida ne ko kuma Mas'aloli na Fiqhu
ne)).
Kuma da wannan za ka fahimci
girman kuskuren masu magudi suna kamanta wasu 'yan gwagwarmayar siyasa da Ibnu
Taimiyya, don kawai an daure su a kurkuku, ko don wasu Gomnatoci sun kashe su,
alhali Manhajinsu ya yi hanun riga da Manhajin Ibnu Taimiyya, gwagwarmayar da
suka yi ba irin Jihadin da Ibnu Taimiyya ya yi ba ne. Babban misali a kan haka
shi ne yadda Mabiya Sayyid Qutub suke kamanta shi da Ibnu Taimiyya, alhali shi
Ibnu Taimiyya Manhajinsa na Salaf ne, shirka da bidi'o'i ya yaka, kuma ya yaki
Manhajin Khawarijawa na kafirta al'ummar Musulmi da tawaye wa shugabanni da
ta'addanci a kan al'ummar ta Musulmi. Shi kuma Sayyid Qutub Manhajinsa na
Khwarijawa ne, babu abin da ya koyar face kafirta Musulmai da fito-na-fito da
shugabannin Musulmai, da fita daga cikin al'ummar.
Saboda haka Makiya Ibnu Taimiyya
su suka fi cancanta a kira su masu kafirta Musulmi ba shi ba. Su kuma Mabiya
Sayyid Qutub, su dena cakuda karya da gaskiya, Sayyid Qutub bai hada hanya da
Ibnu Taimiyya ba, kwata-kwata Manhajinsu ba iri daya ba ne.
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.