Shirye-shirye sun kankama na gudanar da Ranar Marubuta Hausa ta Duniya a wannan shekara 2025 karo na uku a Dutse, babban birnin Jihar Jigawa. Taron zai gudana a ƙarƙashin taken: “Marubuta a Karni na 21: Kalubalen Tsaro da Tattalin Arziki”.
Taron na bana
zai kasance wata babbar dama ga marubuta daga sassan duniya daban-daban domin
tattauna rawar da adabin Hausa ke takawa wajen fuskantar manyan ƙalubale
na tsaro da tattalin arziki da ke addabar ƙasashe da al’ummomi.
Kuma zai ƙarfafa
haɗin guiwa tsakanin
marubuta da gwamnati, da ƙungiyoyi wajen samar da mafita ga matsalolin tsaro da tattalin
arziƙi.
Zai bai wa marubuta, musamman matasa, damar musayar ilimi da dabaru na amfani
da rubutu a matsayin makamin ci gaban ƙasa. Zai taimaka wajen ɗaukaka harshen Hausa da
al’adunsa a idon duniya.
Domin tabbatar
da tasirin taron, an gayyato ƙwararru daga fannoni daban-daban musamman
fasahar zamani (AI), tsaro da tattalin arziki domin gabatar da bita. Wanda zai
taimaka wajen samar da sabbin fahimta ga marubuta kan yadda za su yi amfani da
AI wajen rubuce-rubuce da faɗakarwa.
Sannan za a
wayar da kan marubuta kan tasirin tsaro da yadda za su bayar da gudummawa wajen
gina zaman lafiya.
Koyar da
marubuta dabarun tattalin arziki da dogaro da kai domin su zama ginshiƙan ci
gaban ƙasa
na daga cikin abinda taron na bana zai maida hankali.
Kamar yadda
aka sani ne marubuta tun tarihi suna taka muhimmiyar rawa wajen gina al’umma.
Misalai a Afirka ta Kudu, rubuce-rubucen marubuta sun taimaka wajen wayar da
kai kan ’yanci da adalci. A Indiya, marubuta irin su Tagore sun yi tasiri wajen
tabbatar da ’yancin kai. A Nijeriya kuma, marubuta a shekarun baya sun kasance
muryar jama’a wajen ilmantarwa da nishadantarwa, da faɗakarwa.
Kwamitin
shirya taron na kira ga gwamnati a matakai daban-daban da hukumomi da NGOs, da
kamfanoni da su mara wa taron baya domin nasararsa. Nasarar taron ba wai ta
marubuta kaɗai ba ce,
nasara ce ta al’umma baki ɗaya.
Ranar Marubuta
Hausa ta Duniya a Dutse za ta kasance tarihi wajen ƙara ɗaukaka harshen Hausa da
kuma tabbatar da cewa marubuta suna daga cikin ginshiƙan magance matsalolin
tsaro da tattalin arziki.
Abdulrahman
Aliyu Ph.D
Sakataren
kwamitin shirya taron

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.