Cite this article as: Ɗangulbi A. R. & Kurawa H. M. (2024). Tauhidi a Wasu Waƙoƙin Siyasar Zamani: Nazarin Habaici-Sakayau Domin Kafa Shugabanci Nagari. Proceedings of International Conference on Rethinking Security through the lens of Humanities for Sustainable National Development Interdisciplinary Perspectives. Pp. 379-385.
TAUHIDI A WASU WAƘOƘIN SIYASAR ZAMANI: NAZARIN
HABAICI-SAKAYAU DOMIN KAFA SHUGABANCI NAGARI
Na
Aliyu Rabi’u Ɗangulbi, (Ph.D)
Sashen Harsuna da Al’adu
Jami’ar Tarayya Gusau
Da
Halima Mansur Kurawa
Sashen Harsuna da Al’adu
Jami’ar Tarayya Gusau
Tsakure: Kodayaushe aka yi
maganar shugabanci nagari, abin da zai zo a zukatan masu karatu ko sauraro, shi
ne, wane ne shugaba nagari? Shugaba nagari shi ne, mutum mai tsoron Allah da
tausayin na ƙasa da shi da nuna gaskiya da riƙon amana ga shugabancin al’umma da
aka ɗora masa. Idan waɗannnan abubuwa suka haɗu ga mutum, to ana kyautata masa
zaton ya kasance shugaba nagari, wanda zai yi shugabanci cikin adalci da ke
haifar da zaman lafiya da haɓaka tsaro. Wannan muƙala mai suna, ‘Tauhidi a Wasu
Waƙoƙin Siyasar Zamani: Nazarin Habaici-Sakayau Domin Kafa Shugabanci nagari’
ta yi bayani ne a kan rawar da ‘habaici-sakayau’, yake takawa wajen faɗakar da
‘yan siyasa domin su kyautata ɗabi’unsu da halayensu kuma su zama masu tsoron
Allah da yarda da ƙaddara ta alheri ko sharri kasancewar su ne tushen samar da
zaman lafiya da tsaro a cikin al’umma. An yi amfani da wasu waƙoƙin siyasar
zamani kamar waƙar “Yau Nijeriya riƙo sai mai gaskiya, Baba Buhari kai muke so
Nijeriya” ta Ibrahim Yala Hayin Banki da waƙar “‘Yan Nijeriya mu fito mu yi
P.D.P. ta gyara ƙasata” ta Shu’aibu ‘Yan Medi Ƙaraye da kuma waƙar Ɗan takarar
kujerar Gwamna a jihar Neja Mu’azu Bawa Rijau ta Kabiru Yahaya Kilasik, da ta
“Munafuccin Karen Ruwa” ta Garba Gashuwa Kano, wajen isar da saƙon wannan
muƙala tare da hira da masu ruwa-da-tsaki a wannan fanni. Haka kuma, Muƙalar ta
fito da sakamakon da ke yin nuni ga illar da tsafe-tsafe da zuwa wurin bokaye
da ‘yan bori da malaman tsibbu suke yi wajen neman biyan wata buƙata ta siyasa
ko wani shugabanci na al’umma. Yin haka ya saɓa wa koyarwar addinin Musulunci
da aƙidar tauhidi. Saboda haka, mawaƙan siyasar zamani suna amfani da
habaici-sakayau wajen faɗakar da ‘yan siyasa da sauran al’umma a kan illolin da
ke tattare da bin ƙazamun hanyoyi wajen neman muƙaman siyasa da sauransu.
Muhimman Kalmomi:
Tauhidi, Waƙa, Habaici, Sakayau, Siyasa, Shugabanci, Tushe, Kafa
1.0 Gabatarwa
Wannan muƙala wata faɗakarwa ce da ke jawo
hankalin ‘yan siyasa da sauran mutane da duk wani mai neman biyan wata buƙata
ta duniya, ya neme ta wurin Allah Mahaliccin kowa, mai kowa mai komai, maimakon
bin ƙazamun hanyoyin tsafe-tsafe da bokaye da ‘yan bori da malaman tsibbu. Mutane,
musamman ‘yan siyasa da masu neman kuɗi da mulki kowane iri suna zuwa wurin
bokaye da masu tsafe-tsafe da ‘yan bori da bin sauran hanyoyin da ba su dace da
shari’a ba a lokacin da suke son tsayawa takarar wata kujera ta siyasa ko kuɗi
ko wata sarauta ta gargajiya. Waɗannan mutane suna yin imani da bin irin waɗannan
hanyoyi bisa ga yarda da cewa, idan har suka bi irin waɗannan hanyoyi,
buƙatunsu za su biya. Tauhidi shi ne dogara ga Allah ga dukkan al’amuran rayuwa
wajen gudanar da harkokin yau-da-kullum. Wannan tauhidi yana taimaka wa mutum
ya ƙara yarda da Allah, da imani da ƙaddara ta alheri da ta sharri; domin kuwa,
su ne tushen samar da shugabanni nagari masu gaskiya da riƙon amana a tsarin
shugabanci na sarautar gargajiya da mulkin siyasa da ake magana a kansa.
Mawaƙan siyasa na zamani malamai ne masu hikima da hangen nesa wajen yin amfani
da basirarsu wajen jawo hankalin mutane cikin waƙoƙinsu ta hanyar amfani da
habaici-sakayau domin su ji, kuma su gyara kurakuransu. Duk wanda ya nemi biyan
wata buƙata ta duniya ta hanyar tsafi ko bokaye da saurnsu, babu shakka ya saɓa
wa aƙidar tauhidi da addinin Musulunci ya yarda da shi. Saboda haka ne ya sa
mawaƙan siyasa suke jawo hankalin ‘yan siyasa da su koma ga hanyar gaskiya ta
yarda da ƙaddara ta alheri da akasin haka, domin su zama shugabannin al’umma da
za a iya alfahari da su. Habaici kuwa, wata magana ce mai ɓoyayyar ma’ana wadda
idan mutum bai san dalilin yin ta ba, ba zai fahimci inda maganar ta nufa ba.
Mawaƙan siyasa suna amfani da habaici-sakayau su yi wa al’umma kashedi ko gargaɗi
ga barin aikata wani abin da bai dace ba, ko wanda ya saɓa wa tunani da
hankalin ɗan Adam. Habaici-sakayau nan, shi ne wanda mawaƙi ke furtawa ta
hanyar amfani da kalmomin lamirin sakaya zance, kamar su ‘wani,’ wata’, wane,
wance da su wane, domin sakaya sunan wanda yake yi wa habaicin a zukatan
al’umma.
1.2 Habaici
Habaici wata magana ce da ake furtawa zuwa ga wani mutum
ko wasu mutane a matsayin hannunka-mai–sanda ko shaguɓe ko gugar-zana don wanda
aka yi wa, ya ji kuma ya gyara halayensa ba tare da an ambaci sunansa ba. Masana
da manazarta sun yi bayanai daban-daban dangane da ma’anar habaici. Bergery
(1934:431) da Ɗangambo (1984:41) da
Ɗangulbi (2013:95) da Malumfashi da wasu (2014: 24), sai Umar (1987) da Koko
(1989) da Swift ed (2023) da kuma Yahya (1997), dukkansu sun yi ittifaƙi a kan
cewa, “habaici magana ce mai ɓoyayyar manufa”. Watau akan yi magana ce gajeruwa
da nufin isar da wani saƙo ko wani abu ga wanda aka yi maganar domin sa.Wato
akan yi habaici a cikin sigar karin magana don a gargaɗi wani mutum ko a yi
masa hannunka-mai-sanda ko shaguɓe ga wani abu maras kyau da yake aikatawa
domin ya ji, ya daina, kuma ya yi ƙoƙarin gyara ɗabi’unsa da ake zargin sa da
su. Dangulbi (2013:95) ya ce, “habaici wani kalami ne da ake furtawa a taƙaice
a matsayin wanka-da–jirwaye, ko gugar-zana domin a musguna wa wani mutum ko a
faɗakar da shi a kan wani ko wasu miyagun ayyuka ko ɗabi’u da yake aikatawa waɗanda
suka saɓa wa buƙatar al’ummar Hausawa da yake zaune tare da su.” Ya ƙara da
cewa, ana amfani da karin magana a gina habaici don a gargaɗi mutum ya gyara
halayensa. Wannan ya nuna cewa, ita karin magana ana amfani da ita a gargaɗi
masu aikata munanan halaye, musamman shugabannin siyasa ko wasu masu riƙe da
muƙaman sarauta ko neman wani matsayi na siyasa. Haka kuma, ana amfani da
kalmomin lamirin suna kamar, ni, kai, ke, ku, su, mu, wani, wata, wasu, wanda,
wadda, waɗanda domin a yi wa mutum ko mutane shaguɓe ko hannunka-mai-sanda.
Sannan ana yin amfani da lamiran suna na gama-gari kamar kowa, kowanne, kowace,
waɗanda ake magana a kansa ko a kansu da sauransu. Har wa yau, akwai kalmomin
tsigalau kamar ɗan, ‘yar da ‘yan waɗanda ake gina habaici da su domin a bayyana
wani hali ko ɗabi’a ko sifa ta wanda ake yi wa habaicin. Bugu da ƙari, akwai
kalmomi kamar: ‘o’o, ‘a’, ‘an’, ‘in,’mai’ ‘masu’ da sauransu. Duk waɗannan
kalmomi da mawaƙan Hausa sukan yi amfani da su suna gina habaici cikin
waƙoƙinsu domin su gargaɗi ko wayar wa ‘yan siyasa da sauran masu sauraron su
kai. Waɗannan kalmomin lamirai sun taka
muhimmiyar rawa a fagen isar da saƙo na gyara ɗabi’un ‘yan siyasar Nijeriya.
1.3 Habaici-Sakayau
A wannan nau’in habaici-sakayau, akan yi
amfani da kalmomin sakaya magana ta hanyar ɓoye sunan wanda ake yi wa habaici,
a bar mutane su yanke wa kansu hukunci wajen ƙoƙarin gano wanda ake yi wa
habaicin. Galadanci (1976) da (Bagari 1986) sun ce, ana amfani da kalmomin
mafayyaci kaikaitau da wakilin suna kaikaitau kamar haka: Wani, wata,
wasu, waanѐ, wancѐ, ko waɗansu,
domin a gina habaici zuwa ga shugabanni ko ‘yan siyasa ko jam’iyyar siyasa ko ɗan
adawa wanda ba a son a ambaci sunansa ƙarara domin a kauce wa tashin hankali
tsakanin masu saurare da ‘ya’yan jam’iyyar wanda ake yi wa habaici. Siyasa abu
ce mai tafiya da ra’ayi da kuma zamani, saboda haka, kowane ɗan siyasa yana
ƙoƙari ya ga cewa, tafiyarsa ta yi daidai da zamanin da ake ciki ta hanyar yin
abubuwan da zamani da mutanen zamani suke buƙata. Habaici yakan iya sa masoyan ɗan
takara ko ɗan siyasa su ƙaurace wa zaɓen wanda ɗabi’unsa da halayensa suka saɓa
wa aƙidar addini da tauhidi da kuma manufar jam’iyyarsu ko al’ummarsu. Sannan
sukan dubi matsayin shugaba ko ɗan siyasar da ya kasa aiwatar da mulki daidai
da tafiyar zamani saboda rashin ilimi ko ƙwarewa ga hulɗa da jama’a, ko rashin ɗaukar
ƙaddara wajen neman muƙami, sai su jefe shi da habaici da ya yi daidai da
halayensa da ɗabi’unsa a bayyane domin ya ji, kuma ya gyara.
Misali, Ibrahim Yala yana cewa:
Duk wani
wanda ba ya jin tsoran Rabbana,
To mun daina
girmama shi ya cuta mana,
Mai rawani da
jiniya Allah isar mana,
Za mu
buga da ku bana faɗin Nijeriya.
(Ibrahim Yala:
Waƙar APP/ANPP 2003).
Tsoron Allah da yarda da ƙaddara ta alheri ko
sharri ɗabi’a ce mai kyau da ke tabbatar da mutunci da kyawawan ɗabi’un ɗan
siyasa ko shugaba. Idan shugaba ya kasance yana da irin waɗannan halaye, to za
a same shi mutum mai gaskiya da adalci, waɗanda su ne tushen samar da
shugabanci nagari. Idan aka samu shugaba wanda ba ya da imani da tsoron Allah,
to talakawansa za su bijire masa, komai kwarjininsa a kujerar mulki. Saboda
haka ne ya sa mawaƙan siyasa sukan yi amfani da habaici-sakayau su jawo hankalin
talakawa da su ƙaurace wa irin wannan shugaba da ba ya da tsoron Allah wajen
jagorancin jama’a. Yana da wuya a sami shugaba maras tsoron Allah ya zama mai
adalci, domin yakan kasance mai danne ko take haƙƙin jama’arsa. Sannan kuma, ya
tursasa wa jama’arsa su aikata abin da ba daidai ba ta hanyar amfani da ƙarfin
mulki. Wannan dalilin ne yakan taimaka wajen zaburar da talakawa su bijire wa
shugabanni tare da nuna rashin girmawa a gare su.
1.4 Bin Bokaye da Malaman Tsibbu
Wannan ɗabi’a ta yarda da bokaye da malaman
tsibbu ta zama ruwan dare game-duniya a tsakanin ‘yan siyasa da masu neman
muƙaman siyasa ko sarautun gargajiya a wannan zamani. Lokuta da dama za ka sami
gidajen bokaye da malaman tsibbu da ‘yan bori sun cika da mutane masu neman a
taimaka masu su ci zaɓe ko su sami nasarar karya abokan hamayyarsu. Bokaye da
malaman tsibbu suna amfani da wannan dama su cusa aƙidar imani da
sihirce-sihirce da tsafe-tsafe a zukatan ‘yan siyasa ko masu neman muƙami,
domin su saka su mugunyar hanya ta barin Ubangijinsu lokacin da suke neman
biyan wata buƙata.’Yan siyasa suna zaton bin wannan ƙazamar hanya ita ce ta fi
saurin biya masu da buƙatunsu. Wannan aƙida ta saɓa wa tauhidi, domin Allah shi
kaɗai Yake biya wa kowa buƙatarsa bisa ga ƙudirar ƙarfin ikonsa. Saboda haka,
ya wajaba ‘yan siyasa su sani cewa, duk lokacin da suka buƙaci tsayawa wata
takara ta siyasa, to su nemi biyan buƙata ga Allah don shi kaɗai ne Yake iya
biya masu dukan wata buƙata ba bokaye ko malaman tsibbu ko ‘yan bori ba. Bisa
ga wannan dalili ne ya sa mawaƙan siyasa suke sukar ‘yan siyasa da ba su da
tauhidi domin su jawo hankalinsu su gane kuskurensu, sannan su dawo ga hanyar
gaskiya domin su tsira da imaninsu da mutuncinsu a idon duniya. Misali,
Shu’aibu ‘Yar Medi Ƙaraye ya yi wa wani ɗan takarar kujerar gwamna habaici,
wanda ya tafi wurin bokaye da malaman tsibbu don su taimaka masa ya ci zaɓe.
Mawaƙin yana cewa:
Wani ɗan takarar wasu ya saɓa laya ba a kada shi,
Wai sai dole ya yi Gwamna wataƙil boka ya duba
shi,
Ba sa’a gare shi ba PDP ce za ta kada shi,
Ran zaɓe mu ɗau inuwar lema domin a gyara
ƙasata.
(Shu’aibu ‘Yar Medi: Waƙar PDP).
Al’adar zuwa wurin bokaye ko malaman tsibbu ta
yi ƙamari a zukatan ‘yan siyasa. Saboda haka, a duk lokacin da siyasa ta kunno
kai za ka taras masu neman a tsayar da su takara suna ta kai-kawo wajen bokaye
da malaman tsibbu domin neman sa’a ga buƙatar da suka sanya a gaba. Wannan
kuwa, ɗabi’a ce ta rashin tauhidi, wato maguzanci da Hausawa ‘yan siyasa suka
rungume ta hannu bi-biyu domin samun biyan buƙatunsu na siyasa.Wato, ba su
yarda da cewa, Allah shi Yake ba da mulki ga wanda yake so, kuma Ya karɓe mulki
ga wanda yake so ba. Irin waɗannan ‘yan siyasa ne mawaƙan siyasar zamani suke
suka ta hanyar amfani da habaici don su jawo hankalinsu su koma ga Allah a duk
lokacin da suke neman wata buƙata. Wannan ɗabi’a ta zuwa wurin bokaye da
malaman tsibbu ta sanya wani ɗan takarar kujerar Gwamna ya tafi neman sa’a, sai
aka ba shi laya da nufin shi zai kada abokin takararsa. Amma hakan bai sa ya
sami nasara ba. Duba da wannan rashin tawakkali da rashin tauhidi da wannan ɗan
takara ya nuna wajen neman kujerar Gwamna ta hanyar zuwa ga bokaye don neman
sa’a ya sa wannan mawaƙin ya soki ɗan takarar Gwamnan da habaici kamar yadda ya
gabata a sama. Wato inda yake cewa, wani ɗan takarar wasu ya saɓa laya ba a
kada shi, amma mawaƙin ya nuna masa cewa, ƙarya ne Jam’iyyar PDP ce za ta kada
shi. Haka kuma, abin ya kasance a lokacin da aka yi zaɓe a jihar Kano lokacin
Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso.
Haka shi ma da yake yi wa wani ɗan takara
habaici dangane da rashin yarda da Allah shi kaɗai Yake ba da mulki ga wanda ya
so, a lokacin da ya so, mawaƙi Garba Gashuwa, ya yi habaici ga wasu ‘yan siyasa
waɗanda suka zama azzalumai da rashin yarda da koyarwar addinin musulunci suka
rungumi hanyar bokaye wajen neman muƙami idan suka hau mulki sai su sa zalunci
a gaba. Ga abin da yake cewa:
Wasu
ba su tsoron zalunci,
Ba
sa gudun keta mutunci
Da
rashin sani ga bambanci,
Ko
kuma su shirya munafunci
Da
rusa hanyar addini
(Garba Gashuwa: Waƙar APP, ‘munafuccin karen
ruwa’).
A nan mawaƙin ya yi amfani da azancin magana na habaici
ga wasu ‘yan takara na babbar jam’iyyar adawa ta PDP, inda ya alaƙanta su da
zalunci a lamarin tafiyar da mulki ga al’umma. Haka kuma, ya
siffanta su da masu keta mutuncin mutane ta hanyoyi daban-daban domin cimma
manufofinsu na siyasa. Bugu
da ƙari, mawaƙi ya ƙara siffanta abokan adawar jam’iyyarsa da rashin sani
(Jahilci) da kuma zuwa ga bokaye
da nuna bambanci waɗanda duk gazawa ce ga mai mulki. Bayan waɗannan misalai a ɗango
na huɗu da na biyar, mawaƙin ya bayyana cewa, su waɗannan abokan hamayyar suna
shirya munafunci da kuma rusa koyarwar addinin
musulunci ta hanyar zuwa wurin bokaye don neman buƙata. Yana isar da saƙon shi ne ga Hausawa musulmi don su ƙyamaci
jam’iyyar PDP, su zaɓi jam’iyyarsa ta APP, kamar
yadda mawaƙin ya bayyana cewa, su
waɗancan ‘yan siyasa ba nagartattun
mutane ne ba.
Mawaƙin yana gargaɗin mai neman muƙami ta hanar bin
bokaye da malaman tsibbu da ya bari ya dawo wa hanyar Allah domin ya rabauta
daga shiga wutar jahannama. Sakin hanyar Allah wajen neman buƙata ya saɓa wa
tauhidi, shi ya sa Garba Gashuwa yake jan hankalin ‘yan siyasa da su bar bin
hanyar bokaye, domin bin bokaye barin hanyar ni’ima ce, wato hanyar shiga
aljanna. Daga ƙarshe, ya rufe da baitinsa, inda yake gargaɗin ‘yan siyasa da su
tambayi tarihin magabata, waɗanda suka saɓa wa hanyar tauhidi suka bi hanyar
bokaye, yaya ƙarshensu ya kasance? Wuta ce makomarsu saboda sun saɓa wa
tauhidi, sun bar Allah, wanda shi ne Yake ba da mulki ga wanda ya so, suka
shiga hanyar tsafi kuma suka halaka.
1.5 Tsafe-Tsafe da shiga Ƙungiyoyin Asiri
Tsafi yana nufin yi wa iskoki ko rafanai hidima domin
neman yardarsu su biya wa wanda yake hulɗa da su buƙatarsa. Bunza (2009) ya
bayyana tsafi da cewa, “yi wa wani abu da ba Allah ba hidima domin neman biyan
buƙata ta duniya”. Ya ƙara da cewa, yanke-yanke da watsa wani abinci a gidan
Tururuwa ko a mararrabar hanya ko gindin wani icce ko bishiya wani salo ne na
hulɗa da aljannu domin su taimaka wa wanda ya nemi biyan buƙata daga gare su.
Bergery (1933/34) akwai dalilai da dama da sukan sa mutane su riƙa bin hanyoyin
tsafe-tsafe don neman biyan wata buƙata ta duniya. Misali:
1.5.1 Jahilci
Jahilci yana nufin rashin ilimi na yadda
abubuwa suke gudana na harkokin rayuwar yau-da-kullum. Wato, duk mutumin da ba
shi da ilimin addini da na zamani ana kiran sa jahili. Shi ma da yake jefa
habaici ga wani ɗan takarar kujerar Gwamna a jihar Neja, wanda ya saki hanyar
Allah don ya sami nasarar lashe zaɓe, amma ba shi da ilimin addini da na boko.
Sai Kabiru Kilasik ya jefe shi da kalmar habaici-sakayau inda yake cewa:
Ga wani na son Gwamnan Neja,
amma an ce bai da boko,
Ba Arabiya ba ya da boko sai girman kai nan na
iko,
Ya ce lallai sai ya yi Gwamna, shi tafiyatai
babu tsaiko,
Lallai ka ebo ta da faɗi, wane da kai nai zai
yi raki.
(Kabiru Kilasik: Waƙar ‘Neja ga mafita’).
Babu shakka rashin ilimi yana daga cikin
dalilan da ke haifar da girman kai ga kowane mutum, balle ma wanda yake neman
wani muhimmin matsayi a cikin al’umma. Rashin ilimi shi ke haifar da dogon
tunanin faɗawa cikin hanyar da ba ta dace ba wajen neman wani matsayi na siyasa
ko na sarauta. Mai ilimi yakan tsaya ya auna ya ga amfani ko illar abin da yake
so kafin ya tsunduma gadan-gadan wajen neman abin, sannan ya dogara ga Allah
lokacin da yake neman sa ta hanyar halal domin ya tsira da imaninsa. Haka nan
ma Kabiru Yahaya Kilasik yana cewa:
Wane buku ne ko kwaɗɗo don na gan shi yana ta
ciccika,
Haka nan yake tun can farko da shi da matatai
dakan-ɗaka,
Mulki dodon bango ne sai ka rage izza da ɓaɓɓaka,
Wata rana da ranka kana nan sai wani
Gwamna ake yi wa jiniya.
(Kabiru Kilasik: Waƙar Neja ga mafita).
Ciccika da izza da ɓaɓɓaka kalmomi ne masu
nuna ji-ji-da-kai, wanda aka fi samun sa ga mutane jahilai marasa ilmi na
addini da na boko. Mawaƙin ya siffanta wani ɗan takarar kujerar Gwamnan Neja da
wasu halittu na ruwa, wato buku da kwaɗɗo waɗanda ya ce su ne suke nuna ƙasaita
da izza. Wato, mawaƙin ya dabbantar da wannan ɗan takara domin ya jawo hankalin
mutane su lura da cewa, waɗannan halittu suna da halaye na girman kai ko saurin
fushi idan aka taɓa su. Saboda haka, shi wannan ɗan takara bai san cewa mulki
dodon bango ne ba, wata rana sai an yi kamar ba a yi ba. Ya yi masa habaici ta
hanyar sakaya sunansa ta hanyar amfani da kalmar ‘wani’ domin ka da
mutane su gane wanda ake yi wa habaicin, sai dai idan sun san halaye da ɗabi’un
wannan mutum. Ba komai ya jawo masa girman kai ba, illa rashin ilimi da rashin
sanin ya kamata. Mawaƙin ya nuna wa wannan ɗan takara cewa, ko da an zaɓe shi
ya yi mulki, to, ya sani da izzarsa da ji-ji da kansa wata rana sai labari;
domin zai sauka mulki ya koma tare da jama’ar da suka zaɓe shi ya zauna, ya
girbi abin da ya shuka na alheri ko akasin haka. Haka shi ma da yake sukar wani
shugaba maras ilimi da aka zaɓa, sai ya kasa iya tarbar baƙinsa da suka zo daga
ƙasashen Turai saboda ba ya jin harshen Turanci. Misali, inda Kamilu ɗan
almajirin mawaƙa yake cewa:
Wani ya hau mulki ba ilimi,
Ya ruɗe an mashi Turanci.
(Kamilu: Runhu an furen banza).
Rashin ilimi matsala ce mai girma ga
wanda yake neman matsayi na jagorancin jama’a. Domin duk mutumin da ba shi da ilimi ba zai san abin da mutane ke so ba, balle ya yi masu abin da ya dace. Ilimi shi ne tushen samar da kyakkyawar
hulɗa tsakanin shugaba da waɗanda yake shugabanta, ko waɗanda suka zo domin su
yi hulɗa da shi ko da ƙasarsa da yake shugabanta. A baitin da aka kawo a sama,
mawaƙin ya bayyana irin illar da rashin ilimi take da shi ga shugaba domin
yakan kasa aiwatar da kyakkyawar hulɗa sakaninsa da waɗanda yake da wata hulɗa
ta siyasa ko cinikayya ko makamanta haka da su. Yin magana da wani harshe na
daban da ya bambanta da harshen ƙasa, dole sai an koye shi, sannan a iya magana
da masu jin wannan harshe. Wannan dalili ne, ya sa mawaƙin ya yi wa wani
shugaba habaici saboda rashin iya ko jin harshen Turanci. Rashin jin harshen Turanci babbar illa
ce ga shugaba, musamman a ƙasar da harshen Turanci shi ne
harshen gudanar da hulɗa tsakanin ƙasar da wata ƙasa. Domin ba zai
iya jawo hankalin mutane su fahimci abin da gwamnatinsa take so ba. Saboda
haka, wannan illar zaɓen mutumin da ba shi da ilimi a kowane irin muƙamin
gwamnati, ta jawo hankalin mawaƙan siyasa su riƙa amfani da habaici wajen
ƙasƙanta shugabanni ko ‘yan siyasa a bainar ko idon jama’a. Mulkin siyasa yana
buƙatar mutum mai ilimi da ƙwarewa a harshen Turanci da sha’anin mulki domin ya
kasance ba ya jin shakkun zuwan baƙi idan sun zo masa daga ko’ina.
1.5.2 Son Kuɗi ko Mulki
Son kuɗi ko mulki wata buƙata ce ta zuciya,
wadda take zame wa mutane alaƙaƙai a zukatansu. Wannan buƙata takan jefa mutane
su riƙa bin hanyoyi na tsafe-tsafe da bokaye da malaman tsibbu domin neman
biyan buƙatunsu. Wannan ɗabi’a tana daga cikin abubuwan da ke saka mutane su
zama marasa tausayi da rashin jinƙai idan sun sami mulki ko sun mallaki dukiya.
Duk wanda ya nemi biyan wata buƙata ta ƙazamar hanya za a taras ba yakan kula
da bai wa talakawa haƙƙinsu su ba, wanda hakan kan jefa mutane cikin tunanin aikata
kowane irin abu na ta’addanci domin su sami sauƙin rayuwa. Saboda haka, sai
mawaƙan siyasa su riƙa amfani da habaici-sakayau da manufar gargaɗin ‘yan
siyasa su daina amfani da matasa wajen neman biyan buƙatunsu na siyasa domin
samun al’umma ta gari da shugabanci nagari. Domin shugabanci nagari shi ne
tushen samar da adalci da zaman lafiya da tsaro a ƙasa, musamman a yankin
Zamfara da ke arewa maso yammacin Nijeriya.
1.6 Habaici-Sakayau Ga Jam’iyya
Jam’iyya wata ƙungiya ce ta jama’a masu ra’ayi
iri ɗaya suka taru suka kafa ta domin cimma wata manufa ta siyasa. Kowace
jam’iyya tana alfahari da yawan magoya bayan da take da su. Idan jam’iyya ta
kasa samun magoya baya da za su taimaka mata ta kai ga ci, to takan samu
matsala da za ta kai ta ga rushewa. Duba da irin kwarjini da jam’iyyar APC take
da shi a duk faɗin Nijeriya ya sa Kamilu ya yi wa wata jam’iyya habaici domin
ya soki tafiyar ta da ta magoya bayanta.Ya yi amfani da harshen Turanci, ya
kira jam’iyya da ‘Fati’ (party), wanda hakan ya sa ya ba ta sunan
namiji. Misali, Murtala Mamsa yana cewa;
Wani fati ya mutu mun gano,
An je zaɓen duka gwamnoni.
(Murtala Mamsa:Waƙar A.P.C.).
A ɗan waƙa na farko mawaƙin ya yi amfani da
habaici-sakayau don ya muzanta wata jam’iyyar adawa da magoya bayanta bisa
ƙaryar da suka yi wa al’umma na taimaka masu ga samun abubuwan more rayuwa da
ayyukan cigaban ƙasa, amma suka kasa. Sannan ya nuna cewa, saboda ƙarya da suka
yi wa jama’a shi ya sa fatin ya mutu. Sannan ya aibata su da cewa, sun yi ƙarya
da suka ce, sun ga ɗiyan bishiyar ƙarya. Kowa ya san Hausawa suna cewa, ‘ƙarya
fure take yi ba ta ‘ya’ya’. Saboda haka, wannan habaici da mawaƙin ya yi,
yana yi wa ‘yan jam’iyya mai mulki shaguɓe ne ko hannunka-mai-sanda domin su
sauya salon tafiyarsu ga al’amarin siyasa ko da za su samu fatinsu ko
jam’iyyarsu ta dawo da darajarta.
Mawaƙin ya yi amfani da aron kalmar Turanci a
inda ya kira jam’iyya da sunan ‘Fati’ shi ne ya sa ya gina
habaici-sakayau da cewa, ‘wani Fati’ domin ya ƙasƙanta jam’iyyar da yake
yi wa habaicin. Kamar yadda aka sani ba a gane kwarjinin jam’iyya sai ran da
aka je wajen jefa ƙuri’a. Wannan jam’iyya da ke tinƙaho cewa, tana da mutane,
ashe duk kurari ne kawai. Ba a tabbatar da haka ba sai a lokacin jefa ƙuri’a
sai ga shi jam’iyyar ta sha kaye. Wato, ba a zaɓe ta ba. A duk lokacin da fati
bai yi nasarar lashe zaɓe ba, to babu tabbas da cewa, zai cigaba da bunƙasa. A
dalilin haka ne ya sa mawaƙin ya jefe shi da habaici yana cewa, ‘wani Fati
ya mutu mun gano, an je zaɓen duka gwamnoni’. Saboda haka, martabar Fati ko
jam’iyya ita ce, a zaɓe ta domin ta kafa gwamnati, idan ba haka ba, to za ta
mutu. Irin wannan yanayi ne da jam’iyyun siyasa suke shiga ya sa, Muhammadu
Awwalu Isah Bunguɗu yake yi wa jam’iyyar NPN habaici-sakyau domin ya kambama
tasa jamiyyar PRP, inda ya nuna cewa:
Ga wata
tunkiya da ba ta da tsoron tsara,
Ta kashe damisa
da zilla balle kura,
Mai tsoron
tsiya ƙazama mai kai ƙara,
Mun kore ta
dole ta yi gudu ta tsira,
Balle kai biri
da kai zure kai gwaiwa.
(Muhammadu
Awwalu Isah Bunguɗu: Waƙar ‘PRP mu gode Allah’).
1.7 Kammalawa
Mafi
yawan mawaƙan siyasar zamani suna alfahari da yin amfani da habaici cikin
waƙoƙinsu domin su jawo hankalin ‘yan siyasa da masu sauraro su fahimci
saƙonnin da suke isarwa gare su tare da samar masu nishaɗi. Muƙalar ta gano
cewa, mafi yawan ‘yan siyasa da ke bin hanyar bori da tsafe-tsafe da malaman
tsibbu wajen neman biyan buƙatarsu ta siyasa, marasa ilimin addini ne, da na
zamani. Wasu kuma suna da ilimin amma saboda son jin daɗin duniya ne yake jefa
su cikin wannan hali ido rufe. Mawaƙan siyasa suna ƙoƙari matuƙa wajen jawo
hankalin ‘yan siyasa don su fahimci cewa, Allah shi kaɗai Yake ba da mulki ga
wanda Ya so, a lokacin da Ya so. Saboda haka, suke kira ga ‘yan siyasa da su
guji yin tsafe-tsafe da shirka wajen neman mulkin duniya da ba ta da tabbas.
Idan kuwa aka samu haka a tsakanin masu neman mulki, suka dogara ga Allah, to
za a sami shugabanni nagari masu tsoron Allah da gaskiya da riƙon amana waɗanda
za su yi shugabanci cikin adalci. Kowa ya dogara ga Allah, ya nemi Allah ya yi
masa zaɓi, zai sami nasarar cimma gurinsa ta hanyar da ta dace. Sannan a sami
shugabanni nagari waɗanda za su kawo wa ƙasa zaman lafiya da tsaro da cigaban
tattalin arzikin ƙasa.
Manazarta
Abdullahi, S. U. (1987). Gaskiya
dokin Ƙarfe. Kano, Triumph Publishing Company.
Bagari,
D. (1986). Bayani Hausa:Jagora ga mai
Koyon Ilimin Bayanin Harshe. Rabat-Moroc, Imeremerie El- Maarif Al-Jadida.
Bergery,
G.P. (1993). Hausa-Enlish and
English-Hausa Vocabulary. London: Oxford University Press.
Dangambo,
A. (1984). Rabe-raben Adabin Hausa da
Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph Publishing Company.
Dangulbi,
A. R. (1996). Habaici da Zambo a cikin Waƙoƙin Baka na Hausa. Takardar da aka
gabatar a taron ƙara wa juna sani a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari, Sakkwato.
Encyclopedia
Britannica Updated Feb. 11,2023. An article History.
Koko,
H. S. (1989). Jagoran Naarin Tatsuniyoyi.
Sakkwato: College of Education.
Mawaƙa
Dauda Adamu Kahutu Rarara: Waƙar Muhammadu Buhari ta APC.
Kabiru Yahaya Kilasik (2015). Waƙar Neja ga
Mafita ta Muhammadu Bawa Rijau ɗan takarar Gwamnan Neja.
Muhammmadu Awwalu Isah Bunguɗu (1983). Waƙar PRP.
Garba Gashuwa, ( 1999). Waƙar APP, Mnafuccin Karen Ruwa
Malumfashi I. da Nahuche I. (2014). Ƙamusun
Karin Magana,
Martan Websters {10th Edition Dictionary}
Mudassir Kasimu Kano: Waƙar APC
Murtala Mamsa Jos: Waƙar Jam’iyyar APC.
Ibrahim Yala Hayin Banki: Waƙar Muhammadu
Buhari
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.