𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum malam barka da dare. Malam ni mai laifice Kuma laifin babba. dan Allah malam wlh na yi nadama na yi dana sani kullum cikin neman yafiyar Allah nake yi na aikata laifin zina da aurena yayin da na tuba na koma neman gafarar Allah kawai na gane ina dauke da ciki Kuma na san ba nasa ba ne malam mene ne makomar wannan cikin malam ina cikin damuwa na rasa yadda zan yi da cikin nan ina neman fatawarka malam Dan Allah yazama sirrin tsakaninmu. Ga shi yana son cikin mijina saboda ba mu taɓa haihuwa ba yan uwansa Sun sani a gaba suna kirana juya ni yanzu ban san yadda zan yi ba dan Allah a taimaka min
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh
Babu makawa abin da kin
aikata na zina kina matar aure yana cikin manyan laifuka, ko da zina zunubi ce
maigirma ita kaɗai to girman zunubin
nakaruwa idan aka ce mai aure ta yi zina, shiyasa ma hukuncin mazinacin da bai
taɓa
aure ba shi ne bulala 100, wanda kuma yake da aure ko yataɓa
aure shi ne ajefeshi harsai ya mutu.
Hakika kin tafka babban
kuskure. Domin zina tana cikin Kaba'irori wato zunubai mafiya girman laifi a
wajen Allah. Awani hadisi Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam cewa ya yi "Bayan
yin shirka da Allah, babu wani zunubi mafi girman laifi kamar maniyyin da
namiji ya sanyashi a cikin mahaifar matar da ba ta halatta gareshi ba".
Duk macen da ta yi zina
alhalin tana da aure haƙiƙa ta ci amanar mijinta, kuma ta tonawa
'yaƴanta da danginta asiri, saboda duk wani
mutum kirki zai ƙyamaci
auren 'yaƴanta don gudun gori
daga bakunan mutane. Kuma ga babban cin mutuncin da ta yi wa mijinta wanda
tabbas sai Allah ya bi ma sa haƙƙinsa
a ranar alƙiyamah matuƙar be yafe mata ba. Saboda haka ki nemi
yafiya a wajen mijinki cikin salo ba tare da ya gane abin da kika aikata ba.
An tambayi SHAIK BIN BAAZ
dangane da matar datake da aure sai ta samu ciki ta hanyar zina, shin ya
halatta ta zubda cikin ɗan? ko za ta kyaleshi, idan
ta kyale cikin shin za ta baiwa mijinta labari ko ba zata bashi ba? sannan mene
ne yake wajibi akan mijin a wannan halin?
Sai ya amsa dacewa: Bai
halatta agareta ta zubda wannan cikin ba, abin da yake wajibi akanta shi ne
tuba zuwa ga Allah maɗaukakin sarki, da kuma kin
bayyana al'amarin, ɗan da ta haifa kuma za a jinginawa
mijinta ma'ana ɗansane, saboda faɗin
Annabi sallahu Alaihi wasallam (Ɗa na
mai aure ne mazinaci kuma uƙuba
ce kawai tasa) Ma'ana wanda yai zina baida hakkin ajingina ɗan
gareshi, shi kawai uƙubar
zinarce akansa. Fatawa bin baaz (21/205).
Da wannan majalisar fatawa
ta kasar saudiyyah tai fatawa, Allah yagyara halayen mu gaba ɗaya.
Tare da girman laifin da
kika aikata da muninsa a al'ada da kuma hankali, babu wanda zai shiga tsakanin
Allah da bawansa, Allah yana farin ciki da tuban bawa kuma yana karɓar
tuban, Allah maɗaukakin sarki Ya ce:
قُلْ يَا عِبَادِيَ الَّذِينَ أَسْرَفُوا عَلَىٰ أَنفُسِهِمْ لَا تَقْنَطُوا مِن رَّحْمَةِ اللَّهِ ۚ إِنَّ اللَّهَ يَغْفِرُ الذُّنُوبَ جَمِيعًا ۚ إِنَّهُ هُوَ الْغَفُورُ الرَّحِيمُ
Ka ce: (Allah Ya ce): ''Ya bayĩNa
waɗanda
suka yi ɓarna
a kan rayukansu! Kada ku yanke ƙauna
daga rahamar Allah. Lalle Allah na gafarta
zunubai gaba ɗaya.
Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai gafara, Mai jin ƙai.'
(Suratul Zumar Aya ta 53).
Ibnu kasir rahimahullah Ya
ce: Wannan aya tana kirane ga dukkan masu saɓo
harda kafirai su tuba su koma zuwa ga Allah, tana kuma ba da labarin Allah yana
gafarta zunubai baki ɗaya ga duk wanda ya tuba
yadawo daka aikata laifukan, komai irin yawansu da girmansu ko da sunkai yawan
kumfar kogi, matukar an yi tuba nagaskiya Allah yana gafarta su.
Amma nasabar ɗan
za a jingina shi ga mijinki na aure ne, matukar yasadu dake, saboda faɗin
Annabi sallallahu Alaihi wasallam daya ce: (Ɗa na
me aurene) ma'ana ɗan na mijin dakike aure da
shi ne ko da ba a saduwa da shi cikin ɗan
ya shiga ba, in dai kin kwanta da mijin bayan zinar ɗan na
sane.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.