Article Citation: Baffa, A.S. & Ibrahim, O.M. (2025). Sabon Salon Buɗe Waƙoƙi a Ƙarni Na Ishirin Da Ɗaya. Zauren Waƙa, 4(2), 50-59. www.doi.org/10.36349/zwjohps.2025.v04i02.006.
SABON SALON BUƊE WAƘOƘI A ƘARNI NA ISHIRIN DA ƊAYA
Na
Ahmed Sulaiman Baffa
Department of African
Languages & Linguistics
Yobe State University
Damaturu, Nigeria
Email: ahamadsulaimanbaffa
4455@. Com
GSM: 07068946160
Da
Ogah Muhammed Ibrahim
Department of General
Studies & Pre-ND
Isa Mustapha Agwai 1 Polytechnic,
Lafia
Tsakure
Al’umma
ta lura da cewa waƙa aba ce mai saurin
kama zuaciya da isar da saƙo cikin ƙanƙanin lokaci, wannan
ya sa masana da manazarta suka ba da lokutansu musamman don nazartar waƙoƙin. Tun a ƙarni na shabakwai aka
fara samun rubutattun waƙoƙi a ƙasar Hausa masu mabuɗi da marufi. Haka abin ya ci gaba har ya gangaro ƙarni na 18, da 19 da
na 20. Sai dai ana samun bambance-bambance dangane da matakai da ake bi wajen
buɗe waƙoƙin a kowane ƙarni. Wannan ya sa
aka dubi matakan buɗe waƙoƙi a ƙarni na 21 inda aka
samu matakai shida da mawaƙan ƙarni na 21 ke amfani
da su wajen buɗe waƙoƙinsu, waɗanda suka samu sakamakon samuwar sigogin waƙar baka da na
rubutacciyar waƙa a waƙoƙin waɗanda suka haifar da samuwar waɗannan sababbin matakai na buɗe waƙa.
Matakan sun haɗa da; take wato kiɗa da amshi da sharar fage da ambaton Allah da yin addu’o’i
da ambaton Annabi (SAW) da kuma rashin amfani da mabuɗi. Sanin waɗannan matakai zai
taimaka wa manazarta da ɗalibai wajen nazari,
kuma zai bayyana tasirin baƙin al’adu a kan na Hausawa. Sannan an
kawo bayanin kammalawa.
1.0
Gabatawa
An lura da cewa waƙa aba ce mai saurin
kama zuciya wajen sauya wa al’umma tunani da kawo saƙonni masu muhimmanci
ga jama’a. wannan ya sa masana da manazarta suka duƙufa wajen nazarinta.
Tun ƙarni na sha bakwai aka fara samun ɓirɓishin rubutattun waƙoƙi irin su; ‘Waƙar Daliyya’ da,
‘Nuniyya’ ta Wali Ɗanmarina. Sha’anin waƙa ya ci gaba da wanzuwa har ƙarni na sha takwas
lokacin da aka samu malamai irin su; Malam Muhammadu Na Birnin Gwari wanda ya
yi waƙoƙi da dama, waɗanda suka haɗa da; “Ma’akusa” da, “Jawahiru” da, “Billahi Arumu”. Haka
Malam Shi’itu ɗan Abdurra’uf ya yi
waƙoƙi da dama kamar; “Fassarar Arshada” da “Waƙar Tuba”. A ƙarni na sha tara kuma
aka samu mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo a (1754-1817) da almajiransa sun yi waƙoƙi da dama masu
manufofi na addini kamar su; “Waƙar Cin Birnin Alƙalawa” da “Waƙar Tsarin Mulkin Musulunci” ta Abdullahi Fodiyo da sauransu
(Yahaya, 2002:37-59). A ƙarni na ashirin al’amarin waƙa ya zama muhimmin
al’amari, jigoginta suka faɗaɗa daga manufofi na addini suka haɗa da al’amuran rayuwar duniya, an yi waƙoƙi da dama kamar “Waƙar Zambon Ƙazama” ta Aliyu
Namangi da “Waƙar ‘Yar Gagara” ta Aƙilu Aliyu da sauransu. Kamar yadda masu iya magana ke cewa:
“Idan kiɗa ya sauya dole rawa
ma ta sauya”. Wannan sauyi shi ne za a iya cewa abin da ya faru da tsarin mabuɗan waƙoƙin Hausa a ƙarni na ishirin da ɗaya. Sauyin lokaci da cuɗanya da baƙin al’adu ya yi tasiri kan tsari da sigogin waƙoƙin Hausa a ƙarni na ashirin da ɗaya musamman mabuɗan waƙoƙi. An samu sauye-sauye dangane da mabuɗan waƙoƙi a ƙarni na 21 ta fuskoki daban-daban. waɗanda ba a samu irinsu a waƙoƙin ƙarni na 17-20 ba.
Wannan ya sa aka dubi
sabbin tsarin matakai na mabuɗan waƙoƙin Hausa na ƙarni na ishirin da ɗaya don fito da sababbin matakan buɗe waƙoƙi da mawaƙan ke amfani da su yayin buɗe waƙoƙinsu. Wannan takarda ta yi bayanin matakai shida da mawaƙan ke amfani da su
yayin buɗe waƙoƙinsu. Matakan sun haɗa da; take wanda ya ƙunshi kiɗa da amshi da sharar
fage wanda ya ƙunshi sunan mawaƙi da sunan wanda aka yi wa waƙa da wanda ya ɗauki nauyin waƙa da lambar waya da gabatar da sallama. Sannan ambaton Allah
wanda ya ƙunshi gaskata shi da yabon sa da girmama shi da yi masa
kirari da sauransu. An dubi addu’a da ta haɗa da nema ƙarin basirar tsara waƙa da ƙarin ilmi da neman tsari da sauransu. An kawo ambaton Annabi
wanda ya haɗa da yi masa salati
da yabo da kamun ƙafa da shi da ambaton iyalansa da sahabbansa da sauran
Annabawa.
1.1 Waƙoƙi A Waƙoƙin Ƙarni Na 21
Waƙoƙin da suka shahara a
yau waƙoƙi ne da ba zai yiwu a kira su kai tsaye da rubutattu ko waƙoƙin baka ba. Duba da
yadda waƙoƙin suka haɗa sigogi daban-daban
na waƙar da baka da kuma na rubutacciyar waƙa. Hakan ya sa masana
da dama suka yi ƙoƙarin samar musu suna wanda zai dace da su. Daga ciki akwai
Dumfawa (2014) ya kisu da Makaɗan Zamani, Atowa da
Dono (2014) sun kira su da Hausa Poems in The 21ts Century, shi kuma Usman
(2018) ya kira su da Ruwa-biyu. Wasu masan kuma su kira su da Jemagu, wasu kuma
da waƙoƙin fiyano
Idan aka iya la’akari
da waɗannan sunaye da
masana suka bayar ga cewa akwai abin dubawa kamar haka:
a. Jingina
su ga zamani, idan zamanin ya wuce da me za kira su?
b. Kiransu
da ruwa biyu, shima ba zai yiwu ba saboda ba sigogin waƙar baka dana
rubutacciyar waƙa ba ne kaɗai a cikinsu, suma
sun zo sabin abubuwa nasu daban. Haka bayanin yake idan aka kira su jemagu.
Don haka na zaɓi na kira su da waƙoƙin ƙarna na 21, saboda sun haɗa sigogin rubutacciyar waƙa kamar mabuɗi da marifi da amsa-amo da tsarin layuka da baiti da kari,
da kuma sigogin waƙar baka kamar sanƙiranci da amshi da kiɗa da da gaza da sauransu, waɗanda su uka haifar da samawar waɗannan sabin salailai na mabuɗan waƙa. Bayan haka kuma waƙoƙin sunzo da sabin abubuwa da babu su a waƙoƙin da suka gabace su,
kamar jagorancin mace da namiji da sauransu. Waɗannan dalilai ya sa aka kira su waƙoƙi ƙarni na 21.
2.0 Sharhin Tubalan Take
A lokutan da suka shuɗe mawaƙa na amfani da wasu hanyoyi wajen buɗe waƙoƙinsu, waɗannan hanyoyi kuwa
wasu lafuzza ne da aka san marubuta waƙoƙi na amfani da su yayin bude waƙoƙin su. Mabuɗin waƙa yakan ƙunshi duk wasu lafuzza da mawaƙa ke amfani da su a
yayin buɗe waƙa.
2.1 Mabuɗin Waƙa
Sa’id (1978), ya ce
waƙoƙin Hausa da suka samu kafin ƙarni na ishirin duka
sun bi tsarin farawa da rufewa da ambato da salati ga Annabi ( Tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) da addu’a.
Omar (2013), ta
bayyana cewa mabuɗi salo ne da ke nuni
da cewa an fara waƙa. Ta kuma ƙara da cewa abu ne da ya ɗau salo na musamman tun asalin tarihin rubutattun waƙoƙin Hausa har zuwa
lokacin da take rubuta takardarta.
2.2 Mabuɗin Waƙa Kafin Ƙarni Na 21
Omar (2013), ta
bayyana cewa marubuta waƙoƙi sun fara amfani da mabuɗi da marufi a waƙoƙinsu tun daga ƙarni na 17 har zuwa ƙarni na 20. Hanyoyin da marubuta waƙoƙin ƙarni na 19 da na 20
ke bi don yin amfani da mabuɗi a yayin buɗe waƙoƙinsu sun rabu gida huɗu kamar haka:
a. Ambaton
Allah ta hanyar gaskata shi da yabon sa da girmama shi da yi masa kirari da
sauransu.
b. Ambaton
Annabi Muhammadu (Mai tsira da amincin Allah) ta hanyar yi masa salati da
yabonsa da kamun ƙafa gare shi da ambaton alayensa da sahabbansa da sauran
annabawan Allah.
c. Yin
addu’a ta hanyar roƙon Allah wani abun buƙata, masamman basira ta tsara waƙa, ko neman buɗi na ilimi ko neman tsira da sauransu,
d. Rashin
amfani da mabuɗi da marufi wato,
rashin amfani da hanyoyin da aka zayyana a sama.
Mabuɗin Waƙa a Ƙarni na Ishirin da Ɗaya
Ta la’akari da yadda
matakan buɗe waƙoƙi suke a lokutan da
suka gabata za a iya cewa, wasu daga cikin mawaƙan ƙarni na 21, sun ɗau sahun magabata wajen amfani da mabuɗi a yayin aiwatar da waƙoƙinsu, duk da cewa ba su taƙaita a kan hanyoyin
da magabatan suka yi amfani da su ba. Sun zo da sababbin tsari da wasu matakai
da suke amfani da su wajen buɗe waƙoƙinsu.
3.1 Matakan Buɗe Waƙoƙi a Ƙarni na Ishirin da Ɗaya (21)
A nan an bayyana
matakan da mawaƙan ƙarni na 21 ke amfani da su wajen buɗe waƙoƙinsu, saboda sun bambanta da na magabatansu. Mawaƙan ƙarni na 21 na amfani
da matakai har guda shida a yayin buɗe waƙoƙinsu kamar haka:
3.1.1 Take: kiɗa da amshi
Wannan shi ne matakin
farko kuma abin da ke fara shiga kunnen mai sauraro, kuma wannan ya zama tamkar
wajibi a waƙoƙin Hausa a yau. Wannan ya ƙunshi abu biyu kamar
haka:
a. Kiɗa
b. Amshi
Da yawa daga cikin waƙoƙin ƙarni na 21, abun da
ake fara ji a cikinsu shi ne kiɗa da amshi ko kiɗa sannan amshi ko amshin ya riga kiɗan. Misali: Waƙar Amina Buni Yadi ta Dokta Yarima Ngama ta fara da kiɗa da amshi kamar haka:
An samu kiɗa:------------------------
Sannan amshi.
Amshi: Minista Dokta Yarima Lawan gwanin talakawa mai
nasara,
Magauta dole su ƙyale ka ka kawo gyara PDP.
(Amina Buni Yadi: Waƙar Dokta Yarima Ngama)
Idan aka saurari waƙar Amina Buni Yadi da
ta yi wa Dokta Yarima Ngama abin da aka fara ji kiɗa ne, sannan amshi kamar yadda aka gani cikin misalin da ya
gabata.
Haka waƙar Kamilu Hussaini
Nguru wadda ya yi wa Atiku Bagudu, ita ma abun da aka fara ji shi ne kiɗa da amshi kamar kaha:
Kiɗa: ------------------------------- Sannan Amshi.
Amshi: Waƙe na jihar Kebbi na
koma, gwarzo Bagudu ne gwamna,
Abin da kake mana na
gaskiya, Bello ne ya faɗa mana halinka.
(Kamilu Husaini
Nguru: Waƙar Atiku Bagudu)
Idan aka lura da
wannan misali, za a ga cewa Kamilu Husaini Nguru ya fara amfani da kiɗa sannan amshi a waƙarsa da ya yi wa Atiku Bagudu, Hakan ya nuna cewa kiɗa da amshi su ne mataki na farko da mawaƙan ƙarni na ishirin da ɗaya ke amfani da shi wajen buɗe waƙoƙinsu.
3.1.2 Sharar fage:
Wannan shi ne gabatar
da wasu kalmomi kafin fara waƙa waɗan da suka ƙunshi abubuwa kamar
haka:
• Ambaton
sunan mawaƙi
• Ambaton
sunan wanda za a yi wa waƙa
• Ambaton
sunan waƙa.
• Ambaton
sunan wanda ya ɗauki nauyin waƙa
• Ambaton
lambar wayaA
• Yin
sallama ga masu sauraro
Wasu waƙoƙin wannan ƙarni na 21 akan yi
sharar fage kafin ko bayan kiɗa da amshi wanda
yakan ƙunshi abubuwan da aka lissafo gaba ɗaya a ƙarƙashin sharar fage a wasu lokuta, a wasu lokutan kuma sharar
fagen takan shafi wasu ne daga cikin abubuwan da aka zayyan a ƙarƙashin sharar fagen.
Misali: Waƙar Kabiru Kilasik da ya yi wa Cigarin Mafara.
07036650441,
08123225152
Assalamu alaikum mai
sauraro,
Kabiru Classic ne ke ɗauke da sabuwar waƙa,
Cigarin Mafara
Barista Mainasara Mika’ilu Tafida,
Wanda aka fi sani da
suna Hasken Cigarin Mafara.
A yi sauraro lafiya.
(Kabiru Kilasik: Waƙar Cigarin Mafara)
A wannan waƙar ta Kabiru Kilasik
da ya yi wa Cigarin Mafara, an samu sharar fage da ya ƙunshi lambar waya da
sallama da sunan mawaƙi da kuma sunan wanda aka yi wa waƙa.
Haka waƙar Yahaya Sauwa da ya
yi wa Ciroman Kebbi mai taken “Alheri” ta zo da sharar fage kamar haka:
Assalamu alaikum
al’ummar jihar Kebbi baki ɗaya,
Ga Yahaya Bala
Sama’ila Sanwa ɗauke da sabuwar waƙa,
Mai suna Wutar kara
izar masu ɗiya,
Ya yi wannan waƙa ne ga Alhaji
Muhammadu Mera,
Mai neman tsayawa
takarar kujerar jihar Kebbi,
Mai neman ƙarin bayani sai ya ƙira lambar waya kamar
haka,
08068070503. Ayi
saurare lafiya.
(Yahaya Sauwa: Waƙar Alheri ta Ciroman
Kebbi)
Wannan misali ya
bayyana yadda sharar fagen ya ƙunshi sallama da ambaton sunan mawaƙi da sunan wanda aka
yi wa waƙar da lambar waya.
Assalamu
alaikum.
Za ku saurari waƙa daga bakin ni Amina
Buni Yadi,
Wadda aka yi wa
maigidanmu Yarima Ngama,
Ƙarƙashin jagorancin Alƙali B.A. Don neman
Ƙarin bayani za a iya nemanmu ta lambar waya kamar haka,
08062931262 A yi
saurare lafiya.
Jagora: Na gode
tabara sarkin kyauta Tabara mai baiwa da yawa,
Almaliku mai yanayin
sanyi Tabara kai ke ba mu ruwa,
Ka ninka salati ba
adadi ga Annabi mai kyawon tsayuwa,
Na sanya sahabbai
musu son zaman lumana ba sa son rigima,
(Amina Buni Yadi: Waƙar Dokta Yarima
Ngama)
Ta la’akari da wannan
misalin za ga cewa an samu sharar fage da ya ƙunshi sallama ga masu
saurare da sunan mawaƙiya da sunan wanda aka yi wa waƙa da wanda aka
gudanar da waƙar a ƙarƙashin jagorancinsa, sannan aka kawo lambar waya a ƙarshe.
3.1.3Ambaton Allah:
Wannan hanya ta haɗa abubuwa da dama kamar haka:
a. Gaskata
shi
b. Yabon
sa
c. Girmama
shi
d. Yi
masa kirari
Mawaƙan ƙarni na 21, na amfani
da salon buɗewa na ambaton Allah
ta hanyar yabon sa ko girmama shi ko yi masa kirari ko gaskata shi.
Misali: Kamilu
Husaini Nguru a waƙarsa ta Atiku Bagudu ya yi amfani da ambaton Allah wajen buɗe waƙarsa inda yake cewa:
Jagora; Sarki buwayi
gwani Allah, ka san shi ne masanin mulki,
Shi ne ya yi yo jaki
na gida cikin iko nasa yai doki,
Shi ne ya yi yo
mutumin banza, sannan ya yiyo mutumin kirki,
Haka nan ya yiyo ɓauna a dawa sannan Allah haka yai zaki,
Mu yi nema na halal
jalla shi ya hana mu je sata.
(Kamilu Husaini
Nguru: Waƙar Atiku Bagudu)
Wannan misali bayyana
yadda Kamilu Husaini Nguru ya yi amfani da ambaton Allah a yayin buɗe waƙarsa. Kuma ambaton ya zo ta hanyar kirari da girmama Allah
(SWT) inda mawaƙin ya nuna buwaya da gwanintar Ubangiji wajen halitta.
Haka Amina Buni Yadi
ita ma ta zo da irin wannan salo a mabuɗin waƙarta da ta yi wa Dokta Yarima Ngama kamar haka:
Jagora:
Na gode Tabara sarkin kyauta Tabara mai baiwa da yawa,
Almaliku
mai yanayin sanyi tabara kai ke ba mu ruwa,
Ka
ninka salati ba adadi ga Annabi mai kyawon tsayuwa,
Na
sanya sahabbai musu son zaman lumana bas a son rigima.
(Amina Buni Yadi: Waƙar Dokta Yarima
Ngama)
Wannan misali ya nuna
yadda Amina Buni Yadi ta yi amfani da ambaton Allah a mabuɗin waƙarta da ta yi wa Dokta Yarima Ngama. Ambaton Allah (SWT) ya
zo ta hanyar godiya da yabo a gare shi bisa kyautar da ke yi wa bayinsa ta
hanyar kawo ruwa da sanyi da sauran ni’imominsa
Shi ma Ali Mega a waƙarsa ta “To A Yi Dai
Mu Gani”, ya yi amfani da irin wannan salo wajen buɗe waƙarsa misali:
Jagora: To da fari Tabara gwani shi ne wanda
ya ƙagi wuta da ruwa,
Mahaliccin saman
bakwai da ƙassai ga mu cikin matsuwa,
Taimaka mana rabbi guguwar canji ta fara hawa
Mulkin kama-karya
‘yan Yobe muna faman taɓuwa,
Allah sarkin haƙuri canja mana wanda
ba za su ci ba.
Jagora: To Rabbi
sarki gatanmu ƙara mana son manzoka fari,
Ɗan Amina rasulullahi kowa ya riƙa ya yo katari,
Jalla har da
sahabbansa da sahabbai gida haƙuri,
Allah kai za ka yi,
kai kake mana ba wani ɗan zina ba.
(Ali Mega: Waƙar To A Yi Dai Mu
Gani)
Wannan misali ya nuna
yadda Ali Mega ya yi amfani da ambaton Allah (SWT) a yayin buɗe waƙarsa mai taken “To A Yi Dai Mu Gani”.Ambaton ya zo ta fuska
kirari ta hanyar nuna gwanintarsa kan halittar wuta da ruwa da sammai bakwai da
ƙassai bakwai.
3.1.4 Yin addu’a
Wannan hanya da mawaƙi ke bi roƙon Allah wata buƙata, kamar su:
a. Neman
basira ta tsara waƙa
b. Neman
buɗi na ilimi
c. Neman
tsira da sauransu.
Mawaƙan ƙarni na 21, ba a bar
su a baya ba wajen yin addu’a a cikin mabuɗin waƙoƙinsu. Ga wani Misali:
Ali Mega a waƙarsa ta “To A Yi Dai
Mu Gani” ya yi amfani da addu’a inda yake cewa:
Jagora: To Rabbi sarki gatanmu ƙara mana son manzoka
fari,
Ɗan Amina rasulullahi kowa ya riƙa ya yo katari,
Jalla
har da sahabbansa da sahabbai gida haƙuri,
Allah
kai za ka yi, kai kake mana ba wani ɗan zina ba.
(Ali Mega: Waƙar To A Yi Dai Mu
Gani)
Ta la’akari da yadda
mawaƙin ya tsara mabuɗin wannan waƙar, za a ga cewa, an yi amfani da addu’a inda mawaƙin ke neman Allah ya ƙara mana son manzo da
sabbansa.
Sai kuma waƙar Ɗahiru Na Maikwari,
wanda ya yi wa Abu Magaji, ita ta zo da irin wannan salo kamar haka:
Jagora: Abu Magaji Allahu ka ƙara ɗaukaka,
Abu
Magaji ka yi mana Allahu yai maka,
Abu
Magaji dan manzo ɗaha mai Maka
Kariya
ya yo maka kowa ba shi yo maka,
Shatima
Bature giwa ba a far maka,
Kura
ki ƙara haushi zaki ya far miki,
(Ɗahiru Na Maikwari: Waƙar Abu Magaji)
A wanna misali za a
ga yadda Ɗahiru na Maikwari ya yi amfani da addu’a wajen buɗe waƙarsa, inda yake fatar Allah ya ƙara wa maigidansa Abu
Magaji ɗaukaka.
3.1.5 Ambaton Annabi Muhammadu ( Mai tsira da amincin
Allah):
Wannan hanya ce da
ake bi wajen yi masa abubuwa kamar haka:
a. Salati
b. Yabonsa
c. Kamun
ƙafa gare shi
d. Ambaton
Alayensa
e. Ambaton
Sahabbansa
f.
Sauran Annabawan Allah.
A ƙarni na 21, wasu mawaƙa kan yi amfani da
wannan salo wajen buɗe waƙoƙinsu wato ambaton
Annabi. Mawaƙan sukan yi hakan ne ta hanyar salati ko yabo ko kamun ƙafa ko ambaton alaye
ko sahabbansa. Misali:
Muhammadu Barnin
Magaji a waƙarsa ta Salisu Tafida ya yi amfani da irin wannan salon wajen
buɗe waƙar kamar haka:
Jagora: Rayuwata ta
nutsu kullum ni so nake in ga Muhammadu,*2
Cikin dare ban bacci
kullum ka gan ni na koma can Kudu,
Ban da aikin yi sai
sallah na riƙi Allah in ga Muhammadu,
Na yi Gabas na yi
Yamma na dawo Arewa kai har na koma kudu,
Tsaya tsakiya cak ni
dai farin cikina in ga Muhammadu,
Allah idan ka haɗa ni da manzonka na sani na ƙare lafiya.
(Mahammadu Birnin
Magaji: Waƙar Salisu Tafida)
Wannan misali ya nuna
yadda Muhammadu Birnin Magaji ya yi amfani da begen Annabi wajen buɗe waƙarsa ta Salisu Tafida. Ta hanyar fatarsa ita ce kullum ya ga
Annabi Muhammadu.
Haka shi ma Yahaya
Sauwa a waƙarsa ta “Alkairi ta Ciroman Kebbi”, ya yi amfani da irin
wannan salo ga abin da ya ce:
Jagora:
Annabinmu ɗan gatan Allah wanda
ba ya zalunci,
Mai
isar cika wajen Allah mai hali da karamci,
Rayuwa
da ba ta begenka ba ta hurce ƙasƙanci,
Kai
muka biya ɗan Abdallah kai ɗai ka ceto mu.
(Yahaya Sauwa:
Alkairi ta Ciroman Kebbi)
A nan an ambaci
Annabi ta hanyar yi masa yabo, inda mawaƙin ya bayyana halinsa na karamci, ya kuma nuna rashin begen
Annabi zai jawo ƙasƙanci. Sannan ƙarshe ya yi kamun ƙafa gare shi, don neman ceto.
Shi ma Kabiru Kilasik
ya zo da irin wannan misali na salon buɗe waƙa a waƙarsa ta Cigarin Mafara kamar haka:
Jagora: Manzo ƙaunarka nake, ni kan
zaɗin ka nake,
Manzo Allah mai hana ƙarya, Ilahi ƙaunarka nake,
Manzona ma’asumi
bayin Allah, sarkinmu kake,
Kowa
ya yarda da manzona, a ƙiyama za ya sam tsira.
(Kabiru Kilasik: Waƙar Cigarin Mafara)
A wannan misali mawaƙin ya ambaci Annabi
(SAW) ta hanyar nuna masa ƙauna, sannan kuma ya yabe shi.
3.1.6 Rashin Mabuɗi
Wannan wata hanya ce
da mawaƙi ke bi yayin fara waƙarsa inda ba zai yi amfani da kowace hanya ba daga cikin
hanyoyin da aka ambata a sama sai dai hanya ta farko kaɗai wato, ba amfani da kiɗa ko amshi. Galibi mawaƙa a wannan ƙarnin sun fi amfani da wannan hanya, musamman a waƙoƙin soyayya. A taƙaice ana iya cewa
babu wata takamammiyar hanya ko wani salo na musamman da suke amfani da shi a yayin
buɗe waƙoƙinsu. Sai dai galibi
mawaƙi yakan fara ne da wasu abubuwa kamar haka:
Bayar da umarni ga
masu yi masa kiɗa ko amshi, inda zai
nemi su ba shi kiɗa, ko wani abu mai
kama da haka. Misali;
Umar M. Sharif shi ma
ya yi amfani da maimaita amshin waƙarsa wajen buɗe waƙar kamar haka:
Amshi: Hafiz kai nake
so a zuciya, tsaya ka saurare ni,
Hafiz ka daɗe a zuciya, kar ka kore ni.
(Umar M. Sharif: Waƙar Hafiz Kai Nake So)
A nan an ga misalign
yadda Umar M. Sharif ya fara waƙa ba tare da bin ɗaya daga cikin matakan da aka zayyana a sama ba. Sai dai ya
yi amfani da wasu kalmomi na soyayya ne wajen fara waƙar.
Nura M. Inuwa a waƙarsa ta Hussuna da
Huzzuna ya buɗe waƙar da amshi wanda ke ɗauke da wasu kalaman soyayya, kamar haka:
Amshi: Huzzina na yi tuntuɓe, nai gam-da-katar da dinshina,
Idanu dole yai
rufewa, ba nisa garin masoyi.
(Nura M. Inuwa: Waƙar Hussina da
Huzzina)
Wannan misali ya nuna
yadda Nura M. Inuwa ya fara waƙarsa ta Hussina da Huzzina ba tare da bin matakan buɗe waƙa da aka kawo a sama ba. Sai dai ya yi amfani amshi mai
bayyana sunan masoyiyarsa.
Waƙar Hauwa ‘Yar Filani
ta Yankari ba ta da mabuɗi, ta fara waƙar ta hanyar nuna
mamakinta ga dajin Yankari kamar haka:
Jagora: Yankari ƙudura ta Allah daji na al’ajab,
Sansani
na ahalil dabbobi,
Giwa
zaki Burungu ga Ɓauna saniyar sake
Nau’i
nau’i cikin cikn dabbobi.
(Hauwa ‘Yar Fulani:
Waƙar Yankari)
Wannan misali ya
bayyana yadda Hauwa ‘Yar Fulani ta fara waƙarta ta “Yankari” ba tare da bin matakan buɗe waƙa da aka ambata a sama ba. Sai dai ta fara waƙar ne kai tsaye da
mamakin ikon Allah (SWT) game da sha’anin dajin Yankari.
Haka Dauda Kahutu
Rarara ya yi a waƙarsa ta “Mai Malafa Ya Karya Ta Ƙure”, ita ma ba mabuɗi ya fara waƙar yana cewa:
Mai malafa ƙarya ta ƙure,
Ku faɗi ko kar ku faɗi, sama,
Mai malafa ƙarya ta ƙure
PDP ta mutu an gama.
(Dauda Kahutu Rarara:
Waƙar Mai Malafa Ƙarya ta Ƙure)
Idan aka dubi wannan
misali za a ga cewa Dauda Kahutu Rarara bai yi amfani da matakan buɗe waƙa da aka zayyana a sama ba. Sai dai ya buɗe waƙar ne da amshi mai ɗauke da taken waƙar, inda yake nuna gazawar abokin takarar maigidansa.
4.0 Kammalawa
Wannan takarda ta
dubi muhimmancin waƙa ga al’umma da taƙaitaccen tarihin samuwarta tun daga ƙarni na 17 har zuwa
na 20 da ma’anar waƙa da hanyoyi da magabata suka bi wajen amfani da mabuɗi a waƙoƙinsu. Sannan aka shiga zuciyar takardar wato, tsarin mabuɗin waƙoƙin ƙarni na ishirin da ɗaya, inda aka kawo matakai shida da mawaƙan ƙarni na 21 ke amfani
da su yayin buɗe waƙoƙinsu. Matakan sun haɗa da; take wanda ya ƙunshi kiɗa da amshi da sharar
fage wanda ya ƙunshi sunan mawaƙi da sunan wanda aka yi wa waƙa da wanda ya ɗauki nauyin waƙa da lambar wayar mai waƙa da gabatar da
sallama ga masu sauraro. Sai kuma ambaton Allah wanda ya ƙunshi gaskata
maganarsa da yabonsa da girmama shi da ya masa kirari. An dubi addu’a da mawaƙan ke yi kamar nema ƙarin basira ta tsara
waƙa da ƙarin ilmi da neman tsari da sauransu. An kawo ambaton Annabi
wanda ya haɗa da; salati da yabo
da kamun ƙafa a gareshi da ambaton iyalansa da sahabbansa da sauran
Annabawa. Sannan aka dubi rashin mabuɗi. Misalan da aka kawo sun tabbatar da samuwar waɗannan matakai na buɗe waƙoƙi a wannan ƙarni na 21. Kana daga ƙarshe aka kawo jawabin kammalawa.
Manazarta
Abba, M. da Zulyadaini, B. (2000). Nazari Kan Waƙar Baka Ta Hausa. Zaria: Gaskiya Corporation Limited.
Atuwo, A. A. da Bunza, D. B. (2014).
“Transformation of Hausa Poems in the 21 Century” Taron ƙara wa juna sani na ƙasa da ƙasa kan nazarin
Hausa. Sashen Nazarin Harsunan Najerya, Jami’ar Bayero, Kano.
Auta, A. L. (1986). “Gudumawar Waƙoƙin Makaɗan Baka Dangane da Adana Tarihi Kundin Digiri na biyu, Kano:
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Bunza, D. B. (2015). Aron Murya Cikin Rubutattun
Waƙoƙin Hausa A cikin Yobe Journal of Language, Literature and
Culture.Yobe; Department of African Languages Linguistics.
CNHN (2006). Ƙamusun Hausa.
Kano: Jami’ar Bayero.
Ɗanjuma, S. (1992).
“Rabe-Raben Waƙoƙin Hausa da Tasirinsu ga Rayuwar Hausawa”. Kundin Digiri na
Biyu, Kano: Sashen Koyar da Harsunan Najeriya, Jami’ar Bayero.
Dunfawa, A. A. (2002). “Waƙa A Tunanin Yara”.
Kundin Digiri na uku, Sokkwato: Sashen Koyar da Harsunan Najeriya, Jami’ar
Usmanu Ɗanfodiyo.
Dunfawa, A. A. (2014). “Makaɗan Zamani: Wani Ƙarin Kaso na Rukunin Makaɗa”. Takarda da aka gabatar a taron ƙasa da ƙasa kan nazarin
Hausa, ƙarni na 21, a Jami’ar Bayero, Kano.
Gusau, S. M. (2002). “Salo a Waƙoƙin Baka: Tsokaci Kan Turke
da Rabe-Rabensa”. A Cikin Nazari a Kan Harshe
da Adabi da Al’adun Hausa, Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya. Jami’ar
Bayero.
Gusau, S. M. (2003). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kano: Benchmark Publisher Limited.
Gusau, S. M. (2011). Adabin Hausa A Sauƙaƙe. Kano: Century Research and Publishers Limited.
Isah,
Z. (2013). “Farfaganda A Waƙoƙin Fiyano Na Hausa Daga 2003-2013”. Kundin Digri na Biyu,
Zariya: Department of African Languages and Cultures Ahmadu Bello University, Zariya.
Jamilu,
A. (2019). “Siyasa Aƙida:Nazarin Jigon Aƙida A Waƙoƙin Kabiru Yahaya Kilasik”. Kundin Digri na Biyu, Sokkwato:
Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Omar
S. (2013). Mabuɗi da Marufi a Waƙoƙin Malam Mu’azu Haɗeja A cikin Ɗunɗaye Cibiyar Nazarin
Harsunan Najeriya Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sokoto.
Sa’id,
B. (2002). “Rubutattun Waƙoƙin Hausa na Ƙarni na Ashirin a Jahohin Sokoto da Kabi da Zamfara: Nazari
a Kan Bunƙasarsu Da Hikimomin da ke cikinsu”. Kundin Digiri na Uku,
Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Usman
B.B. (2018). Ruwa Biyu: Sabon Zubin Waƙoƙin Ƙarni Na Ashirin Da Ɗaya A cikin Yobe Journal of Language, Literature and
Culture.Yobe; Department of African Languages and Linguistics.
Yahya,
A. B. (1995). “Ƙawancen Jigo Tsakanin Waƙoƙin Sarauta na Baka da
Rubutattu’’. Takarda Wadda aka Gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Yahya,
A. B. (2001). Salo Asirin Waƙa. Kaduna: Fisbas Media Services.
Yahaya,
I. Y. (1988). Hausa A Rubuce: Tarihin
Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. Zaria: Kamfanin Buga Littattafai Na Arewa.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.