Daga
Yusuf. M. Kazaure
IDAN NA YI KUSKURE DAMAN NI ƊALIBI
NE A GAFARCE NI SANNAN A YI MINI GYARA.
Tsokaci: Ni ɗalibi ne mai neman sani a koyaushe da maraba da gyara, idan na yi kuskure a gafarce ne ko na yi mummunar fahimta a fahimtar da ni.
Ni ɗalibi
ne kuma mai neman sani a cikinku, na san maganar taku ce ta manya, wadda bai
kamata mu ce wani abu ba, saboda haka a gafarce ni a bisa wannan kuskuren.
A batun gaskiya www.amsoshi.com
ya taɓo mana ciyon da
ya daɗe yana sosa mana
rai, sannan ya bayar da ingantattu kuma sahihan misalai, da hanyoyin da ya
kamata a bi domin gyara da ci gaba a zamanance.
Haƙiƙa ni kaina na taso da burin nazartar
harshen Hausa, bisa wasu muhimman dalilai, wanda hakan tasa a yanzu haka ina da
Digirin farko a fannin B.A Hausa, sai dai kash! Wallahi a yanzu sam an cire
muni sha'awar ci gaba da nazarin wannan harshe bisa wasu dalilai, wanda a yanzu
haka ina tunanin a fannin da zan yi PGD (postgraduate Diploma), in saura sheƙa.
Kaɗan
daga cikin dalilan da suka sanya ni son nazarin harshen Hausa sun haɗa da:
A- ina son wallafa litattafai, ta
yadda ko bana raye ayyukana zasu ci gaba da bayyana a doron ƙasa,
kamar yadda a yau ake tunawa da su; Alh. Abubakar Imam, da su Ahmadu Ingawa, su
Bello Kagara da sauran su.
Wlh tun a firamare na ji ina son
zama irin su, yadda suka bayyana basira da hikimarsu ta hanyar rubuta
litattafan da suka haɗa
da; Magana jari ce, da Ruwan Bagaja, da su Iliya Ɗan Maiƙarfi da sauran su.
b- Ina son na san wane ne ni,
ma'ana waye cikakken Bahaushe?
c- Ina son a fannin Hausa ni ma
ya kasance ana damawa da ni nan gaba idan lokacin mu ya zo.
d- Da sauran dalilai sun fi a ƙirga wlh.
Amma a yanzu sam an cire min
wannan sha'awar gaba ɗaya.
Bisa dalilan nan da suka haɗa
da:
a- Alokacin da muke koyan darasi
na koyi darasi da dama, dangane da malaman shashen mu da na sauran sashe
musamman a fannin Science couses, har da tambayar miyasa a Hausa, History,
Arabic ba a fiye fita da sakamako mafi daraja ba (first Class) saɓanin Science courses?
1- Daliban da suke nazarin waɗannan fannonin ba su da
ilimin cin hakan ko kuwa?
Mukan yi iya bakin ƙoƙarin
mu wajen ganin mun ci A ko B, a kwas amma cikin nufin Ubangiji sai hakan ta
gagara, wanda ba wai ba a cin makin da ya kai a ba mutum A ko B, bane a'a
sam-sam ba haka bane, amma dai a biyo ni bashin wannan......
Amma a bin mamaki a sauran
kwasa-kwasai musamman na gidan sayins basu fiye.... maki ba, akan samu A ko B,
kuma akan samu masu sakamako mafi daraja da yawa a kowace shekara a ɓangarorinsu da dama,
sosai-sosai matuƙar ɗaliban
sun yi abinda ya dace.
Amma za a daɗe ba a ji irin wannan abin
ba a fannonin Hausa, Arabic, ko History, domin tunda nake ban taɓa jin wanda ya fita da
(First Class) a History ba.
1- Ko har yanzu ba a samu haziƙin ɗalibin da zai iya ci bane?
Waɗanda
wannan batu ya ɓatawa
rai, a gafarce ni wataƙila kuskuren fahimta ta ne yasa nake ganin hakan, fahimta ta
bai zama wajibi ta zama gaskiya ba.
b- A lokacin da zan rubuta kundin bincike na
kammala Digirin farko, na zaɓi
" matanin" da zan yi bincike a kai, inda na zaɓi taken bincike mai alaƙa kai tsaye da tarihin
mahaifa ta, domin nima na fara bayar da tawa gudummawar a mahaifa ta, ta
binciko muhimman abubuwa game ta ita, amma kash ! Na fuskanci ƙalubale
da dama na rashin bani lokaci da yimin bayanin tambayoyina ga masanan, a
matsayina na ɗalibi
mai neman sani, ba alfahari ba, ban da na saka naci da ƙwawa wlh da binciken ba
zai kammalu ba.
Hakan yasa na ƙara
cire tsammani, saboda rashin ɗaukar
mutum da muhimmanci balle a ba shi gudummawar da ta dace.
c- A yanzu kana ji kana gani ko a
makarantu masu zaman kansu (private school), ba ma manyan kamfanoni ba, za a
nemi masu karatu na fannoni daban-daban amma kash sai ka ji an ce babu masu
irin karatunka.
A kwai yayana wlh har M.A Hausa
yake da ita, kuma malami ne a makarantar gwabnati amma cemun ya yi "A kwai
sanda a makarantar da yake koyarwa, sai da aka tura kowane malami semina, amma
ban da shi kaɗai, da
ya yi magana aka ce masa wai ai ban da malamim Hausa"
Abin tambayar a nan miyasa aka
ware Hausa?
a- Ba a ɗauke ta da muhimmanci bane ko kuwa?
b- Su waye suka ware malaman
Hausar, sannan ina manyan malaman Hausar da ba su bibiyi dalili ba?
c- shin hakan ba zai sanya ɗaliban su raina kwas ɗin ba, balle har su yi
sha'awar nazarin?
d- Anya hakan ba zai sanya wasu
malaman su raina Malamin Hausar ba, ganin yadda ta faru ba?
Bayan haka ina da tarin tambayoyi
da misalai wanda rubutn zai yi tsayi idan kawo su za mu yi.
Allah ya sakawa malaman mu, irin
su www.amsoshi.com, duk da Allah bai halicce mu kai ɗaya ba, da a ce malaman Hausa na koyi da irin
ayyukansa na bunƙasa harshen Hausa da wallahi da yanzu ba wannan batun ake ba.
Na san a wannan zaure akwai
malamai na da abokanan karatu, amma dan Allah ina fatan za su fahimci zancena
ta hannun dama, ba ta hannun hagu ba domin ita fahimta fuska ce, kowa da irin
tasa fahimtar, amma ni fatana a yi mini adalci wajen fahimtar manufata.
Idan a kwai wani matani da mutum
bai fahimta, kafin yanke hukumci zai iya tuntuɓa
ta domin ya ji, miye manufata sannan ya san inda na nufa.
Muna fatan Allah ya zaɓa mana abinda
ya fi alheri amin.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.