Cite this article as: Abdullahi I.S.S. & Dalha I. (2025). Kimar Mace A Ma’aunin Matakan Rayuwar Maguzawa. Zamfara International Journal of Humanities,3(3), 213-222.www.doi.org/10.36349/zamijoh.2025.v03i03.020
KIMAR MACE A MA’AUNIN MATAKAN RAYUWAR MAGUZAWA
Na
Ibrahim Sarkin Sudan Abdullahi
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato
Da
Ibrahim Dalha
Ɗalibi a
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato
Tsakure: Tun gabanin Hausawa su karɓi kowane saukakken addini mata suke da kima a
wurinsu. Manufar tabbatar da wannan hasashe shi ne ya ja hankali aka gudanar da
ƙwarya-ƙwaryan nazari saboda a ƙyallaro shi a cikin al’adun matakan rayuwar
Maguzawa na aure da haihuwa da mutuwa. Takardar ta yi amfani da karance-karance
a matsayin hanyar bincike. An ɗora
nazarin a kan tunanin Hausawa da yake cewa: “Inda aka san darajar goro nan ake
nema masa ganye.” Takardar ta yi garkuwa da wasu misalai na al’adun Maguzawa
guda goma sha biyar (15) waɗanda
suka ratsi matakan rayuwarsu na aure da haihuwa da mutuwa; saboda a tabbatar da
kimar da mace take da ita a wurinsu. Wasu daga cikin sakamakon da aka iya
hangowa a dalilin wannan bincike sun haɗa
da: Sanin kimar mace tare da tabbatar da ita a aikace da Maguzawa sukan yi, ya
taimaka ta fuskokin ɗorewar tarbiyarsu da kyautatuwar
zumuncinsu da tausaya wa junanusu tare da haɗin
kan da yake tsakaninsu. Bugu da ƙari, wannan nazari ya gano cewa, kimar da mace take
da ita a al’adun
Maguzawa ita ce ta yi tasiri matuƙa har ya zuwa bayan da wasunsu suka karɓi addinin Musulunci. Ke nan, wannan ya tabbatar mana
da abin da Hausawa suke cewa: “Daɗin
goyo shi ke sa jijjiga.”
Keɓaɓɓun
Kalmomi: Kima da Mace da kuma Matakan Rayuwa.
Gabatarwa
Maguzawa
mutane ne da suka daɗe da
sanin kimar ɗan’adam duk kuwa da kallon da ake yi musu na
waɗanda suka bambanta da mafi yawan Hausawan da
suka karɓi addinin Musulunci. Idan aka waiwayi
rayuwarsu cike take da tanade-tanaden da suke tabbatar da kiyaye haƙƙin ɗan’adam da sauran batutuwan da suka shafi zamantakewa.
Sanin kimar ɗan’adam a zamantakewar Maguzawa, shi ne ya sa
al’ada ta tilasta yara su riƙa mutunta manya tare da taimaka musu ta fuskokin riƙa musu kayan da ke
hannunsu ko kuma kama musu wani aiki domin su samu sauƙi. Haka abin yake ga manya, su ma al’ada ta tanadar musu da haƙuri da tausayawa ga
lamuran da suka shafi yara. Irin wannan tarbiya ita ce ta yi amo a zamantakewar
da take tsakanin miji da mata. Hasali ma mata suna cikin wani ɓangare da al’adar Maguzawa ta tanadar musu da wata kima
ta musamman. Ga al’ada, sanin kimar ɗan’adam
da kiyaye haƙƙoƙinsa shi yakan haifar da
tausayi a tsakanin al’umma. Hakan ya sanya Nuhu (2020:395) ya yi amannar cewa,
zaman tare yana buƙatar
masu zaman da su tausaya wa juna a duk wani abu da zai shafi abokin zama. Duk
da kallon da wayewar kan zamani take yi wa wasu daga cikin al’adun Maguzawa na
gargajiya, akwai abin koyi daga cikinsu, musamman waɗanda suka shafi kiyaye kimar mace. Ɓatan dabon da wasu al’adun Maguzawa na kiyaye
kimar mace suka yi saboda guguwar sauye-sauyen zamani, shi ya haifar da kallon
da wasu suke yi musu na mutanen da suka ƙanƙame ɗabi’unsu
na gargajiya. Hasali ma wasu da suke da masaniyar Maguzawa suna gudanar da noma
da wasu aikace-aikacen gida tare da matansu, sai suke tunanin suna barin su a
cikin ƙuncin
rayuwa. Sun kasa gane cewa, tukunyar da ake tuƙa farin tuwo a cikinta, bayanta baƙi ne.
Maƙasudin wannan takarda shi
ne, fayyace wasu abubuwan da suka shafi kimar mace a al’adun Maguzawa na matakan
rayuwa. An yi wannan tunani ne saboda a toshe wata kafa ta ilimi da aka hango.
Baya ga haka kuma, nazarin zai ƙara tabbatar da yadda Maguzawa suke da ƙoƙarin kiyaye kimar mace tun kafin guguwar rajin
kare haƙoƙin mata da take kaɗawa a wannan lokaci ta bayyana. Nazarin ya yi la’akari da
cewa, ayyukan da Ibrahim, (1982 da 1985) da Abdullahi (2008) da Nuhu (2020)
suka gudanar ba su keɓe wani
fasalin da suka yi bayanin kimar mace a Maguzance ba. Wannan dalili ya sa aka
ga dacewar cike wannan giɓi na
ilimi, saboda a tabbatar wa da masu rajin kare haƙƙoƙin mata cewa, Maguzawa sun daɗe da wannan wayewar tun kafin su haɗu da kowace al’umma.
Hanyoyin Bincike
Nazari kan lamarin da ya
shafi rayuwar Maguzawa yana buƙatar tuntuɓar wasu daga cikin ayyukan da aka gudanar a
kansu. Wannan dalili ya sa aka yi wa takardar guzurin da ya kai ga leƙa wasu daga cikin ayyukan da suke da dangantaka da al’adun Maguzawa domin su zama jagora ga bayanan da aka fito
da su. Takardar ta samu nasarar yin ido biyu da wasu daga cikin ayyukan da aka
gudanar a matakan digiri na uku da na biyu da kuma na ɗaya. Har wayau, an ci nasarar leƙa wasu
maƙalu da aka gabatar a mujallun ilimi waɗanda suka tattauna batutuwan da suke da alaƙa da binciken da aka gudanar. Ayyukan da aka samu damar
kaiwa gare su, an same su ne ta hanyar leƙa ɗakunan karatu daban-daban.
Hanyar Ɗora Aiki
A wannan bincike, hanyar ɗora aiki tana nufin tafarkin da magabata suka
samar domin zama jagora ga ayyukan ilimi, saboda nazarce-nazarcen da aka
gudanar su samar da kyakkyawar alƙibla ga al’umma. A ƙoƙarin
ganin wannan nazari ya samu wannan tagomashi, an ɗora shi a kan tunanin Bahaushe da yake cewa: “Inda aka
san darajar goro nan ake nema masa ganye.” An yi amfani da wannan tunani ne
saboda dacewarsa da yanayin yadda Maguzawa suka san daraja da kimar mace, inda
suke ba ta wani matsayi na musamman a al’adunsu na matakan rayuwa (aure da
haihuwa da mutuwa). Kimar da mace take da shi a wurin Maguzawa, shi ne ya sanya
al’adarsu ta yi wani tsari na musamman wanda ba ta yi wa namiji ba. Kenan, a
wannan bincike, mace ita ce tamkar ɗan
itaciyar “goro” wanda ga al’ada akan lulluɓa masa ganye da manufar darajanta shi, saboda ba a son ya
bushe. Sakamakon bushewarsa kamar walaƙantawa ce a gare shi.
Bayanin Fitulun Kalmomin Taken Bincike
Ƙoƙarin wannan takarda na yin susa a gurbin da yake ƙaiƙayi, shi ne ya sa aka ware
wannan muhalli domin fito da ma’anonin kalmomin da suka
gina taken da aka sanya mata. Kalmomin da aka bayyana ma’anoninsu saboda su zama jagora wajen fahimtar wannan
takarda su ne: Kima da mace da matakan rayuwa.
Kima
Kima dai kalma ce da
Hausawa suke amfani da ita wadda take da ma’anar “daraja” ko kuma matsayi. A
wannan takarda, kalmar kima tana nufin darajar da mace take da ita a tsarin
matakan rayuwar Maguzawa. Hakan bai rasa nasaba da tuntuɓar wasu Ƙamusoshi na Abraham
(1977:626) da CNHN (2006:311) inda aka gano cewa, ma’anonin da suka bayar duka sun yi tarayya da juna.
Mace
Mace kalma ce da take nuna
jinsin da yake kishiyantar namiji. Bugu da ƙari,
Newman (2020:168) da CNHN (2006:311) duka sun aminta da cewa, mace kishiyar
jinsin namiji ce. Don haka CNHN (2006:311) ya bayyana cewa, kalmar mace tana
nufin jinsin halitta na mutum ko dabba mai ɗaukar ciki ta haihu, kishiyar namiji. Har wa yau, aikin
Ingawa (1984:1) yana da ra’ayin cewa, “Macen mutum halitta ce wadda Maɗaukakin Sarki Allah ya yi wadda take ta
bambanta da halittar namiji. Dukkan mata na duniya suna da wasu abubuwa na daga
halittun jiki iri ɗaya, sai dai kawai wata
macen ta fi wata girma, ko kuma ƙanƙantar
abin da aka halitta, ko kuma ta fi ta farar fata ko baƙi.”
Matakan Rayuwa
Ana iya bayyana matakan
rayuwa da ma’anar wasu tsare-tsare na al’ada wanda mutum yake shiryawa daga
farkon rayuwarsa zuwa ƙarshenta. Bunza,
(2013:426) ya bayyana cewa, a falsafar al’ada,
kowane mutum yana hawa matakai uku a rayuwarsa. Idan muka zura wa waɗannan matakai ido, suna da tsari kamar haka:
i.
Idan aka haifi mutum ya
kai munzalin aure, ya kammala mataki na farko.
ii.
Mataki na biyu kuma shi
ne, idan ya haihu, ya sami ɗa ko ɗiya.
iii.
Baya ga wannan, matakin da
zai shiga na mutuwa shi ne na ƙarshe a rayuwar ɗan’adam. Wannan dalili ya sa manazarta suka haƙiƙance cewa, ɗan’adam yana da tsarin matakai uku a
rayuwarsa. Shi ne suke taƙaita su da matakan rayuwa
na aure da haihuwa da mutuwa.
Muhallin Mace a Matakan Rayuwar Maguzawa
La’akari da bayanan da aka
gudanar a muhallin da ya gabata, an tsara fayyace kimar da mace take da ita a
rayuwar Maguzawa ta hanyar matakai guda uku. Mataki na farko shi ne na aure sai
aka shiga na haihuwa, sannan aka ƙarƙare da
na mutuwa.
Kari a Wurin Gaɗa
Gaɗa dai
wasa ne da ‘yan mata suke gudanarwa domin nishaɗantar da
junansu a lokacin da suke cikin nishaɗi. A ganin CNHN (2006:149) wasa ne na
‘yan mata na waƙa da tafi
da ‘yan
tsalle-tsalle. Ƙoƙarin Maguzwa na tabbatar da
mace tana da kima a wurinsu, idan ‘yan mata
suna gaɗa, shi ne
ya sanya samari sukan taru su yi wa budurwar da suke ƙauna karin kuɗi da
manufar ta fito ta yi rawa a gaban makaɗi. Bugu da ƙari, kimar da mace take da shi a wurinsu
ita ta sanya hatta makaɗin da yake cashe kiɗa ga ‘yan matan yakan amfana da kyautar kuɗi ko wani
abu mai daraja a lokacin da suke wasan gaɗa. Idan babu mace a wurin gaɗa, wasan
ma ba zai gudana ba ballantana ya yi armashin da za a sami kari na kuɗi ko wani
abu mai daraja.
Toshi a Wurin Neman Aure
Toshi dai
wata nau’in kyauta ce da namiji ko wani nasa yakan bayar ga macen da yake da muradin aura
da manufar nuna so
da ƙauna da kuma jawo hankalinta ko na wani nata domin ƙara wa dangantakarsu tagomashi. Kimar mace a wurin Maguzawa ya sanya suke ba wannan al’ada muhimmanci, inda akan fara ta tun daga ranar farko da aka haɗu
tsakanin masoyan juna har zuwa lokacin ɗaura aure. Toshi bai tsaya ga ba da
kuɗi kawai ba, aikace-aikacen
da saurayi yakan yi ko wani nasa ana ɗaukarsa
a matsayin toshin yarinyar da aka nuna ana so da aure. Duk wani aiki na
kyautatawa ga iyayen yarinyar da yake ƙauna kamar noma da sauran
aikace-aikacen gida na yau da kullum ana kallonsu a matsayin toshi. Kimar da
mace take da shi a wurin Maguzawa, shi ne ya sa al’adar toshi ta samu karɓuwa matuƙa. Tun daga lokacin da
iyayen yaro suka nuna suna sha’awar haɗa shi da wata yarinya suke fara bayar da
toshi. Har ila yau, magabatan yaro sukan samu lokaci na musamman su tanadi
wani abu da za su kai gidan surukan ɗansu.
Duk lokacin da ake wani buki a gidansu yarinyar da suka yi wa ɗansu kame da ita, sukan yi ƙoƙarin bayar da gudunmawa
har sai inda ƙarfinsu ya ƙare. Ga al’ada, kowace ranar kasuwar da ya san budurwar da yake so tana ci sai ya nemi abin da ya kai ya sayar don ya yi mata toshi. Yayin da budurwa ta aminta da saurayi ya tafi gidansu, a
duk lokacin da ya je zance ba zai je hannu sake ba. Dole ne ya nemi abin da zai
bayar. Idan kuma wasu bukukuwa sun tashi na danginta nan ma sai inda ƙarfinsa ya ƙare. Kimar mace ta ɓangaren ba da toshi a wurin Maguzawa ba ta kaɗaita ga bayar da wani abu ba. Gungun abokan
masoyan mace (samarinta) daban-daban sukan haɗu su yi ta karakaina wajen kai gayyar aiki a gonakin
iyayenta. Hakan yana tabbatar wa da iyayen mace cewa, ‘yarsu tana da tagomashin
samari masoya. Kimar mace ta sanya iyayenta sukan ci albarkacinta, inda samari
sukan yi musu toshi na ayyukan gona da sauransu.
Tsarance
Wata
al’ada ce ta Maguzawa inda saurayi da budurwar da zai aura za su kwana a kan
shimfiɗa ɗaya ba
tare da wani tunani na lalata ya kasance a tsakaninsu ba. Kowane ƙauye ko kowace ƙasa ta Maguzawa da irin fahimtar da kuma tsarin da al’adarsu ta tanadar wa tsarance. A tsarin
zamantakewar Maguzawa, duk saurayin da ya kasa yaƙi da zuciyarsa a lokacin tsarance har ya
taɓa ko da
hannun budurwar ne, mutuncinsa ya zube a wurinta da iyayenta da abokansa da ma ƙawayenta. Sakamakon haka za
su riƙa
kallonsa a matsayin marar amana, kuma bai san kimar macen da zai aura ba.
Hasali ma hakan kan iya sanyawa al’umma su tsangwame shi ta yadda zai kasa sake jiki saboda kunya.
Idan lamarin ya yi tsanani ma har barin garin sai ya yi,
domin baya ga tsangwama daga iyaye da abokai, budurwar da ya yi wa
haka ma ba za ta sake yarda da shi ba.
Al’adar Aron Amarya
Ga al’adar Maguzawa, zaman
da amarya take yi a gidan lalle, maƙunshiya za ta yanka wa ‘yan matan amarya ɗan
akuya, a ba su su ci, ita kuma ta ɗauki
karfata ɗaya (ƙafar
akuya ta gaba). Idan akwai wata maƙunshiyar ita ma haka za ta
yi kafin a mayar da aron amarya. Wani lokaci akan samu mai aron amarya fiye da ɗaya, musammman idan amaryar tana da dangi da
yawa. Hakan kuma wani abin alfahari ne a wurinta da kuma danginta. Wannan
al’ada tana gwada kimar da mace take da ita a wurin Maguzawa. Wasu daga cikin
hikimar da aka iya ganowa ta kimar mace a wannan al’ada sun haɗa da: Kimar mace ta sanya danginta na ɓangaren uba da na uwa suke rububin ɗaukar aron ta. Daɗin daɗawa, samun masu aron
amarya da yawa yana gwada yawan dangin da amarya take da shi, sannan kuma yana
tabbatar da kimar da mace take ta shi a wurin Maguzawa. Kyautatawar da mai aron
amarya take mata tare da ƙawayenta wata madogara ce
da take ƙara tabbatar cewa, mace tana da ƙima.
Idan an lura, namiji (angon) da zai yi aure babu wani bayani da yake nuna ana
yi masa irin wannan hidima a al’adun Maguzawa.
Wankan Amarya
Abin da
ke gaba bayan ɗaura aure ga al’adar bukin Maguzawa shi ne wankan amarya.Wannan al’ada cike
take da hikimar nuna kimar mace a idon Maguzawa. A tunanin Maguzawa, dole ne a
tsabtace mace kafin a kai ta gidan mijnta, saboda ta shigo wani sabon yanayi na
sabuwar rayuwa. Ana gudanar da wankan amarya da manufar wanke ƙazantar da ta ɗauka ta
budurci da zaman gidan iyaye, saboda a shirya yadda za ta yi zaman gidan miji.
Wankan amarya yana tabbatar da cewa, mace ta samu sauyin ‘yanci, inda yanzu za
ta zauna a ƙarƙashin miji maimakon iyaye.
Don haka ita ma ana kallon ta ne a matsayin uwa, maimakon yarinya. Kenan,
wankan da akan yi wa amarya yana alamta sauya sabuwar rayuwa ne a gare ta. A
cikin al’adar
wankan amarya na Maguzawa, sukan cuɗanya ruwan da ganyen yaɗiya.
Hakan yana da nasaba da tunanin da suke da shi na cewa, cuɗanya
ruwan da ganyen yaɗiya saboda ya yi yauƙi ta yi
ta yaɗuwa a
gidan da ta je zaman aure. Kimar mace ya sa mata ne suke gudanar da wannan
al’ada, saboda haka suke taruwa, in ban da yara da kuma wasu tsirarun samari da
ba a rasa ba. Kuma samarin ba koyaushe suke zuwa ba. Yanayin yadda ake wankan
amarya tare da ɗaura mata farin saƙin zani,
kan sa danginta yin kukan rabuwa da ita, tare da nuna takaicin barin gidansu.
Duka waɗannan
suna nuna kimar da mace take da shi a idanun Maguzawa. Wani abin armashi, babu
inda al’adarsu ta tanadi wankan ango kamar yadda ake na amarya.
Kai
Bante
CNHN(2006:36) ya bayyana
kai bante da, “Kai budurci.” A al’adar auren Maguzawa yana daga cikin abin
farin-ciki da murna ga mace da iyayenta har ta yi aure ba tare da wani namiji
ya taɓa saduwa da ita ba, shi ne
sukan ce wance ta kai ɗiyaucinta. Kamar yadda a ɓangare ɗaya kuma
yake zama abin baƙin ciki ga iyaye da dangi
ga wadda ta taɓa yin lalata. Sanin kimar
da ke tattare ga mace ya sanya Maguzawa suke ƙoƙarin tabbatar da nesantar aikata lalata duk kuwa da shaƙuwar da za su yi da juna. Tsoron abin kunyar da za a iya
shiga a dalilin lalata shi ne ya sa mata suke tsoron aikatawa, saboda yakan
rage kimarta da ta iyayenta a idon al’umma.
Kasancewar ɗan’adam tara yake bai cika
goma ba, Maguzawa suna da wasu hanyoyi da suke amfani da su domin tabbatar da kimar
macen da ba ta taɓa lalata ba. Misali,
Maguzawan Kaibaki da na Ƙwanƙi duka suna amfani da wasu
tsafe-tsafensu da suke haɗawa da ɗan’akuya
wajen tabbatar da kimar mace na cewa ta kai bantenta. Su kuwa Maguzawan Kaita
ango ne da kansa yake bayyana cewa amaryar da ya aura ta kai bantenta ko ba ta
kai ba. Abdullahi (2008:194) ya rawaito cewa, akwai manazartan da suke da
ra’ayin ana iya raba tsafin da Maguzawa suke yi na tabbatar da mace ta kai ɗiyaucinta
dangane da abin da suke bauta wa. Masu bautar Kurmawa suna da nasu
tanade-tanaden; kamar yadda masu amfani da tsafin Uwargona suke da nasu. Abin
dai da ake so a fahimta a nan, shi ne, hikimar da ke cikin tanade-tanaden
tabbatar da mace ba ta sadu da wani namiji ba in ba wanda aka aura mata ba, shi
ne domin a nuna kimar da ke gare ta. Wadda ta taɓa saduwa
da namiji kafin aure kuwa, al’adar Maguzawa ta tanadi wasu abubuwa da za su
tabbatar mata da zubewar kimarta a idanun al’umma. Wasu daga cikinsu sun haɗa da:
Kunyatar da iyayenta da saurayin da zai aure ta da kuma ita kanta akan cewa ta
ci amana. Akan rage wa mace dukiyar auren da aka tanadar mata, saboda zubewar
kimarta a dalilin lalatar da ta aikata. Bugu da ƙari, akan hana kowane saurayi ya aure
ta, sai dai ta auri tsoho, wani ma zai iya kaiwa shekarun kakanta. Haka kuma,
takan sami rashin tabbas a rayuwarta, musamman idan aka doge sai an gudanar da
wasu al’adunsu na
bukin aure. Al’ada ta
tanadi huda ƙwarya a
sanya a ɗakinta ko
a kai ta gidan miji tare da kuikuyo yana nuna alama ce ta rashin kima a
Maguzance. Wannan ya nuna Maguzawa suna lura da kimar da ke ga mace, don haka
suka haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen tabbatar da ita. A ƙoƙarin tabbatar da wannan ƙimar, mace da iyayenta sukan
tashi tsaye wajen ganin sun sami wannan nasarar.
Ɗaukar Amarya
Kiyaye kimar mace da
Maguzawa sukan yi, shi ne ya sa a al’adarsu amarya take samun tagomashi a
lokacin da za a kai ta gidan mijinta yayin da ake shagalin bukin aure. Wasu
daga cikin al’adun da ake gudanarwa waɗanda
suke nuna kimar da mace take da ita a wurin Maguzawa sun haɗa da: Dangin miji maza da mata, babba da yaro sukan zo ɗaukar amarya; kamar yadda abokan ango sukan zo. Abokin
ango shi yakan ja goɗiyar da
za a ɗora
amaryar a kai
domin a kai ta gidan mijinta. Ana raka amarya gidan mijinta ne da kaɗe-kaɗe da waƙe-waƙe, wani lokaci ma akan haɗa da busa algaita. Idan ba a sami goɗiyar da za a ɗora amarya a kanta ba, to wasu Maguzawan sukan goya ta a baya. Za a sami mata daga cikin dangin ango su riƙa goya amaryar. Idan wannan ta gaji sai ta ba wata har a kai ta ɗakin mijinta. Wasu
kuwa abokin ango ne zai ɗauke ta ya saɓa a wuya zuwa
gidan mijinta. Wasu kuma idan kusa ne da ƙafarta za ta tafi. Daga
cikin masu raka amaraya, akan sami masu hawa dawaki da jakuna. Kimar amarya a
wurin Maguzawa ya sa ake ɗora ta a kan goɗiya ko a
goye ta a baya kamar wata sarauniya.
Zaman
Aure
Shi ne haƙiƙanin rayuwar da take
gudana ta fuskar zamantakewa a tsakanin miji da mata. Duka wanda ya yi aure ana
sa ran a ga kyakkyawar zamantakewa mai ɗorewa a
tsakaninsa da wadda ya aura. Ga al’adar Maguzawa, ba a samun bambanci ta fuskar
yanayin zaman aure. Tun
daga ranar da aka kai amarya, da
zarar jama’a sun watse ta fara zaman aure ke nan. Maguzawa ba su gina wa ango
da amarya gida su kaɗai daga shi sai ita, ko da kuwa yana da arzikin
da zai iya gina gidan kansa. Dole ne akwai mutane a cikin gidan suna zaune tare
da su musamman iyayen miji. Sukan yi aikin gona tare da mijinta, sannan kuma ita ma
tana da wata gona da takan yi nata aikin na ƙashin
kanta. Duka abin da ta noma na gonarta nata ne, kuma tana iya amfani da shi a gidan
a ci in ta ga dama. Tana iya sayarwa ta yi sabgar dangi, ko ta maƙwabta. Baya ga haka kuma, tana iya sayar da
abin da ta noma ta sayi ’yan awaki ta yi kiwo ko kuma ta sami jarin yin wata
’yar sana’a a lokacin rani. Wannan dama da ake ba mata tana taimaka
musu wajen mallakar abin hannunsu inda suke tsayawa da ƙafafunsu ba tare da sun dogara da
mazansu ba. Baya ga haka kuma, hakan ya fito da kimar da mace take da ita, ta
yadda Maguzawa ba su tauye matansu ta fuskar taimaka musu wajen ginuwar
tattalin arzikinsu.
Guɗa
Wata nau’in ɗaga murya ce da mata sukan yi a lokacin da
suke cikin wata murna bisa wata ni’ima da ta same su. Hasali ma Hausawa sukan
yi mata kirari da, “In ka ji guɗa da
labari.” Don haka suka aminta da cewa, “guɗa ba a rangaɗa wa
asara.” CHNN (2006:172) ya bayyana ta da, “ɗaga sauti da ƙaraji wanda galibi mata
kan yi, ta hanyar amfani da baki, da hanci don nuna murna wajen biki ko wucewar
sarki ko jin wani labari mai daɗi, ko
ganin wani abu da ake jiran zuwansa.” Wannan ma’ana ta ci karo da kalmar da
Newman, (2020:92) ya fassara, inda ya yi ƙoƙarin
bayyana ma’anarta da wata kalmar
Turanci da take nuna ɗaga murya mai ƙara da niyyar murna ko baƙin ciki.
Ga al’adar Maguzawa, murna ce take sanya a yi guɗa, baƙin ciki idan ya faru kuka
akan yi. Kimar mace a wurin Maguzawa ya sanya sukan yi guɗa guda huɗu idan
jaririyar da aka haifa jinsinsu ce, amma idan namiji ne akan yi guɗa guda uku. Falsafar da ke cikin bambancin
adadin guɗar da ake wa mace da
namiji sun haɗa da: Kara ga mai haihuwa,
saboda an samu jinsinta. Son kai ga mata, saboda su nuna jinsinsu aka samu. Ƙoƙarin da mata suke na
tabbatuwar zamantakewa ta fuskar ɗawainiyar
riƙon gida da kula da duk wasu ayyuka da sukan wanzar da
ingantacciyar rayuwa a gidan da suke. Haka kuma, suna alamta cewa, al’aurar mace ta fi ta namiji yawa.
Ba Mace Damar Zaɓen Suna
Kasancewar al’adun
Maguzawa suna bambanta daga wuri zuwa wuri a kan sha’anin tsare-tsaren da suke
gudana waɗanda suka shafi raɗa sunan abin da aka haifa. Al’adar Maguzawan
Kainafara tana ƙunshe da tabbatar da kimar
mace yayin da aka zo raɗa wa abin haihuwar da aka
samu suna. Bayan abin haihuwar da aka haifa ya ɓace tun daga ranar haihuwa zuwa kwanaki goma sha huɗu. Ranar da kwanakin suka cika, bayan sun
tabbatar da abin da aka haifa ya dawo daga wurin tsafinsu, sai wasu tsofaffi
maza waɗanda adadinsu ya kai guda
goma su zauna a gindin wata bishiya da ke ƙofar
gidan da aka yi haihuwar. Tsofaffin za su sami karare su yi zane a kowane ɓari na su, sai su kira ungozoma su ce ta kai
wa maijego ta zaɓi guda ɗaya daga cikinsu. Idan Ungozoma ta dawo musu
da wanda ta zaɓa, sai su yi la’akari da
nau’in zanen da yake jikin karan su bayyana sunan abin da aka haifa, tare da ba
ta umarnin ta koma ta bayyana wa mai haihuwar. Kodayake, ba za a bayyana sunan
ba sai ranar aurensa ko aurenta (abin da aka haifa ɗin). Don haka za a yi ta kiran jaririn/jaririyar da laƙabin da kakanni suka sanya masa. Su kuwa Maguzawan
Kudancin Katsina ba sa raɗa wa jaririn/jaririyar da
aka haifa suna sai bayan kwanaki arba’in da haihuwa. Idan aka zo zanen sunan,
mata dangin uba da na mahaifiyar jaririn/jaririyar ne suke haɗuwa a gidan da aka yi haihuwar. Suna kiran
wannan al’adar da Kantsaki. Lokaci da yanayin da aka haifi jariri/jaririyar, su
ne suke tsayawa a matsayin mizanin sunan da ya dace a sanya masa. Keɓe mahaifiyar jariri ko jaririyar da aka haifa
ko kuma wasu dangin mahaifansa mata wajen tabbatar da sunan da ya dace gare su
ya fito da kimar da mace take da shi a wurin Maguzawa.
Ba Mace Damar Sauya Miji In Ba Ta Gamsu Ba
Yana daga cikin kimar da
Maguzawa sukan ba mace na ba ta dama ta sauya mijin da za ta aura idan ba ta
gamsu da shi ba. Maguzawa sukan ƙulla aure ta hanyar yi wa
miji kame tun yarinya tana ƙarama. Wani lokacin idan
yaran sun girma, akan samu bambancin ra’ayi a
tsakaninsu, inda wani daga cikinsu yakan samu sauyin tunani dangane da alƙawarin kamen da iyayensa suka yi masa. Wani lokaci kuma,
waɗanda suka ƙulla alƙawarin ne wani daga
cikinsu yake mutuwa, dalilin haka idan wani ya shigo sai ya ɗauke wa yarinyar hankali ta rabu da wanda aka
yi mata kame tun da farko. Idan haka ta faru, akan sami wani daga cikin manya
ya ba mace damar ta zaɓi wanda take so ta aura a
cikinsu, saboda ƙoƙarin
daidaita su da aka yi abin ya ci tura. Ga al’adarsu, iyayen macen ne suke biyan abin da aka kashe mata
na kuɗi ko kuma wasu kaya na
zahiri da ya taɓa ba ta; sai dai ba a
biyan aikace-aikacen da ya yi wa iyayenta.
Har wayau, yana daga cikin
dalilan ba mace dama ta sauya miji a wurin Maguzawa, idan ta gaji da miji ko
kuma ta ji ba ta son sa aka kuma tabbata akwai wanda take ƙauna.
Idan haka ta faru, akan gane haka idan ta fito, ana tsammanin yaji ta yi, amma
ba ta je gidan iyaye ba, tana gidan wani. Wannan wanda ta koma gidansa shi ne
sabon miji, sai ya nemi tsohon mijinta ya biya shi abin da ya kashe na dukiyar
aure. Sakamakon yana da wahala ya iya biyansa dukkanin abin da ya kashe, yana
iya karɓar wani abu a wurin wanda
matar ta koma gidansa. Misali, kamar jaki ko doki ko kuma saniya. Sukan yi haka
ne saboda tsohon mijin ya rage hasara. Duk da haka, idan tana da ciki, ya zama
na sabon mijnta da ta koma gidansa. Idan kuma suka sami saɓani da sabon mijin bayan wani lokaci ko kuma shekaru,
tana da damar ta koma gidan tsohon mijinta ba tare da an biya shi dukiyar
aurensa ba. Idan kuma tana so ta koma babu wani saɓani a tsakaninsu, takan gudu ne a ɓoye ba tare da sanin sabon mijin ba. Don haka a ɓoye za ta kwashe kayanta tare da ‘ya’yanta su
koma gidan mijinta na baya. Hakan ya sa take kwashe kayan ta bayan gida tare da
taimakon ‘ya’yanta ba tare da sanin kowa ba. Wannan al’adar ta tabbatar da tilasta mace ta zauna da mijin da ba
ta so ba ya daga cikin ɗabi’un Maguzawa. Bugu da ƙari, hakan ya nuna Maguzawa sun bar mata cikin walwala ba
tare da sun tauye su ba saboda kimar da suke da ita.
Biko Idan Mace ta Yi Yaji
Biko dai
wata hanya ce ta al’ada da Maguzawa suke amfani da ita wajen sasanta ma’auratan
da suka sami saɓani a tsakaninsu, ta hanyar ba macen da ta tafi yaji haƙuri domin ta dawo gidan
mijinta. CNHN (2006:46) ya fassara kalmar biko da, “neman dawo da matar da ta yi
yaji.” Shi kuwa
Rambo, (2007:119) yana da ra’ayin
kalmar biko ta samo tushenta ne daga “bi” da ake wa matar da ta yi yaji domin ta
dawo ɗakinta. A
ɓangare ɗaya kuma,
biko yana nufin hanyar sasantawa a tsakanin namiji da mace bayan sun ɗan samu
wani saɓani da ya
haifar da ta bar ɗakinta (Rambo, 2021:697). A zamantakewar rayuwa, duk kyawun da zama ya yi
tare da juna a tsakanin ma’aurata, wani lokaci akan iya samun cin karo da buƙatun juna. Hakan kuma shi
yake haifar da samuwar saɓani a tsakanin ma’auratan. Duk lokacin
da aka samu matsala tsakanin mata da miji, idan lamarin ya yi tsamari, macen
takan tafi gidansu ko kuma wurin wani daga cikin dangin iyayenta a matsayin
yaji. Takan yi haka ne da manufar kai kukanta dangane da wani abu da aka yi
mata wanda bai dace ba. Idan haka ta auku, akwai wasu tanade-tanade da al’ada
ta tsara waɗanda akan
yi su domin daidaita tsakaninsu. Wasu daga cikin hanyoyin da Maguzawa sukan bi
idan haka ta faru sun haɗa da: Iyayen miji ko shi kansa ko kuma
abokansa sukan bi matar gidan iyayenta su bayar da haƙuri saboda a rarrashe ta domin ta dawo.
Har wa yau, sukan sanar da iyaye domin sanin halin da ake ciki, saboda a fara
laluben hanyoyin sulhunta su tare da ba ta haƙuri. Maganganun da suka shafi rarrashi
(lallashi) da bayar da haƙuri su ne
suka fi shahara a lokacin da aka je wurin biko a al’adar Maguzawa. Waɗanda suka
je bikon sukan kira miji su ja hankalinsa ta hanyar ja masa kunne, saboda kauce
wa maimaituwar abin da ya faru. Sakamakon cewa, a al’adar Maguzawa, kasawa ce
magabatan miji a riƙa yawan
ganinsu suna zuwa bikon matar ɗansu. A ɓangare ɗaya kuma,
al’adar Maguzawa ta aminta da miji ya kai ƙorafin matarsa idan tana abin da bai
dace ba. Hasali ma, magabata sukan yi godiya tare da alƙawarin jan kunnenta ga muhimmancin da ke
tattare ga bin dokokin mijinta. Baya ga haka, suna ganin rashin hikima ga mace
ta rayu ba a gidan mijinta ba, sai dai idan wani yanayi na mutuwa ya gitta.
Wannan dalili ya sa wasu iyayen idan suka ga jan kunnen bai ba da mafita ba,
sukan haɗa da
magani domin a gudu tare da tsira tare.
Shawartar Bazawara Game da Wanda Take So
ta Aura
Bazawara
ita ce matar da ta yi aure suka rabu da mijin da ta aura, walau ta hanyar saki
ko kuma mutuwa. Idan mace ta fara zawarci, takan sami manema da dama waɗanda suke
nuna sha’awarsu ga aurenta. A lokacin da bazawara take ƙoƙarin tsayar da wanda take so, a tsarin al’adar Maguzawa ba a tursasa ta
dangane da wanda ya kamata ta aura. Sukan dai ba ta shawara, saboda yaƙinin da suke da shi na cewa,
tana da masaniyar yanayin zama da miji. Bazawara tana da damar sauya ra’ayi a kan namijin da ta yi wa
alƙawarin aure
idan ta ji ba ta son sa, sai dai daga baya a zo a sasanta a mayar masa da a bin
da ya kashe.
Kulawa da Macen da Take Takaba
Bayan
tabbatar da mutuwar mamaci, babu abin da ke gaba idan an binne shi sai shiga
takaba da matansa za su yi. Maguzawa suna fara takaba ne bayan kwanaki bakwai
da rasuwar mijinsu, wato ranar da ake ƙare zaman makoki. Lamarin kwanakin da mace take ɗauka na
zaman takaba ya danganta daga yanayin al’adar wuri. Misali, Ibrahim (1982: 177)
ya nuna akwai Maguzawan da suke shafe watanni bakwai da kwana goma a matsayin
kwanakin zaman takaba. Su kuwa Maguzawan Kainafara da Ƙwanƙi da da kuma Lezumawan Babban Kada duka
suna shafe watannin biyar suna zaman takaba. Saɓanin
Maguzawan Gidan Bakwai, tasu al’adar ta zaman takaba tana kai adadin watanni
shida. Darussan da ke cikin zaman takabar Maguzawa su ne, macen da take zaman
takaba tana samun kulawa matuƙa, saboda
haka takan kasance a cikin gida tsawon waɗannan watanni ba tare da zuwa ko’ina ba.
Akan ɗauki
matakan lura da ita saboda kiyaye kimarta da ta mijinta da ya mutu. Sakamakon
ba sa ƙaunar ta
aikata wani abin kunya da zai zubar da kimarta da ta mijinta da ya mutu da kuma
ta zuriyarsu. Hakan ya sa hatta aikace-aikace ma ɗauke mata
ake yi.
A ɓangare ɗaya kuma,
Maguzawa sun lura da maganar Hausawa da take cewa: “Da abokin daka akan sha
gari.” Wannan dalili ya sa a al’adar Maguzawan Kaibaki da ke Fago maza suke wa
matansu da suka rasu takaba. Yanayin takabar maza ya bambanta da yadda mata
suke gudanarwa. Idan namiji ya tsinci kansa a yanayin mutuwar matarsa, yakan
shiga takaba ne bayan kwanaki bakwai da mutuwar matar. Takabar namiji ba ta
wuce ta juya rigarsa ya sanya ta baibai na tsawon kwanaki uku ba. A cikin
kwanakin da yake takabar, ba a so ya gudanar da wasu aikace-aikace da suka
danganci zuwa gona da makamantansu. Duka wannan al’ada, tana tabbatar da kimar
da mace take da shi a wurin Maguzawa.
Auren Matar Mamaci
Ga
al’adar rayuwa, bayan an yi aure an haihu babu wani mataki da ke gaba kuma sai
na mutuwa. Duk da yake lamarin mutuwa ba daɗi ne da
shi ba, amma kasancewarta abin da babu makawa sai ya riski mai rai, shi ne ya
sanya ta zama mataki na ƙarshe a
rayuwarsa. Yana daga cikin al’adun
Maguzawa, duk macen da mijinta ya mutu tana da damar yin wani auren musamman
idan tana da sauran shekarun da wani zai iya aurenta. Idan kuma ta tsufa da
yawa, takan dangana ga yanayin da ta tsinci kanta ta ƙarasa rayuwarta ba tare da sake wani
sabon aure ba. A tsarin zamantakewar Maguzawa, alhakin aurar da wadda mijinta
ya mutu ya rataya a kan dangin mijinta ne ba iyayenta ba. Dangin mijinta da ‘ya’yanta (idan akwai manya a
cikinsu) sukan yi tsayin daka wajen nemo mata wanda ya dace da ita. Abin da
yake nuna kimar mace a wannan al’ada tasu shi ne, dangin mijinta da ya rasu za
su yi bakin ƙoƙarinsu wajen tabbatar da
cewa, mijin da suka aura mata zai kiyaye darajarta kamar yadda ɗan’uwansu
ya yi mata. Don haka ba za su yarda su aurar da ita a hannun wanda zai tozartar
da ita ba. Sakamakon suna tunanin cewa, tozartar da ita tamkar cin amanar ɗan’uwansu
ko mahaifinsu ne da ya mutu. Tabbatar da hakan ya sanya tun daga nema zuwa ɗaurin
aure da ɗaukar ta
zuwa ɗakin
sabon angonta, a ƙofar
gidan mijinta da ya mutu ake gudanar da waɗannan
al’adu.
Bugu da ƙari, a duk lokacin da macen
da mijinta ya mutu ta fita daga takaba, akan gudanar da buki, inda ‘yan’uwa da abokan arzuki sukan zo
su taya ta murna. Sukan gayyaci makaɗi ya zo ya kwana yana buga gangarsa,
mahalarta taron kuma suna tiƙar rawa.
Mutanen da suka shaidi bukin suna haɗa rawar da suke gudanarwa tare da kewaya
wutar da suka hura zuwa wayewar gari. Su kuma matan mamacin kowace takan ɗaura
farin saƙi ta yi ƙunshi da lalle a ƙafarta. Idan gari ya waye
kafin taron bukin ya watse, kowace daga cikinsu takan saki ɗan akuya
da kuma zakaran da suka zo da shi a cikin mazan da suke rawa. Su kuma za su yi
ta wawar su, kowa ya yagi abin da ya yaga, waɗanda suke
da ƙarfi ma
sukan iya ɗauke su
gaba ɗaya. An
nuna cewa, wasu matan sukan ɗauko zakaran da suka zo da shi su danƙa shi ga wanda suke so ya
aure su. Idan haka ta faru, nan take sukan tafi gidansa shi ke nan ta zama
matarsa. Wannan ya tabbatar da kimar mace a wurin Maguzawa. Ba don kimar da
mace take da shi ba, ba za su zo su kwana suna rawa, sannan a ƙare da wasoson zakara guda
ba. Domin zakara guda bai fi ƙarfin
arzikinsu ya yi ba.
Sakamakon Bincike
Wasu daga cikin sakamakon da wannan bincike ya
iya tsinkayowa sun haɗa da:
i.
Sanin kimar mace tare da
tabbatar da ita a aikace da Maguzawa sukan yi, ya taimaka ta fuskar ɗorewar tarbiyarsu da kyautatuwar zumunci da
tausaya wa junansu tare da haɗin kai a
tsakaninsu.
ii.
Bugu da ƙari, wannan nazari ya gano cewa, kimar da
mace take da ita a al’adun Maguzawa ita ce ta yi tasiri a ɗabi’un
wasu daga cikin Hausawan da suka karɓi addinin Musulunci.
iii.
Maguzawa mutane
ne da suka ɗauki mata
a matsayin iyaye, saboda haka al’adarsu ta ba su wata daraja ta musamman.
iv.
Al’adun
Maguzawa ba su tauye wa mata yanayin walwala ba. Sun ba su dama daidai da kimar
da al’ada ta ba su.
v.
Watsi da
wasu al’adun Maguzawa waɗanda suka ƙunshi kiyaye haƙƙoƙin ɗan’adam a
wannan lokaci, shi ya haifar da kallon da ake wa wasu Hausawa na rashin sanin
kimar mata a zamantakewarsu.
Kammalawa
Matsayin da mata suke da shi na kasancewarsu iyaye ga kowa, ba ƙaramar kima ya tabbatar musu ba a cikin al’umma. Wannan dalili ya sa matakan rayuwa na al’ada ba su wofintar da su sun zama koma baya ba. Takardar ta mayar da hankali wajen fito da kimar da mata suke da ita a ma’aunin al’adun Maguzawa na matakan rayuwa. Binciken ya samu nasarar leƙo wasu al’adu da suke tabbatar da darajar da mata suke da ita a wasu daga cikin al’adun Maguzawa na aure da haihuwa da kuma mutuwa. Duk da cewa, wasu Hausawan da suka karɓi addinin Musulunci suna bambanta kansu da Maguzawa, amma hakan bai hana su amfana da nagartattun ɗabi’unsu na darajanta ɗan’adam ba. Domin ko ba komai, tarsashin waɗanan ɗabi’u sun yi tasiri a rayuwar Hausawa ta yadda lamarinsu ya zama tamkar abin da masu magana suke cewa: “An tashi daga kan faƙo, an koma kan daɓe.”
Manazarta
1.
Abdullahi,
I.S.S. (2008). “Jiya Ba Yau Ba: Waiwaye a kan Al’adun Matakan Rayuwar Maguzawa
na Aure da Haihuwa da Mutuwa.” Kudin Digiri na Uku (Ph.D). Sakkwato: Sashen
Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo.
2.
Abdullahi,
I.S.S. (2012). “Zawarci da Auren Bazawara a Maguzance.” Cikin Amfani, A. H. da
Wasu (Editoci). Champion of Hausa Cikin
Hausa: A Festschrift in Honour of Ɗalhatu Muhammad, Pp. 473-479. Zaria: Ahmadu Bello
University Press.
3.
Abdullahi,
I.S.S. (2021). “Takabar Maguazawa.” Cikin Yakasai, S. A. da Wasu (Editoci). A Great Scholar & Linguist: A
Festschrift in Honour of Professor Ibrahim Ahmad Mukoshy, Pp. 740-748.
Kaduna: Amal Printing.
4.
Abraham,
R. C. (1977). Dictionary of the Hausa
Language. London: Hodder & Stoughton Educational Ltd.
5.
Bunza, A.
M. (2013). “Littafin Ruwan Bagaja a Ma’aunin Matakan Rayuwar Bahaushe.” Cikin
Bunza, A. M. da Noofal, M. A. (Editoci), Ruwan
Bagaja in Perspectives, Pp. 425-447. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
6.
Cibiyar
Nazarin Harsunan Nijeriya, (2006). Ƙamusun
Hausa na Jami’ar Bayero. Zaria: Ahmadu Bello
University Press.
7.
Garba,
Z. (2016). Nazari a kan Sababbin Sana’o’in Mata Hausawa a Garin Sakkwato.
Kundin Digiri na Biyu (M.A). Sakkwato: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Usmanu Danfodiyo.
8.
Ibrahim,
M. S. (1982). “Dangantakar Al’ada da Addini: Tasirin Musulunci Kan Rayuwar
Hausawa. Kundin Digiri na Biyu (M.A). Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Bayero.
9.
Ibrahim,
M. S. (1985). Auren Hausawa: Gargajiya da
Musulunci. Cyclostyled Education. Zaria: Hausa Publication Centre.
10. Ingawa, Z. S. (1984). Magungunan Hausa
Don Mata:Nazari kan Matan Hausawa da Ire-iren Buƙatunsu na Magunguna. Kundin Digiri na Ɗaya (B.A). Kano: Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Bayero.
11. Newman, P. & Newman, R. (2020). Hausa Dictionary: English-Hausa/Hausa-English. Kano:Bayero
University Press.
12. Nuhu, A. (2020). “Zamani Abokin Tafiya:
Wasu Al’adun Maguzawan Ƙasar
Katsina a Ƙarni na
21.” Kudin
Digiri na Uku (Ph.D) Sakkwato: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar
Usmanu Danfodiyo.
13. Nuhu, A. (2020). “Kyawawan Al’adu da Ɗabi’u a Matsayin Hanyar Samar da
Ingantacciyar Al’umma:
Waiwaye Daga Wasu Waƙoƙin Hausa na Zamani.” Cikin Bunza, M.U. da Wasu
(Editoci) Nigeria in Search of Stability:
The Relevence of History, Language, and Religious, Pp. 388-396. Kaduna:
Pyla-Mark Services Limited.
14. Rambo, R. A. (2007). “Nazari a kan Wasu
Keɓaɓɓun
Al’adun Auren Hausawa da na Dakarkari.” Kudin Digiri na Biyu (M.A). Sakkwato:
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo.
15. Rambo, R. A. (2021). “Falsafar Yaji da
Biko: Nazari a kan Zamantakewar Auren Hausawa da na Dakarkari.” Cikin Yakasai,
S. A. da Wasu (Editoci). A Great Scholar
& Linguist: A Festschrift in Honour of Professor Ibrahim Ahmad Mukoshy, Pp.
694-703. Kaduna: Amal Printing.
16. Safana, Y. B. (2001). “Maguzawan
Lezumawan Babban Kada Gundumar Safana (Jihar Katsina). Kundin Digiri na Ɗaya (B.A). Sakkwato: Sashen
Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu
Danfodiyo.
17. Sallau, I. A. (1981). “Taƙaitaccen Nazari Kan Maguzawa
da Al’adunsu.” Zariya: Kundin Digiri na Ɗaya (B.A). Sashen Koyar da
Harsuna da Al’adun
Afirka, Jami’ar Ahmadu
Bello.
18. Sani, S. M. (1988). “Kainafara Arnan Birchi.” Kundin
Digiri na Ɗaya
(B.A). Zariya: Sashen Koyar da Harsuna da Al’adun Afirka, Jami’ar Ahmadu Bello.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.