Wasu cikin Manazarta suka ce: ba su san wanda ya fara haramta Azumin Nafila a ranar Asabat ba kafin Shaikh Muhammad Nasiruddeen al-Albaniy. Shi Shaikh Albaniy ya dogara ne a kan Hadisin Abdullahi bn Busr (ra), daga ‘yar’uwarsa al-Samma’u (ra). Alhali Hadisi ne da manyan Malaman Hadisi suka illata shi.
- Imamu Zuhriy yana sukarsa.
- Imamu Malik ya ce: Hadisin karya ne.
- Yahya al-Qattan yana kaffa-kaffa da shi.
- Abu Dawud ya ce: an soke Hadisin (Mansukhi).
- Imamu al-Nasa’iy ya ce: Hadisi ne birkitacce.
- Ibnu Taimiyya ya ce: Hadisi ne “Shazzi”.
- Haka Ibnul Qayyim ma ya fada.
- Ibnu Hajar ma ya ce: Hadisi ne birkitacce.
To ka ga idan aka dauki maganar Malaman da suka
raunana Hadisin, to dole a jefar da shi. In kuma aka lura da maganar wadanda
suka kyautata Isnadinsa, to Hadisi ne “Shazzi”, ya saba wa Hadisai Mutawatirai.
Almajirin Imam Ahmad, Abubakar al-Athram ya ambaci
Hadisin sai ya ce
"فجاء هذا الحديث بما خالف الأحاديث كلها".
ناسخ الحديث ومنسوخه للأثرم (ص: 201)
“Sai wannan Hadisin ya zo da abin da ya saba wa dukkan Hadisai”.
Sai kuma ya ambaci Hadisan da ya saba musu, daga
ciki
- Hadisin Azumin watan al-Muharram gaba dayansa.
Alhali akwai ranakun Asabat fiye da daya a cikin watan.
- Haka Hadisin Azumtar watan Sha’aban.
- Hadisin Sittu Shawwal.
- Hadisin Ashura.
- Hadisin Arafah.
- Hadisin Azumi na tsakiyan kowane wata.
Duka wadannan Azumi dole ana samu suna dacewa da
ranar Asabat.
A takaice, Haramta Azumin Nafila a ranar Asabat ya
saba wa Ijma’i, kamar yadda Shaikhul Islam ya ce
"إن ظاهر الحديث خلاف الإجماع".
شرح العمدة لابن تيمية (2/ 653)
Saboda haka asali ra’ayoyi biyu ake da shi a
mas’alar; ra’ayin Jumhur na karhanta ware ranar Asabat ita kadai da yin Azumin
Nafila, in ba ranakun falala ba.
Da kuma ra’ayin su Imamu Malik da Ibnu Taimiyya na
halasci a sake ba kaidi.
Alhali a ka’ida; idan aka yi sabani zuwa ra’ayoyi
biyu a kan mas’ala, to bai kamata daga baya a kirkiri ra’ayi na uku ba.
Don haka babu abin da ya hana azumtar ranar Arafa
a ranar Asabat, ita kadai ba tare da an hada ta da wata rana ba.
Saboda haka kar ka yarda wani ya hana ka yin
Azumin ranar Arafah, idan ta zo a ranar Asabat, ra’ayin haramtawan ya saba
Ijma’i.
~
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
11 June, 2024
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.