𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Salamu alaikum, inna son sanin fassarar mafarki da kashe-kashensa?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam
warahmatullah.
Wato ƴar uwa sha'anin
mafarki abu ne babba wanda sai wanda suke da ilimin kawai, amman ga abin da na ɗan binciko cikinn ƙaramin ilimi da
fahimta da Allah ya hore min.
Mafarki na gaskiya yankine
na Annabta, kamar yadda akwai ruwayoyi da yawa daga Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya ce: “Mafarkin ƙwarai yanki arba'in
da shida ne na Annabci.” (Al-imamul Bukhari 6472; da Muslim, 4201). (Al-Bukhari,
3; da Muslim, 231). “Kuma wanda ya fi faɗin gaskiya shi ne ya
fiku gaskiyar mafarki. Waɗanda su kafi mafarki
na gaskiya su ne waɗanda suka fi,gaskiya
a magana.” (Muslim, 4200).
“Idan zamani (tashin
kiyama) ya kusanto, da wuya mafi yawan mafarkai basu zama na ƙarya ba. Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: “Hakan ze kasance ne
saboda Annabci, saboda haka masu imani za a basu wasu abubuwa a yana yin
mafarki wanda ze kusanto su ga labarai masu kyau ko taimakonsu akan su yi haƙuri da imaninsu.”
(Al-Bukhari, 6499; da Malam Muslim, 4200) Iri ɗaya za a iya cewa mu'ujizar da ta
bayyana bayan lokacin Sahabbai. Wannan be faru ba a lokacinsu saboda ba sa buƙatar su, saboda ƙarfin imaninsu, amma
mutanen da suka zo bayansu musamman a yanzu suna buƙatarsu saboda
imaninsu yana da rauni.
MAFARKI KALA UKU (3)
NE:
1. RAHMANI (Wanda
suke zuwa daga Allah),
2. NAFSAANI (psychological,
wato wanda suke daga mutum ne.)
3. SHAYTAANI (waɗanda suke zuwa daga
gurin sheɗan).
Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya ce: “Mafarki kala uku ne: mafarki daga Allah, mafarki da
yake haddasa wuya da wanda yake daga sheɗan, da kuma mafarki wanda yake zuwa daga abin
da mutum ya tuna bayan ya tashi, kuma ya ga (faruwarsa) lokacin da ya yi bacci.”
(Al- imamul Bukhari, 6499; da Muslim, 4200)
Mafarkin Annabawa
wahayi ne wanda an yi musu kariya daga sheɗan. Ummah sun yarda akan hakan. Annabi
Ibrahim ya shirya cika umarnin Allah na yanka ɗan sa Isma'il lokacin da ya ga hakan
cikin mafarkinsa; Allah ya ƙara musu Aminci duka.
Mafarkin sauran
mutane wanda ba Annabawa ba sai dai mu auna su akan hasken wahayi [Misali Ƙur'ani da Sunnah].
Idan mafarkin ya dace da Ƙur'ani da Sunnah, to hakan dama ya tabbata sai mu amsa;
idan kuma ya saɓa to ba za mu amsa ba
balle mu yi aiki da shi. Wannan fa al'amari ne mai tsanani, saboda da yawa ƙirkirarrun al'amura
da malaman sufaye da sauransu ta nan suke amfani su ce sun yi mafarkin abu
kaza.
Duk wanda yake son ya
yi mafarki na gaskiya to ya kasance zancensa gaskiya ne ko da yaushe, ya ci halal,
ya kiyaye haram, ya tsaya akan abin da shari'a ta umarce shi, da kaucewa abin
da Allah da Manzonsa (Sallallahu Alaihi Wasallam) suka haramta, da barci a yana
yin tsarki da fuskantar alƙibla, da tuna Allah har sai ido ya
rufe. Idan mutum ya yi wannan da abubuwa masu kyau to da wahala ne mafarkinsa
be zama gaskiya ba.
Mafarki mafi zama
gaskiya sune waɗanda ake ganinsu a
lokacin suhur, saboda a wannan lokacin ne Allah yake saukowa ƙasa (sakkowa da ta
dace da shi (SWA)) kuma ake saukar da rahama da gafara..... (Duba Madaarij
al-Saalikeen, 1/50-52)
Al-Imamul Haafiz ibn
Hajar ya ce: Gaba ɗaya mafarki ɗayan biyu ne (wato
kala 2 ne):
1. MAFARKIN GASKIYA.
Wannan sune mafarkin Annabawa da mutanen kirkir waɗanda suka bisu. Ze
iya kasance da sauran mutane ma, amman hakan yana da ɗan wuya, kamar irin
mafarkin kafirin sarki wanda Yusuf (AS) ya fassara masa shi. Mafarkan gaskiya
sune wanda suka zamo gaskiya a rayuwa bayan an ga faruwarsu a mafarki.
2. HARHAƊA MAFARKIN ƘARYA, wanda suke
gargaɗi akan wani abu.
Wannan suma kala kala ne:
1. Wasan sheɗan don ya wahalar da
mutum, kamar irin mutum ya ga an cire masa kai kuma yana tafiya kan yana binsa,
ko mutum ya faɗa cikin hargitsi kuma
be ga kowa ba da ze taimake shi, da sauransu.
2. Idan ya ga wasu
mala'iku suna gayamasa ya yi wani abu da aka haramta, ko yin wasu abubuwa da a
hankalce ba za su yiyu ba.
3. Ko mutum ya ga
wani abu da ya faru da shi a rayuwarsa ta gaskiya, ko yana so yafaru, kuma sai ya
ganshi a mafarki ya faru; ko ya ga wani abu da yake yawan faruwa da shi idan
yana farke. Irin wannan mafarkan mafi yawa suna magana ne akan abin da ze zo
gaba ko yake faruwa yanzu ko ya jima da faruwa. Duba: Fath al-Baari,
12/352-354.
Abu Sa’eed al-Khudri
(Allah ya ƙara masa yarda) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) ya ce: “Idan ɗayanku ya yi mafarki wanda yake so, to daga
Allah ne, sai ya godewa Allah ya bayar da bushara da sauran mutane. Idan kuma
ya ga abin da baya so, mafarki wanda baya so, to wannan daga sheɗan ne, sai ya nemi
tsarin Allah daga gare shi kuma kada ya faɗawa kowa, baze cutar daahi ba.” (Al-Bukhaari,
6584, da Muslim, 5862).
Abu Ƙutaadah ya ce: Manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Mafarki magaskaci (mai kyau) daga
Allah ne, amma sururu mafarki (mara kyau) daga sheɗan ne. Idan ɗayanku ya ga abin da
ba haka daga abin da ba shi so, to lallai abin sani daga sheɗan ne, to lallai ya
yi tofi gefen hagunsa sau uku, kuma ya nemi tsarin Allah daga sheɗan, kuma ba ta cutar da
shi da komai.” (Al-Bukhaari, 6594, da Muslim, 5862 suka ruwaito). “tofin” yana
nufin yawu kaɗan, ko kuma iska ba
tare da tofa yawun ba.
An karɓo daga Jabir (Allah
ya ƙara
masa yarda) cewa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Idan
ɗayanku ya ga mafarkin
da ba shi ya so ba, to ya yi tofi a gefen hagunsa sau uku, kuma ya nemi tsarin
Allah daga sheɗan sau uku, kuma ya
canza gurin kwanciyarsa daga inda yake kwance zuwa ɗayan bangaren.” (Imamu
Muslim, ya ruwaito, 5864)
Ibn Hajar ya ce: a haɗa abubuwan da aka ce
game da mafarkai masu kyau, zamu iya cewa:
1. Mutum ya yabi
Allah dangane da mafarki mai kyau.
2. ya yi farin ciki da
shi.
3. Ya gayawa mutane
waɗanda yake so ba waɗanda baya so ba.
Idan kuma zamu haɗa abubuwan da aka ce
dangane da mafarki mara kyau zamu iya faɗin abubuwa 4:
1. Ya nemi tsarin
Allah daga sharrin mafarkin.
2. Ya nemi tsarin
Allah daga sharrin sheɗan.
3. ya yi tofi sau uku
a gefen hagunsa idan ya farka.
4. Kada ya bawa kowa
labari.
5. A cikin Bukhari,
Baab al-Ƙayd fi’l-Manaam, an ambaci abu na biyar daga Abu
Hurairah, wanda shi ne yin salla. Yadda ruwayar take shi ne: duk wanda ya ga wani
abu da ba ya so (a mafarki) kada ya faɗawa kowa, sai dai ya tashi ya yi salla.
Wannan ruwayar Mausul ce Imam Muslim y a ruwaito ta a sahih dinsa.
6. Muslim ya ƙara da abu na shida,
wanda shi ne canza asalin yadda kwanciyar take zuwa ɗayan ɓangaren.
A ƙarshe, abubuwa shida
ne za ayi, huɗun da muka ambata da
kuma yin salla raka'a 2 nafila, da canza bangaren kwanciya. Duba Fath al-Baari,
12/370.
A cewar hadisi da
ruwayar Abu Razeen daga Al-Tirmidhi, kada ya gayawa kowa sai dai wanda yake
kusa da shi sosai yake son sa sosai kuma yake kula da shi, ko wanda yake da
hikimah sosai. A cewar wata ruwayar, kada ya faɗawa kowa sai wanda yake da hikimah ko
yake ji da shi. A cewar wata ruwayar kuma, kada ya faɗawa kowa game da
mafarkinsa sai dai wani malami ko wanda ze bashi shawara mai kyau tsakani da
Allah.
Al-Ƙaadi Abu Bakr ibn
al-‘Arabi ya ce: game da malami, ze fassara masa shi ta hanya mai kyau iya
kokarinsa, kuma wanda ze bashi shawara ta gaskiya ze koya masa wani abu da zeyi
masa amfani ko ya taimake shi. Wanda yake da hikima kuma shi ne wanda yasan
yadda ze fassara masa kuma ya gayamasa iya abin da ze taimake shi, ko kuma ya
yi shiru. Wanda yake ji da shi ko yake son sa, idan ya san wani abu mai kyau ze
faɗa, idan kuma be sani
ba ko yana kokonto to ze yi shiru. Duba Fath al-Baari, 12/369
Imamul Baghawi ya ce:
Ka sani cewa fassarar mafarki yana shiga ɓangarori daban daban. Mafarki za a iya
fassara shi da hasken Ƙur'ani ko hasken Sunnah, ko ta hanyar karin magana da
mutane ke amfani da shi, ko ta hanyar sunaye. (Sharh al-Sunnah, 12/220)
Ya ba da misalai akan
hakan, kamar: Fassara da hasken Ƙur'ani: igiya da
ma'anar dace, sabida faɗin Allah:
وَاعْتَصِمُوا بِحَبْلِ اللَّهِ جَمِيعًا وَلَا تَفَرَّقُوا
“Kuma ku yi daidami
da igiyar Allah gaba ɗaya, kuma kada ku
rarraba.....” [Aal ‘Imraan 3:103].
Fassarar a haskem
sunnah: kamar hankaka wakiltar haramtaccen mutum (fasiƙi), saboda Manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ambace shi da hakan.
Fassara ta hanyar
karin magana: kamar haƙa rami ma'ana makirci, saboda mutane suna cewa: “Idan
za ka haƙa rami to haƙa daidai kai”
Game da littafin
“Fassarar Mafarkai” cewa an danganashi ga Ibn Seereen, bincike masu yawa sun
nuna cewa za a yi dangana shi gare shi gaba ɗaya.
ALLAH NE MAFI SANI.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.