30 ga watan Oktoba na shekarar 1945 aka haife ta a wata unguwa da ake kira Takardawa dake cikin Birnin Sakkwato, Arewa Maso yammacin Nijeriya.
Tayi karatun Addinin Musulunci a hannun Malamai daban - daban a cikin Sakkwato ciki kuwa har da Malam Maigandi dake Gidadawa. A Kaduna kuwa tayi karatu a hannun Malam Bagudu.
Ta halarci
Makarantar Elimentare ta Magajin Rafi dake
Sakkwato domin samun ilimin zamani kafin daga bisani tayi aure.
Allah ya
albarkaci auren nata da 'ya'ya /diya 8, 3 Maza, 5 Mata.
Abdulkadir
da Hassan da Husaini sune 'ya'yanta
/diyanta maza, Asma'u da Hadiza da Maryam da Safiya da Aisha kuma sune
'ya'yanta /diyanta mata.
Su 3
Mahaifiyarsu ta haifa dukansu kuwa Mata ne, ita ce ta biyu duk da yake akwai
namiji tsakanin ta da wadda take bima wanda tun a matakin jarinta ne ya rasu.
Gaba da baya
yar sarauta ce ( ta wurin mahaifi da mahaifiya)
ta auri Basarake, ta kuma haifi
Basarake.
Ya'yanta
/diyanta mata daya ta auri Sarki, 3 suka auri 'ya'yan Sarakuna d'aya kuma ta
auri d'an wani shahararren Malamin Addinin Musulunci /Babban Alkali.
Marigayiya Hajiya Aishatu Marafa Ahmadu Danbaba (1945-2021).
Wannan
baiwar Allah ita ce Marigayiya Hajiya Aisha/Aishatu yar Sir Ahmadu Bello GCON
KBE Sardaunan Sakkwato Firimiyan Jihar Arewa na farko kuma na karshe dan Sarkin
Rabah Malam Ibrahimu dan Sarkin Musulmi Abubakar II /Mai Rabah dan Sarkin
Musulmi Muhammadu Bello dan Mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo Tagammadahullah
Birahamatihi.
Ita ce 'ya
/d'iya ta biyu daga cikin 'ya'ya /d'iya uku wadanda Marigayiya Hajiya
Amina/Gwaggon Kano yar Sarkin Bichi Abubakar dan Sarkin Bichi Mustapha ta
haifawa Sardaunan Sakkwato Sir Ahmadu Bello, sauran sune Marigayiya Hajiya
Fatima /Inno da Hajiya Lubabatu/Luba wadda ke raye a halin yanzu.
Makada Musa
Dankwairo Maradun a faifansa mai amshi "Ya wuce reni ba ayi mai shi, Amadu
jikan Garba sadauki" da ya yiwa Mahaifinsu (Sardaunan Sakkwato Sir Ahmadu
Bello) ya na ambatarta a ciki ya na cewa "Mai girma d'an Mai girma Uban
Luba baban A'i da Inno".
Mijinta
shine Marigayi Mai girma Sanata Alh. Ahmadu Danbaba Marafan Sakkwato dan
Magajin Garin Sakkwato Usman dan Magajin Garin Sakkwato Abdu wanda kuma jika ne
ga Magajin Garin Sakkwato na farko Malam Abubakar Haruna Dan Jada Ba'allibe.
D'anta
Marigayi Alhaji Hassan Ahmadu Danbaba yana rike da sarautar Magajin Garin
Sakkwato ne Allah SWT ya yi masa wafati.
'Yarta/D'iyarta
Hajiya Asma'u (Ammi) ita ce matar Marigayi Mai girma Sarkin Sudan na Wurno
Alhaji Shehu Malami, Hajiya Hadiza ce matar Alh. Umaru Shehu Goronyo Tsohon
Shugaban Majalisar Dokoki a Tsohuwar Jihar Sakkwato (Sokoto da Zamfara a yau)
kuma tsatso daga zuriyar Sarkin Musulmi Aliyu Babba dan Sarkin Musulmi
Muhammadu Bello dan Mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo, Hajiya Maryam tana
auren Alhaji Bashir Huseini Adamu jikan
Malam Ibrahim Dan Tunku wadda Mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo ya baiwa Tutar
Jihadin Jaddada Addinin Musulunci a Kazaure ta Jihar Jigawa ta yau.
Yarta/D'iyarta
Marigayiya Hajiya Safiya ta auri Alhaji Alhassan dan Malam/Alkali Mutasibbi
Sakkwato yayinda Hajiya Aisha ke auren Farfesa Isah Muhammad Maishanu,
Kwamishinan ilimi mai zurfi na Jihar Sakkwato daga tsatson zuriyar Sarkin Kabin
Yabo Muhammadu Moyijo daya daga cikin manyan mataimakan Mujaddadi Shehu Usman
Danfodiyo dake da Tutar yakin jaddada Addinin Musulunci a Daular Usmaniyyah.
Hajiya
Aishatu Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato, Matar Marigayi Alhaji Ahmadu
Danbaba Marafan Sakkwato, Mahaifiyar Magajin Garin Sakkwato Alhaji Hassan
Danbaba ta rasu a shekarar 2021, Allah SWT ya jaddada mata rahama ita da dukan
Magabatanmu ya sa mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani, amin.
Ibrahim
Muhammad Danmadamin Birnin Magaji, Jihar Zamfara, Nijeriya.
Jumu'a,
10/07 /2025.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.