Ticker

6/recent/ticker-posts

Tarihin Ginuwar Wasu Al’amuran Siyasar Jam’iyyu a Cikin Rubutun Zuben Hausa Daga 1950-2023 (Babi Na Hudu)

Yusuf, J. (2025). Tarihin Ganuwar Wasu Al'amuran Siyasar Jam'iyyu a Cikin Rubutun Zuben Hausa Daga 1950-2023 (Ph.D. Thesis) Department of Nigerian Languages, Usmanu Danfodiyo, Sokoto.

Tarihin Ginuwar Wasu Al’amuran Siyasar Jam’iyyu a Cikin Rubutun Zuben Hausa Daga 1950-2023

TARIHIN GINUWAR WASU AL’AMURAN SIYASAR JAM’IYYU A CIKIN RUBUTUN ZUBEN HAUSA DAGA 1950-2023

Na

Jibril Yusuf
Email: yusuf.jibril@kasu.edu.ng
Phone: +2347030399995

*** ***

BABI NA HUƊU

SIYASA A RUBUTACCEN ADABIN HAUSA

4.0 Shimfiɗa

A wannan babin an kawo bayanai da suka shafi siyasa da ma’anonin da masana da manazarta suka ba ta, sannan aka dubi wasu na’u’o’inta a taƙaice. Haka kuma an kawo bayanai kan waɗansu daga cikin dalilan da ake ganin sun haifar da ƙamfar rubutaccen adabin siyasa waɗanda wannan bincike ya mayar da hankali a kansu. Daga nan an kawo bayanai kan irin dangantakar da take tsakanin siyasar addini da siyasar jam’iyya, wanda shi ne ya ba da damar gane irin yadda addini da aƙidu suka yi tasiri a fagen siyasar jam’iyyu a Arewacin Nijeriya. Haka kuma an kawo bayani kan matsayin mata a cikin siyasa da yadda ake takura wa abokan hamayya da kuma amfani da yarfe a cikin siyasar jam’iyyu.

4.1 Ma’anar Siyasa

A ma’ana ta lugga an bayyana kalmar siyasa da mabambantan ma’anoni kamar haka: Ƙamusun Dar-Elmashreƙ a cikin Idris, (2016:49) an bayyana kalmar da cewa, Balarabiyar kalma ce wadda asalinta daga kalmar “saasa” ne, amma saboda ƙa’idar tasarifi na nahawun Larabci sai kalmar ta koma “siyaasa”, wadda take nufin juyawa a kan wani lamari ko kuma yarda da wani ko jiɓintar al’amarin al’umma tare da saninsu ko ba tare da saninsu ba.

Ƙamusun Ingilishi na Merriam-Webster (2024) ya bayyana siyasa da cewa:

the art or science concerned with guiding or influencing governmental policy or the art or science concerned with winning and holding control over a government, especially, competition between competing interest groups or individuals for power and leadership (as in a government).”

Fassara;

“hanya ko fasaha ce ko kimiyya da ta shafi karkato ra’ayin al’umma domin samun shugabanci da juya akalar gwamnati; hanya ce ta fafutukar neman samun ƙarfin faɗa a ji, wadda kan gudana tsakanin ɓangarori biyu, domin samun shugabanci.”

A cikin Ƙamusun CNHN, (2006:397) an kawo ma’anoni huɗu da suke bayyana siyasa kamar haka:

-Tafiyar da al’amuran jama’a ta hanyar neman ra’ayinsu da shawarwari da su.

-Rangwame, musamman a ciniki.

-Dabara ko wayo.

-Iya hulɗa da jama’a.

Ƙamusun nan na Ingilishi mai suna Oxford Advanced Learner Dictionary ya bayyana siyasa da cewa:

the activities involved in getting and using power in public life, and being able to influence decisions that affect a country or a society.”

Fassarar Marubuci:

harkoki ne da suka shafi neman samun ƙarfin iko a cikin al’umma da kuma samun tasiri wajen yanke shawara wadda ta shafi ƙasa ko al’umma.

Shi kuwa Ƙamusun Almunjid Wasiɗ a cikin Idris, (2016:47) ya bai wa siyasa ma’anoni guda biyu. Ma’ana ta farko ya bayyana siyasa da cewa ingantar da al’umma da shiryar da su zuwa ga tafarkin tsira. Ma’ana ta biyu kuwa cewa ya yi, siyasa na nufin gudanar da fannin mulki da ayyukan ƙasa a cikin ƙasar ko a wajenta, inda ta haka ne ake samun siyasar cikin gida da ta ƙasashen waje.

Ta fuskar ma’ana ta ilimi kuwa, masana da dama sun bayyana fahimtarsu dangane da ma’anar siyasa, inda suka dubi kalmar ta fuskoki mabambanta. Daga cikin su akwai:

A ra’ayin Mashi, (1986:16) ya bayyana siyasa ne ta fuskoki uku: Hanya ta farko ya bayyana ta da ma’anar salo. Sauran hanyoyin kuwa wato ta biyu da ta uku, ya bayyana siyasa da cewa sulhu ko sauƙi. Waɗannan ma’anoni da ya bai wa siyasa ba za su rasa nasaba da yadda siyasa ta kasance hanyar lallashi ko lallaɓa mutane domin neman goyon bayansu ba. Haka kuma ya kalli siyasa a matsayin yaudara ko ƙarya, saboda yadda ‘yan siyasa kan tsara wani lamari na yaudara domin neman biyan buƙata. Don haka ne ma wasu suke yi wa siyasa kallon cin amana da ƙarya da yaudara da butulci, har ya sa ma ake ganin duk wanda bai cika waɗannan abubuwa ba, to bai ma cika ɗan siyasa ba.

 Mashi, (1986:17) ya ci gaba da cewa za a iya kallon siyasa a matsayi guda biyu, wato za a iya samun siyasar jam’iyyu da kuma siyasar duniya baki ɗaya. Siyasar jam’iyyu ta shafi wata ƙungiya ta siyasa wadda take neman mulkin al’umma. Ita kuwa siyasar duniya ta shafi ra’ayoyin al’umma waɗanda kan kasance ba ƙasa ɗaya ko al’umma guda ya shafa ba. Misali; bambancin launin fata da fafutukar neman ‘yanci da siyasar addini da sauransu.

A ra’ayin Funtua, (2003:19-20) ya nuna siyasa da cewa, ararriyar kalma ce ta Larabci wadda take nufin sauƙi ko rangwame ko jin ƙai. A da, da zarar an ce wa mutum ɗan siyasa to ana nufin mutum mai jin ƙai, kuma mai rangawame, wato dai mutum mai jin tausayin al’umma. Ya ƙara da cewa, za a iya bayyana siyasa a matsayin hanyar sanin tafiyar da jama’a ce, kuma nasiha ce, kuma gargaɗi ce. Wannan ne ma ya sa masana adabin Larabci suke cewa siyasa na nufin tafiyar da mulki cikin adalci. Ya kuma bayyana cewa a wurin Balarabe inda wannan kalma ta samo asali, idan aka ce mutum ɗan siyasa ne, to ana nufin mai tafiyar da mulkin jama’a, mai hikima, sannan wanda yakan zauna ya yi shawara da jama’a bisa lura. Duk wanda ya kasance da waɗannan abubuwa to ya zama ɗan siyasa ke nan.

Shi kuwa Idris, (2016:49) ya bayyana siyasa da cewa hanya ce ta tafiyar da mulkin jama’a a zamanance ko a gargajiyance, ko kuma dabara ce ta jawo hankalin mutane ta hanyar karkata ta inda suka sa gaba a kowane fage. Misali idan ɗan siyasa ya lura da abin da mutane suka fi so, to shi ma sai ya karkata ta can ko da kuwa da gaske har cikin zuciyarsa ba yana nufin hakan ne ba. Idris, (2016:49) ya ƙara da cewa, idan aka yi la’akari da waɗannan halaye na ‘yan siyasa za a iya cewa, duk wanda ya iya shan kan mutane, da lallaɓa su da iya jan ra’ayinsu ko da kuwa ta hanyar yaudara ce za a iya cewa ya iya siyasa.

A taƙaice dai, idan aka dubi waɗannan ma’anoni da aka bai wa siyasa za a ga cewa yawanci ma’anonin sun yi tarayya wajen amfani da waɗansu muhimman lamura, kamar su; tausasawa da jin ƙai da jan hankali da rangwame da mulki da ƙarya da yaudara da wayo da sauransu.

Ke nan, a fahimtar wannan bincike, siyasa tana nufin neman ra’ayin jama’a ta hanyar amfani da lafuzza masu daɗi da suka ƙunshi tausasawa da nuna jin ƙai da rangwame da ƙarya, domin samun biyan wata buƙata wadda takan iya kasancewa na neman shugabancin al’umma ko cimma wani buri na rayuwa.

Kodayake, a yau al’umma sun fi kallon siyasa a matsayin wayo ko zance mai daɗi ko lallashi ko ƙarya ko danne haƙƙi ko yaudara. Funtua, (2003:18). Wannan kuwa ba zai rasa nasaba da irin salon da shugabanni suka ɗauka wajen gudanar da shugabancin al’umma a yau ba.

4.2 Samuwar Siyasar Zamani ga Hausawa

Kalmar zamani suna namiji tilo, jam’inta shi ne zamunna ko zamanai. Kalmar tana nufin yayi ko lokaci; a ma’ana ta biyu kuma an bayyana kalmar da cewa, lokacin da ake ciki ko mai ci (CNHN, 2006: 489). Dangane da wannan aiki kuwa kalmar zamani tana nufin lokacin da al’ummar ƙasar Hausa suka samu cuɗanya da baƙin al’umma wanda ake danganta wannan cuɗanyar da samuwar rubutu wanda ya haifar samuwar ilimin addinin Musulunci da kuma hanyar rubutun zamani.

Idan aka dubi zamani ta wannan fuskar za a iya cewa zamani shi ne, duk wata rayuwa da aka yi ta bayan rayuwar gargajiya kafin cuɗanyar Hausawa da baƙi. Ke nan, idan aka yi batun siyasar zamani kuma za a iya bayyana shi da cewa, siyasar da ta samu bayan zuwan baƙi ƙasar Hausa, wanda ta yi nuni da hanyoyin gudanar da shugabanci da jagorancin al’umma bisa wani daidaitaccen tsarin addini ko kuma tsarin Turawa.

4.2.1 Siyasar Addini

Idan aka yi batun siyasar addini a ƙasar Hausa kai tsaye siyasar Musulunci ce za ta fara zuwa a rai. Wannan ba zai rasa nasaba da yadda addinin Musulunci ya shigo ƙasar Hausa kuma ya sauya rayuwar Hausawa ta fuskoki da dama ba. Siyasar Musulunci ta samu ne bayan cuɗanyar da aka samu tsakanin Hausawa da Larabawa a wuraren ƙarni na goma sha biyar. Yahaya, (1988:10) da Idris (2016:37) sun bayyana cewa, Larabawa sun zo sun tarar da Hausawa da tsarin siyasarsu ta gargajiya sai dai bayan Hausawan sun karɓi Musulunci sai suka koma bin tsarin na Musulunci wajen gudanar da mulki da shugabanci. An faɗa cewa, wani malami mai suna Abdulkarim Almagili ya taso daga ƙasar Maroko, ya iso ƙasar Katsina zamanin sarkin Katsina Ibrahim Maje a ƙarni na sha biyar, wuraren shekarar 1494. Duk da cewa ko da ya iso ya tarar da malamai da masallatai a Katsina, amma dai kafin ya tafi sai da ya kafa makarantar koyon addinin Musulunci da ilimin shari’a da yadda za a gudanar da ita. Daga nan sai ya zarce Kano, inda ya tarar da Muhammadu Rumfa kan mulki. Sarki ya roƙe shi kan ya rubuta masa littafi da zai zamo masa jagora wajen gudanar da mulki da shari’a bisa tafarkin Musulunci, sakamakon hakan ne Almagili ya rubuta masa wani littafi mai suna Taj Al-Din Fi Ma Yajibu Alal Mulk. (Idris, 2016: 37).

Hiskett, (1975:12) yana ganin cewa Musulunci ya shigo ƙasar Hausa ne tun a wuraren ƙarni na goma sha huɗu. Hujjarsa ita ce, samun sunayen da suke da alaƙa da Musulunci a cikin jerin sunayen sarakunan da suka yi mulki a yankunan ƙasar Hausa a wannan ƙarnin. Musulunci bai yi ƙarfi sosai a wancan lokacin ba, sai bayan da aka samu zuwan wasu malamai Larabawa daga yankin Afrika ta Arewa a ƙarni na sha shida, wuraren shekarun 1504, cikinsu ne aka samu fitaccen malamin addinin Musluncin nan wato Muhammad Bin Abdulkarim Al-Maghili wanda ya koyar da fannonin ilimin Musulunci da dama a garuruwan Katsina da Kano.

Musulunci ya ci gaba da yaɗuwa a yankunan ƙasar Hausa, sai dai bayan wasu shekaru, an fara samun sauyin halaye da ɗabi’u na al’ummar Musulmi a wancan lokaci, inda suka riƙa cakuɗa abubuwa na addinin Musulunci da gargajiya da tsafi da sauran wasu abubuwan da Musulunci bai yarda da su ba. Wannan ne ya sa a farkon ƙarni na sha tara aka samu waɗanda suka gudanar da jihadin gyaran halaye, waɗanda mafi yawansu Fulani ne ƙarƙashin jagorancin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo. Da farko sun fara ne da wa’azi, daga bisani kuma waɗanda suka ƙi jin wa’azin aka yi amfani da makami domin gudanar da jihadi, wanda zuwa shekarar 1812 duk sai da ya kasance an cinye masarautun Haɓe, aka kuma maye gurbinsu da masarautun Musulunci waɗanda ake kira daular Usmaniyya wadda take da cibiyarta a Sakkwato(Hiskett, 1975:13).

Bayan jihadin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo da ɗan’uwansa Abdullahi Fodiyo, an ci gaba da gudanar da tsarin shugabanci bisa turbar Musulunci, inda a lokacin har Abdullahi Fodiyo ya rubuta wata waƙa mai taken “Tsarin Mulki na Musulunci” wanda a ciki ya yi bayanin yadda tsarin mulki na Musulunci yake da yadda ya kamata shugaba da mabiyansa su kasance, da waƙar “Murnar Cin Birnin Alƙalawa”. Shi kuma Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ya rubuta waƙar “Wallahi-Wallahi” waɗanda duk sun ƙunshi siyasar Musulunci ne.

Bayan kusan ƙarni guda da kafuwar tsarin mulki na addinin Musulunci a ƙasar Hausa, sai Turawa suka shigo da nasu tsarin mulki da addini da kasuwanci irin na ƙasashensu. Wannan shigowar tasu ita ce ta kawo tarnaƙi ga ɗorewar tsarin mulki irin na Musulunci a hukumance a ƙasar Hausa.

4.2.2 Siyasar Jam’iyya

Kalmar Jam’iyya tana nufin ƙungiyar jama’a ta siyasa ko ta sana’a ko ta wasu harkoki na rayuwa, wadda take da manufa guda, da tsarin ƙa’idoji da zaɓaɓɓun shugabanni. (CNHN, 2006: 212).

Paul da Roxana (2020: 114) sun bayyana jam’iyya da cewa ƙungiyar siyasa, ko rukunin jama’a, ko sauran ƙungiyoyi.

Yusuf (2018: 26) ya bayyana ma’anar jam’iyya da cewa haɗuwar jama’a ne a matsayin ƙungiya, ko dai ta siyasa ko ta sana’a ko ta wasu harkokin rayuwa, waɗanda suke da manufofi da ƙa’idojin da suke tafiyar da su.

A taƙaice za a iya ba da ma’anar jam’iyya da cewa rukunin jama’a ne da suke da manufa iri guda waɗanda suke gudanar da harkokinsu a bisa wasu ƙa’idoji da sharuɗɗa da suka sanya wa kansu domin tafiyar da ƙungiya domin neman shugabanci ko wasu harkoki na rayuwa.

Ke nan, siyasar jam’iyya tana nufin neman ra’ayin jama’a ƙarƙashin wata ƙungiya guda, ta hanyar jan hankali da lafuzza masu daɗi, ta hanyar tausasawa da nuna tausayi da jin ƙai, domin cimma wata biyan buƙata, musamman na neman shugabanci ko jagorancin al’umma.

Idan aka yi batun siyasar jam’iyya, to za a iya alaƙanta shi da cuɗanyar da aka samu tsakanin Turawa da al’ummar ƙasar Hausa. Turawan da suka shigo ƙasar nan sun kasu zuwa gida biyar. Rukunin farko su ne ‘yan leƙen asiri, na biyu su ne ‘yan kasuwa, waɗanda suka shigo domin hada-hadar cinikin bayi da sauran wasu kayayyaki na ƙasar Hausa. Na uku kuwa su ne, waɗanda suka zo da niyyar yawon buɗe ido domin fahimtar yadda ƙasar Hausa da al’ummar Hausawa suke. Ayari na huɗu sun kasance ayarin ‘yan Mishan ne, waɗanda suka zo da niyyar ya ɗa addinin Kirista da ilimin boko, sai kuma rukuni na biyar, su ne ‘yan mulkin mallaka, waɗanda suka zo domin shimfiɗa sabon salon mulki irin na ƙasar Ingila a ƙasar (Yusuf, 2012: 25) da (Bunza, 2015: 11-12) da (Yusuf, 2018: 16).

Dudley, (1968:77) ya ce, wuraren shekarar 1903 Turawa sun mamaye ƙasar Hausa, inda suka musanya daular Usmaniyya ta zama ƙarƙashin ikonsu, domin shimfiɗa mulkin mallaka. Kasancewar sun sami yankin na ƙasar Hausa yana da tsarin shugabanci na sarakuna, sai suka yi amfani da sarakunan wajen shimfiɗa tsarin nan na mulkin ‘angulu da kan zabo’ ta hanyar amfani da sarakuna wajen gudanar da mulkin mallaka.

Sarakunan da suka nuna tirjiya kuwa, wasu an kashe su, wasu kuwa an cire su daga kan mulki aka maye gurbinsu da waɗanda Turawan suke so. Misali; Sarkin Musulmi Attahiru Ahmadu na ɗaya, wanda Turawan suka kashe, da Sarkin Haɗejia Muhammadu Mai-Shahada, wanda shi ma kashe shi suka yi, da kuma Sarkin Kano Alu wanda aka cire shi daga kan mulki. A Zazzau an sauke Sarki Kwasau aka naɗa Aliyu Ɗan Sidi, a Gwandu kuma aka cire Sarkin Gwandu Muhammadu Aliyu, aka maye gurbinsa da Sarkin Kalgo Halliru (Birniwa, 1987:14)

Duk da cewa tsarin sarautar gargajiya ya ci gaba, amma sai ya kasance duk wani umarni ko hani yana zuwa ne daga wajen Turawan mulkin mallaka ƙarƙashin tsarin En’e-En’e. Wannan tsarin ne ya ci gaba har zuwa lokacin da hada-hadar karɓar ‘yancin kai ya kankama a wuraren shekarun 1959. Kafin wannan lokaci an yi ta hanƙoron karɓar mulkin kai, amma sai ‘yan Arewa na wancan lokaci suka ga cewa, ba su da isassun masu ilimin zamanin da za su iya tsayawa a madadinsu. Bayan shigowar Turawan mulkin mallaka a wuraren shekarar 1903, sun kafa makarantar boko a 1905 a Sakkwato, wadda ba ta yi nasara ba, sai aka sake buɗe wata a 1909 a Kano (Yahaya, 1988:90). Wannan makarantar elementare ce, ba a kuma samu kafa makarantar sakandare a lardin Arewa ba sai a shekarar 1922, inda aka kafa Kwalejin Katsina, bayan kuwa a ɗaya ɓangaren mutanen Kudu sun yi nisa kan sha’anin ilimin boko(Dudley, 1968:72). Wannan ya sa ‘yan Arewa suke ganin cewa za su zama saniyar ware, don za a yi siyasar wannan lokaci ba da su ba ke nan. Haka kuma, su ‘yan kudu suna so a rungumi tsarin ‘jamhuriya’ wanda a ganin ‘yan Arewa, kasancewarsu Musulmi ya saɓa wa koyarwar addinin Musulunci. Waɗannan dalilai su ne suka sa ‘yan Arewa suka dage cewa maimakon tsarin jamhuriya da ‘yan Kudu suke muradi, ya kamata a rungumi tsarin ‘Mulukiya’ ne, domin a ci gaba da tsarin mulki ƙarƙashin sarakuna. Wannan zai ba da dama su ma a dama da su cikin harkokin mulki maimakon su zama ‘yan kallo. (Birniwa, 1987:17-23).

Cikin shekarar 1934 ne ƙungiyoyin suka fara zama da gindinsu a Kudancin Nijeriya, amma a yankin Arewa ko labarin ba a ji. Daga bisani wasu ‘yan Arewa masu kishi da son ganin ci gaban yankin suka yunƙura, domin kakkafa irin waɗannan ƙungiyoyi. Wannan kuwa ya faru ne kasancewa zaman da suka yi da ‘yan Kudu, sai suka koyi yadda ake mulki irin na siyasa. Mutane irin su Malam Sa’adu Zungur wanda ya riƙe muƙamin sakatare a jam’iyyar NCNC wadda reshe ne na siyasar Kudu a Arewa tare da goyon bayan su Azikwe, da Malam Aminu Kano da wasu da dama sun yunƙura domin kafa irin waɗannan ƙungiyoyi (Idris, 2016: 50-51).

Birniwa, (1987:27-28) ya bayyana cewa tun a wuraren shekarun 1930-1940 ne aka fara jin ƙamshin samuwar ƙungiyoyin siyasa a Arewacin Nijeriya. An samu ɓullar ƙungiyoyi da dama duk da cewa ba su fito fili ƙarara a karon farko sun kira kansu da jam’iyyun siyasa ba, amma dai sun samar da cibiyoyin da sukan riƙa haɗuwa lokaci-lokaci domin tattauna al’amuran siyasa.

A ra’ayin Dudley, (1968: 78) yana ganin cewa an fara samun ɓullar ƙungiyoyi ne a tsakankanin shekarar 1943-1944. Ƙungiyoyin da aka samar wannan lokacin sun haɗa da; Ƙungiyar Inganta Rayuwar Mutanen Bauchi (BGIU) wadda Sa’adu Zungur ya kafa a 1943, da Ƙungiyar Tattaunawa ta Mutanen Bauchi (BDC) a 1944, da Ƙungiyar Zumunta ta Sakkwato (YSC) a 1945, da Ƙungiyar Matasa ta Kano (KYA) a 1948 da Ƙungiyar Matasan Zariya (ZYA) ita ma a 1948 da sauransu.

An faɗa cewa, lokacin da sarkin Bauchi ya fahimci cewa wannan ƙungiyar ta Bauchi akwai alamun siyasa a cikinta, sai ya sa aka rufe ƙungiyar tare da dakatar da duk wasu harkokin ƙungiyar(Birniwa, 1987:28).

Kamar yadda aka gani, kakkafuwar ƙungiyoyi ne ya haifar da samuwar jam’iyyar siyasa ta farko wato NCNC a shekarar 1944, wadda aka samu ‘yan Arewa da suka riƙe muƙamai a cikin wannan jam’iyyar kamar su Malam Sa’adu Zungur da Sa’ad Abubakar Zukogi da Habib Raji Abdallah da sauransu, domin a faɗaɗa jam’iyyar ta zama ta ƙasa baki ɗaya, ba ta ‘yan Kudu kaɗai ba. Wannan ya ba wa ‘yan Arewa damar koyon yadda ake siyasa daga Kudu, ta yadda suka zo suka kafa ƙungiyoyin da suka zama silar kafuwar jam’iyyun siyasa a Arewa.

Daga cikin misalan waɗannan ƙungiyoyi da aka kakkafa a Arewa, akwai Ƙungiyar Inganta Rayuwar Mutanen Bauchi (BGIU) da Ƙungiyar Tattaunawa ta Mutanen Bauchi (BDC) da Ƙungiyar Zumunta ta Sakkwato (SYC) da Ƙungiyar Matasa ta Kano (KYC) da Ƙungiyar Abokai ta Kano (FAK) akwai Ƙungiyar Malamai ta Arewa (NTA) da Ƙungiyar Matasan Zariya (ZYA). Waɗannan ƙungiyoyi da ma wasu duk an kafa su ne a tsakankanin 1943 ne zuwa 1948, waɗanda su ne ake ganin suka narke suka zama jam’iyyar NPC a shekarar 1951, daga baya kuma wasu suka ɓalle suka kafa jam’iyyar NEPU. (Dudley, 1968: 78-79) da (Idris, 2016:51).

Daga bisani, Ƙungiyar Matasan Zariya (ZYA) ta kira sauran ƙungiyoyi domin tattauna yadda za su haɗa kai su samar da wata ƙungiya wadda za ta haɗe lardin Arewa baki ɗaya, amma wannan yunƙuri bai ci nasara ba, kasancewar wani kwaskwarima da Sir John MacPherson ya yi alƙawarin yi wa kundin tsarin mulki, wanda daga baya ya ba da umarnin faɗaɗa harkar ƙungiyoyi. Wannan dama ce ta sa a watan Satumbar 1948 aka kira taro domin tattauna irin sauye-sauyen da aka samu a cikin tsarin siyasar Nijeriya. Wannan taron shi ne ya haifar da kafa ƙungiyar siyasa mai suna Jam’iyyar Mutanen Arewa(JMA) a watan Oktoba 1948, wadda daga bisani Malam Sa’adu Zungur ya raɗa mata suna cikin harshen Ingilishi ya kira ta da “Northern People Congress”(NPC) (Dudley, 1968: 80-81) da (Yakubu, 1999:75).

Dangane da kafuwar jam’iyyar NPC kuwa, Dudley, (1968) da Birniwa, (1987) da Yakubu, (1999) da Idris (2016) duk sun yi bayani tare da kawo manufofin jam’iyyar da dalilan kafa ta.

An ƙaddamar da jam’iyyar NPC ranar 1 ga watan Oktoba, 1951, bisa ra’ayin sarakuna da shugabannin jam’iyyar a bisa manufofi da dama. NPC jam’iyya ce da ta samo asali daga ƙungiyoyi daban-daban na Arewa(Idris, 2016: 51).

Jam’iyyar ta samo tsittsigenta ne daga Jam’iyyar Mutanen Arewa (JMA) wadda ƙungiya ce daga cikin ƙungiyoyin da aka kafa, domin ci gaban yankin na Arewa. Ƙungiya ce da ta sadaukar da kanta wajen yaƙi da jahilci da lalaci da zalunci, waɗanda su ne manufofin da aka kafa jam’iyyar NPC a kansu tun a farko(Malumfashi, 2013:12). Daga cikin magoya bayan jam’iyyar waɗanda aka kafa jam’iyyar da su akwai; Sa’adu Zungur da Aminu Kano da Abubakar Tafawa Ɓalewa da Aliyu Makaman Bida. Daga bisani wasu da yawa sun bar jam’iyyar domin ta kauce wa manufofin da aka kafa ta a kansu(Birniwa, 1987: 28).

Bayan kafuwar jam’iyyar, sai ya kasance babbar manufarta ita ce yaƙi da jahilci da lalaci da zalunci da yin gyaran fuska ga hukumar En’e, don ta dace da zamani. Wannan ne ya sa daga farko Arewa ta kasance mai jam’iyya ɗaya, saboda ganin cewa NPC jam’iyyar neman sauyi da fafutukar samun ‘yanci ce, wannan ne ya sa aka hana jami’an gwamnati na wancan lokaci shiga cikinta(Yakubu, 1999: 76). Jam’iyyar ta dawo daga rakiyar manufofinta ne bayan ta lura cewa, ba ta samu goyon bayan sarakuna da muƙarrabansu da samari da ma’aikata ba, sai suka yi watsi da manufofinsu na farko, domin su samu jama’ar da za su cika jam’iyyar, wanda hakan zai ba su damar lashe zaɓe. Wannan sauyin manufofi da jam’iyyar ta yi ya jawo mata karɓuwa da kwarjini a wajen sarakuna da ma’aikatan En’e har ma da manyan masu faɗa a ji na Arewa. Hakan ya jawo mata gagarumar nasarar da ta yi a zaɓuɓɓukan da aka gudanar a Arewa, har ma da matakin gwamnatin tarayya, in ban da a watan Satumba na shekarar 1951 inda jam’iyyar NEPU ta yi nasarar lashe kujeru 12 cikin 26(Dudley, 1968: 80) da (Idris, 2016: 52).

Wani dalili kuma da ake ganin ya ƙara wa jam’iyyar NPC farin jini a wancan lokaci shi ne, kasancewar Alhaji Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato a cikin jam’iyyar, wanda kasancewarsa jinin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ya sa talakawa har ma da masu dukiya suka rungumi jam’iyyar.

Daga bayanan da aka kawo, an fahimci cewa, jam’iyyar NPC ce ta kafa gwamnati a Arewa har ma da ƙasa baki ɗaya, sakamakon rinjayen da alƙaluman zaɓe suka nuna cewa jam’iyyar ce ta sami kaso mafi tsoka na ƙuri’un da aka kaɗa.

Baya ga jam’iyyar NPC, jam’iyyar NEPU ita ce jam’iyyar hamayya mafi girma a Arewa da ma ƙasa baki ɗaya a wancan lokaci. Wannan jam’iyya ta samo asali ne daga ƙungiyar NEPA wadda tun farko ita aka fara kafawa tun a wuraren shekarar 1947. Daga bisani, sai ‘ya’yan ƙungiyar a Kano suka kafa ƙungiyar Taron Masu Zumunta (TMZ) da Ƙungiyar Matasan Kano (KYC) waɗanda su ne suka haɗe daga baya suka kafa jam’iyyar NEPU, bayan an hana JMA bayyana kanta a matsayin jam’iyyar siyasa(Dudley, 1968: 80).

  Masana da manazarta siyasa irin su Dudley, (1968) da Dambazau, (1981) da Birniwa, (1987) da Yakubu, (1999) da Malumfashi, (2009) da Idris, (2016), sun tofa albarkacin bakinsu dangane da kafuwa da manufofi da shugabanni da magoya bayan jam’iyyar NEPU, da ma duk wani abu da ya shafi jam’iyyar.

An bayyana cewa an kafa jam’iyyar NEPU ranar 8 ga watan 8 da misalin ƙarfe 8 da mutane 8 a shekarar 1950, wato shekara guda kafin ayyana NPC a matsayin jam’iyyar siyasa, bayan wani taro da wasu mutane 8 da suka haɗa da; Bello Ijumu da Abba Maikwaru da Mudi Sipikin da Magaji Ɗambatta da Baballiya Manaja da Musa Kaula da Abdulƙadir Ɗanjaji da kuma Garba Bida suka yi(Dambazau, 1981: 14). Wannan bayani ya fito a cikin jaridar Sodangi ta ranar 2 ga Maris, 1960 kamar haka:

“ Mutum takwas ne suka kafa NEPU ran takwas ga watan takwas bayan ta yi ɗimbin shekaru sai ga shi da lokacin zaɓen majalisar Najeriya ya zo ta sami wakilai takwas da ƙyar.”

 (“Mutum 84 Sun Fita Daga NEPU”, 1960).

Wannan ya nuna cewa haƙiƙanin ranar da aka kafa jam’iyyar hamayya mafi girma ta farko a Arewacin Nijeriya ita ce ranar takwas ga watan takwas kamar yadda tarihi ya nuna. An tabbatar cewa mutane takwas ne suka zauna suka kafa ta kamar yadda aka zayyano sunayensu a sama.

 Tun farko sun kafa jam’iyyar ce da manufar haɗa kan ‘yan ƙasa, ba tare da nuna bambancin addini ko ƙabila ko harshe ba, sannan a wayar wa talakawa kai kan sha’anin mulki da tabbatar da an mayar da mulkin jama’a ga hannunsu da kuma fafutukar neman ‘yancin kai daga Turawa. A wani wurin daban ma an ƙara samun bayani makamancin wannan dangane da kafuwar jam’iyyar NEPU kamar haka:

“Don na sani an kafa NEPU ran 8/8/1950 watau yau shekara tara da wata biyar, in an bi shekarar Turawa yau shekara goma ke nan ”

(Yakasai, 1960).

Ke nan idan aka dubi hujjojin biyu sun nuna kafuwar jam’iyyar a wannan rana da aka ayyana, har ma da lissafin adadin shekarun da jam’iyyar ta yi da kafuwa a wancan lokacin, wato shekaru kimanin goma ke nan daga shekar 1950-1959.

Idris, (2016:53) yana ganin cewa jam’iyyar NEPU ta samo asali ne daga ƙungiyoyi biyu masu kama da juna. Ƙungiya ta farko ita ce, masu ra’ayin neman sauyi da suka baro jam’iyyar NPC, bayan an ƙaddamar da jam’iyyar a 1950, sai kuma uwar ƙungiya, wato NEPA wadda tun da farko aka kafa a shekarar 1947 da niyyar haɗa kan jama’ar Arewa da wayar musu da kai kan sha’anin siyasa, domin ita da ma NEPA ba ta ƙaunar tsarin mulkin mallaka da kuma sarakunan da suka ɗaure musu gindi. Shi ya sa NEPU ta ɗora daga inda NEPA ta tsaya, wato ƙoƙarin ciyar da tattalin arziƙi gaba, sannan ta ci gaba da faɗa da zaluncin Turawa da danniyar sarakuna, domin fitar da talaka daga ƙangin bauta. NEPU jam’iyya ce ta talakawa, shugabanninta da magoya bayanta ba su wuce malaman makaranta ba, sai ‘yan garuwa da manoma da masaƙa da majema da maɗinka da masassaƙa da masu faskare da sauransu(Birniwa, 1987: 29-32).

Kasancewar NEPU ba ta neman fada a wajen Turawa da sarakuna kamar jam’iyyar NPC, wannan ya sa ta zama jam’iyyar hamayya. Hakan kuma ya jawo rashin jituwa tsakanin NEPU da hukuma, wanda ya sa gwamnatin mulkin mallaka ta shirya tare da tsara yadda za a yi NPC ta gaje ta ba NEPU ba.

Baya ga siyasar jamhuriya ta ɗaya da jam’iyyun da suka yi rawar gani a cikinta, an samu waɗansu jumhuriyoyi daban-daban, waɗanda su ma an kafa jam’iyyu kuma an gudanar da zaɓuka a cikinsu.

A jamhuriya ta biyu, a tsakanin shekarar 1978-1983, an samu kakkafa jam’iyyu bayan gwamnatin Obasanjo ta cire takunkumin siyasa tare da kafa hukumar zaɓe ta ƙasa. Ƙungiyoyi da dama, sun nemi a yi musu rajista, amma daga cikinsu biyar ne kawai suka sami nasarar zama jam’iyyu, bayan an yi musu rajista. Jam’iyyun su ne; NPN da UPN da NPP da PRP da GNPP. Bayan an gudanar da zaɓen shugaban ƙasa, hukumar zaɓe ta tabbatar da jam’iyyar NPN a matsayin wadda ta lashe zaɓe, inda Alhaji Shehu Shagari ya zama shugaban ƙasa. An kuma gudanar da zaɓen jihohi, wasu daga cikin sauran jam’iyyun sun samu nasarar lashe kujerun gwamnoni a wasu jihohi (Funtua, 2003: 37).

Sojoji sun kawo ƙarshen gudanar da mulkin farar hula ta jamhuriya ta biyu ne a shekarar 1984, inda suka ci gaba da jan ragamar mulkin ƙasar har na wani lokaci. An gudanar da wata gwamnatin gamin gambiza, wato ita ba soja zalla ba, ba kuma farar hula ba a yunƙurin sake komawa ga tafarkin dimokuraɗiyya da gwamnatin soja ta janar Ibrahim Badamasi Babangida ta yi.

An yi ƙoƙarin kafa jamhuriya ta uku, domin a wuraren shekarar 1987 an fara ganin alamun hakan, sannan kuma har an kafa ƙungiyoyin siyasa, kuma sun miƙa wa hukumar zaɓe, domin buƙatar a yi musu rajista. Bayan hukumar zaɓe ta miƙa wa gwamnati shawararta, sai gwamnati ta soke su duka, sannan ta ƙirƙiro jam’iyyu guda biyu, NRC da SDP, waɗanda a ƙarƙashinsu ne aka gudanar da zaɓen 12 ga watan Yuni, 1993, wanda kuma daga baya gwamnati ta soke. A dalilin wannan soke zaɓe, rikici ya ɓarke a cikin ƙasa, wanda ya kawo ƙarshen gwamnatin Janar Babangida ranar 27 ga watan Agusta, 1993(Funtua, 2003: 40-41). An miƙa gwamnatin a hannun Cif Shonekan a matsayin riƙon ƙwarya ya ci gaba da jagorancinta. Wannan gwamnatin ba ta yi dogon zango ba, domin kuwa sojoji sun sake yin juyin mulki a shekarar 1993. Hakan ya mai da janar Abacha ya zama shugaban ƙasa, inda suka soke duk wani tsari na miƙa mulki, wanda ya kawo ƙarshen jam’iyyun NRC da SDP. Daga baya sai gwamnati ta ci gaba da gudanar da wannan tsarin mai kama da angulu da kan zabo, wato soja-soja, farar hula, inda har aka kafa jam’iyyun siyasa daban-daban waɗanda suka haɗa da; UNCP da DPN da GDM da NCPA da CNC(Funtua, 2003: 40-41). Wannan yunƙuri bai yi nasara ba, sakamakon rasuwar shugaba Abacha a shekarar 1998, inda janar Abdulsalam Abubakar bayan zamansa shugaban ƙasa ya rusa waɗannan jam’iyyun da ma tsarin baki ɗaya tare da shimfiɗa wani sabo a shekarar 1999(Ɗan’illela, 2010: 23).

Ɗan’illela, (2010: 23) ya ci gaba da cewa, sabuwar gwamnatin Abdulsalami ta yi alƙawarin miƙa mulki ga hannun farar hula a ranar 29 ga watan Mayu na shekarar 1999, wanda shi ne ya share hanya zuwa jamhuriya ta huɗu. A wannan yunƙuri, an yi wa jam’iyyu rajista, wato jam’iyyun PDP da APP da AD da APGA da kuma PAP. Waɗannan jam’iyyu sun samar da ‘yan takara wanda a ƙarshe ɗan takarar jam’iyyar PDP Cif Olusegun Obasanjo ne ya yi nasarar zama shugaban ƙasa a zaɓen da aka gudanar a watan Janairun 1999(Funtua, 2003: 41).

A cikin tarihin siyasar ƙasar nan, jamhuriya ta huɗu wato wadda muke ciki yanzu, ita ce ma fi tsawo idan an kwatanta ta da sauran jumhuriyoyin da aka yi a baya. A cikin wannan zamanin siyasa da ake ne aka samu zangunan siyasa har guda shida, yanzu haka ana cikin zango na bakwai. Zango na farko na jamhuriya ta huɗu ya faro ne daga watan Mayu 1999 zuwa farkon shekarar 2003, zango na biyu kuwa ya fara daga watan Mayu 2003 zuwa farkon shekarar 2007, sai zango na uku wanda ya fara daga watan Mayu na shekarar 2007 zuwa farkon shekarar 2011, sai zango na huɗu ya fara daga 2011 zuwa shekarar 2015 (Idris, 2016:58). Akwai kuma zango na biyar wanda ya fara daga 2015 zuwa 2019, sai zango na shida daga 2019 zuwa 2023. A yanzu muna zango na bakwai ne wanda ya fara daga 2023. A zango na farko an kafa jam’iyyu biyar ne kacal, su ne; PDP da APP da AD da APGA da PAP waɗanda su ne suka yi zamani har zuwa zango na biyu, amma a zango na biyu an yi wa jam’iyyar APP gyaran fuska inda ta koma ANPP. A zango na huɗu kuma an samu ƙaruwar jam’iyyun siyasa, sai dai waɗanda suka yi tashe a yankin Arewa su ne: PDP da ANPP da AC da DPP, sannan kuma a nan Arewa an samu ƙarin jam’iyyar CPC, an kuma yi wa jam’iyyar AC kwaskwarima ta koma ACN. Daga zango na huɗu zuwa farkon zango na biyar, an samu jam’iyyun siyasa da aka yi wa rajista kimanin guda hamsin a wannan ƙasa.

Haka kuma, a zango na biyar na jamhuriya ta huɗu, an samu wani irin sauyin da a tarihin siyasar Nijeriya ba a taɓa samun irinsa ba, wato inda aka samu jam’iyyar hamayya ta yi nasara a zaɓen shugaban ƙasa. Wannan ko ya faru ne sakamakon haɗewar da wasu jam’iyyu guda huɗu suka yi. Jam’iyyun su ne; ANPP da ACN da CPC da wani ɓangare na magoya bayan jam’iyyar APGA, suka zama jam’iyya guda wadda aka raɗa wa suna APC, wadda a lokacin ta zamo jam’iyyar hamayya mafi girma a Nijeriya, kuma ita ce ta lashe zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar a shekarar 2015.

Bugu da ƙari, A zango na shida an samu jam’iyyun siyasa kusan 60[1] waɗanda aka tsaya takarar shugabancin ƙasa a ƙarƙashinsu, kodayake kaɗan ne daga cikinsu aka ji amonsu. A wannan zango da ake ciki wato zango na bakwai kuwa, an samu raguwar jam’iyyu ne sakamakon soke rajistar wasu da hukumar zaɓe ta yi, saboda rashin cika wasu ƙa’idoji, inda jam’iyyun suka zama guda goma sha takwas[2]. Waɗanda suka yi fice daga cikin jam’iyyun su ne, PDP da APC da LP da NNPP inda daga cikinsu bayan an gudanar da zaɓe, ɗan takarar jam’iyyar APC Bola Ahmad Tinubu ya yi nasara.

4.3 Ma’ana da Samuwar Rubutaccen Adabin Hausa

Kalmar adabi daɗaɗɗiyar kalma ce a cikin harshen Hausa. Bisa asali, an aro ta ne daga harshen larabci wadda take nufin halin ɗa’a ko fasaha ko ƙwarewa. Dangane da ma’anarta a Hausance, Ɗangambo (1984:1) ya bayyana cewa, kalmar adabi tana nufin madubin ko hoton rayuwa na al’umma. Rubutu kuwa shi ne zanen magana a kan takarda ko allo ko wani bagire (CNHN 2006: 374). Ke nan idan aka dubi ma’anonin kalmomin guda biyu, za a iya cewa rubutaccen adabi shi ne hoton al’amuran da suka shafi rayuwar al’umma wanda aka samar a rubuce.

Ta fuskar samuwar rubutaccen adabi kuwa, za a iya cewa ya samu ne bayan da ɗan’adam ya samu fasahar rubutu a doron ƙasa, maimakon ya ci gaba da aiwatar da adabinsa a gargajiyance wato ta fatar baki, sai ya koma yana zana shi kan abin da yake rubutu kansa.

Dangane da al’ummar Hausawa ma ba ta sake zane ba, domin bayan samuwar hanyar rubutu, sai adibai suka fara amfani da wannan hanyar wajen isar da saƙo a rubuce. Ingantacciyar hanyar rubutu ta farko da aka samu ita ce Ajami, wanda ya samu bayan cuɗanyar Hausawa da Larabawa abin da ya haifar da shigowar addinin Musulunci a cikin ƙasar Hausa. Hausawa sun riƙa sarrafa baƙaƙen Larabci wajen rubuta Hausa da su. A wannan yanayi, malamai sun yi amfani da hanyar Ajami wajen samar da ayyukan adabi daban-daban. Ɓangaren da ya yi fice wanda malamai suka yi ayyuka a cikinsa shi ne waƙa. Daga bisani bayan zuwan Turawa waɗanda suka zo da rubutun boko, an samu ‘yan ƙasa waɗanda suka koya, suka kuma riƙa samar da ayyukan adabi a cikin rubutun boko. An samu ayyukan adabi da dama waɗanda aka samar daga cikin dukkan rassan adabi guda uku, wato waƙa da zube da kuma wasan kwaikwayo.

4.4 Ma’ana da Samuwar Rubutaccen Adabin Siyasa

Kamar yadda aka bayyana ma’anar rubutaccen adabi a baya, ke nan za a iya cewa rubutaccen adabin siyasa wani nau’in adabi ne wanda yake ƙunshe da al’amuran siyasa a cikinsa, wanda ya shafi tafiyar da al’amuran jama’a da shugabanci da dai sauransu.

Tun fil azal, Hausawa suna da irin nau’in siyasar da suke gudanarwa, wadda ta shafi mulkin gargajiya, wanda aka kira shi na Musulunci bayan jihadin Shehu Ɗanfodiyo. Tun kafin zuwan Musulunci Hausawa suna gudanar da shugabancinsu a tsarin gargajiya. A wancan lokacin ba a samu wasu ayyuka da suke nuna samuwar adabin siyasa ba, sai bayan zuwan Shehu Ɗanfodiyo, inda aka samu ayyukan malaman jihadi waɗanda mafi yawan su waƙoƙi ne, kuma su ne suka fara fitowa da ruhin siyasar Musulunci a cikin rubutaccen adabi. Alal misali, Hiskett, (1975:13) ya bayyana irin yadda tasirin cuɗanyar da aka samu da baƙin al’ummu ya haifar da samuwar hanyar rubutu, wanda ake ganin ya taimaka ƙwarai wajen samuwar rubutaccen adabi, ciki kuwa har da adabin Hausa. An nuna bayan samuwar tsarin rubutun Larabci da na Ajami ne aka fara samun rubutattun waƙoƙi, tun kafin jihadi da kuma bayan jihadi, inda tun a wannan lokacin ake ganin an fara samun waƙoƙi masu ɗauke da ruhin siyasa. Haka kuma an samu wasiƙu da sarakuna suka riƙa aike wa junansu wanɗanda suke ƙunshe da abubuwan da suka shafi mulki da siyasa da al’amuran jagorancin al’ummominsu. Ke nan an samu ɓullar rubutaccen adabin siyasa ne bayan zuwan Musulunci, musamman kuma bayan jihadin Shehu Ɗanfodiyo.

4.4.1 Rubutattun Waƙoƙin Siyasa

Rubutattun waƙoƙin siyasa na Hausa su ne suka share wa sauran ɓangarorin rubutaccen adabin siyasa hanya, domin su aka fara samu a farko kafin sauran ɓangarorin da suka shafi zube da wasan kwaikwayo. Wannan ba zai rasa nasaba da yadda waƙa ta kasance hanyar koyo da koyar da ilimin addini a zamanin masu jihadi ba. Kasancewar waƙa ta fi saurin isar da saƙo ga al’umma, wannan ya sa bayan zuwan Shehu Usmanu Ɗanfodiyo, ƙanensa Abdullahi Fodiyo ya rubuta wata waƙa mai suna “Tsarin Mulki na Musulunci” wanda a ciki ya yi bayanin yadda tsarin mulki na Musulunci yake da yadda ya kamata shugaba da mabiyansa su kasance, akwai waƙar “Murnar Cin Birnin Alƙalawa” wadda ita ma tana magana ne a kan tsarin shugabanci a Musulunci. Shi ma Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ya rubuta waƙar “Wallahi-Wallahi” in ya yi bayani kan irin haƙƙoƙin shugaba da irin narkon azaba da zai haɗu da shi idan bai yi wa mabiyansa adalci ba. Waɗannan waƙoƙin sun kasance suna kira ne ga yin ɗa’a ga Allah da manzonsa da kuma shugabannin Musulmi na wancan lokaci, wato sarakuna, domin ci gaban tsarin mulkin da Shehu ya shimfiɗa bayan jihadi da kuma wayar wa al’umma kai kan abin da ya shafi addini(Hiskett, 1975:12).

Bayan samuwar rubutun boko, an ci gaba da samun waƙoƙi masu ɗauke da wannan ruhi na siyasa, duk da cewa lokacin ba a fara batun siyasar jam’iyyu ba, amma kuma siyasar neman ‘yancin kai da ta tsarin mulki da tsarin shugabancin sarakuna, da tsarin mulkin Turawa su ne cike a cikin waƙoƙin(Hiskett, 1975:13).

Bayan zuwan Turawan mulkin mallaka a ƙarni na ashirin sun rusa tsarin mulkin daular Usmaniyya wadda take na Musulunci ne, sannan an samu sabon tsarin siyasa wanda Turawan suka zo da shi, inda daga ciki aka samu siyasar jam’iyyu da aka kakkafa domin gudanar da zaɓuɓɓuka ƙarƙashinsu. An samu marubuta da dama waɗanda suka rubuta waƙoƙi domin faɗakarwa ga jama’a, game da muhimmancin shiga harkokin siyasa da jam’iyyar da ta dace.

Tun kafin samuwar jam’iyyun siyasa, an kakkafa ƙungiyoyin wayar da kai kan abin da ya shafi siyasa da mulkin Turawa. Daga baya sai ƙungiyoyin suka rikiɗe suka zama jam’iyyun siyasa(Dudley, 1968: 77-78).

‘Yan kishin ƙasa waɗanda suka samu ilimin zamani su ne suka yi hoɓɓasa wajen ganin an samu ‘yancin kai. Bayan samuwar hakan kuma su ne suka zama jagororin siyasar jam’iyyun da aka kafa. Bugu da ƙari kuma, wasu daga cikinsu ne suka rubuta waƙoƙin siyasa tun a karon farko. Misali; Malam Sa’adu Zungur ya rubuta waƙoƙi ciki akwai, “Arewa Jamhuriya ko Mulukiya” wadda ba waƙar siyasar jam’iyya ba ce. Daga bisani, sai ya rubuta Waƙar “Jihadin Neman Sawaba” wadda waƙar siyasar jam’iyya ce, a matsayinsa na ɗan jam’iyyar NEPU wanda yake yin suka ga ‘yan jam’iyyar NPC mai mulki. Shi ma Mudi Sipikin ya rubuta waƙar “Arewa jamhuriya Kawai” wadda ba ta shafi wata jam’iyya ba, amma daga bisani bayan kafa jam’iyyu, ya rubuta waƙoƙin siyasar jam’iyyu musamman ma na jam’iyyar NPC. Mawaƙa irin su Gambo Hawaja Jos da Aƙilu Aliyu da Lawal Maiturare da Yusuf Kantu da sauransu duk sun rubuta waƙoƙin siyasa a wannan lokaci, waɗanda kusan za a iya cewa, su ne mabuɗin samuwar waƙoƙin siyasar jam’iyya a Arewacin Nijeriya(Ɗangulbi, 2003: 54).

4.4.2 Rubutaccen Zube na Siyasa

Rubutaccen zube na siyasa wani nau’in adabi ne wanda aka shirya shi cikin wani tsari da ba na waƙa ba, ba kuma wasan kwaikwayo ba, wanda yake ɗauke da ruhin siyasar da ta shafi tafiyar da al’amuran al’umma da jagoranci a gargajiyance ko kuma a zamanance. Galibi irin wannan rubutun yakan zo kara zube ba tare da wata ƙa’ida ba illa ta ƙa’idojin rubutu.

Bincike ya nuna cewa, rubutaccen zube mai ɗauke da ruhin siyasa bai samu karɓuwa sosai a cikin al’umma ba a karon farko, domin yawanci marubutan malamai ne waɗanda al’amuransu ya fi ƙarfi a kan wa’azi da faɗakarwa. Daga cikin nau’o’in zuben da aka samu a farko akwai wasiƙu da sarakuna suke aika wa junansu, da huɗubobi na Juma’a waɗanda limamai kan rubuta. Daga baya an samu wasu nau’o’in zube masu ɗauke da ruhin siyasa bayan zuwan Turawan mulkin mallaka. Ire-iren waɗannan nau’o’in rubutaccen zuben sun haɗa da jaridu da jawaban siyasa da ƙagaggun labarai. Dangane da waɗanda za a ce su ne ayyukan rubutaccen zube na siyasa da aka fara ganin ɓullarsu da kuma bunƙasarsu su ne jaridu.

Samuwar jaridu a ƙasar Hausa sun taimaka ƙwarai wajen ci gaban siyasa musamman ma siyasar jam’iyya. Jaridar Hausa ta farko da aka fara samu a ƙasar Hausa ita ce jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo a shekarar 1939, wadda aka samar da ita domin farfagandar yaƙin duniya na biyu(Yahaya, 1988:142). A wani binciken kuma ana ganin cewa, jaridar Hausa ta farko ita ce Jaridar Nijeriya Ta Arewa wadda aka samar a shekarar 1932 (Bunza da Mallam, 2018:293). Duk da cewa an yi amfani da harsuna uku a cikin jaridar wato Hausa da Ingilishi da kuma Larabci, amma dai samun wani ɓangare na Hausa a cikinta ya sa ta zama ta farko da aka fara buga labarai da Hausa.

 Tun daga shekarar 1954 kuma Gwamnatin Arewa ta samar da jaridu na Larduna. Zuwa shekarar 1956 kusan kowane Lardi yana da tasa jaridar. A Lardin Kano, inda nan ne hedikwatar ko mazaunin NEPU, jaridar Sodangi da Daily Mail su ne tambarin NPC wajen farfagandar siyasa. Ta amfani da waɗannan jaridu hukumar mulkin mallaka da jam’iyyar NPC suka shiga yaɗa zantukan hamayya game da NEPU da magoya bayanta, sannan kuma hukuma ta tabbatar ba a ba ‘yan hamayya damar amfani da jaridun ba, balle a ji ta bakinsu. Duk wani aikin ci gaba ko wani abu da hukuma ta san zai sa NEPU ta sami tagomashi ko goyon baya, to ba a sa shi a cikin jaridun Sodangi da Daily Mail. Waɗannan jaridun sun kasance mallakin gwamnati ce, don haka an yi amfani da su wajen yaɗa manufofin gwamnati da kuma yaƙar ‘yan hamayya.

Daga baya jam’iyyar hamayya ta NEPU ta ƙulla ƙawance da NCNC. Wannan ƙawance da aka ƙulla shi ne ya sama masu wata kafa da suka riƙa mayar da martani game da farfagandar hukuma da jam’iyyar NPC. Wannan ne ya sa aka samar da jaridar Daily Comet da kuma jaridar Northern Star ta jam’iyyar AG a Kano, aka keɓe wani ɓangaren jaridun domin ɗimbin masu karantun Hausa, domin sun riga sun san cewa farfaganda ta fi armashi a cikin harshen da mutane ke fahimta (Malumfashi, 2013:12). Samuwar waɗannan jaridun ya tayar wa da magoya bayan jam’iyyar NPC hankali, wannan ya sa suka yi ta kiraye-kiraye a kan a tsawatar wa ‘yan hamayya kan abin da suka kira cin mutunci da zage-zage da suke yi a cikin jaridun Daily Comet da Nothern Star. Ga misali:

“ makon da ya wuce an yi masmitin a ƙofar Mata. An yi maganar zage-zage da wasu marasa albarka suke farfaɗa a cikin ‘Nothern Star’ kullum. Mutane da yawa sun goyi bayan munin abin da ake rubutawa. Ba shakka ba za mu yadda ba, don yawan zagin shugabannin ya yi yawa. Har yanzu ba a yi komai a kai ba. tun da wuri ya kamata shugabannin NPC su tashi tsaye a kan wannan mummunan aiki. Tun ice na ɗanye ake tanƙwasa shi, in ya bushe sai an sha wuya. Mace da namiji kowa yana ganin irin cin mutuncin da Northern Star take yi wa shugabanni kullum, don kuwa ba ita ce kaɗai jarida a Nijeriya ba.”

(“Baƙin Ciki Ya yi Yawa”, 1960).

Lallai wanzami ba ya son jarfa! Duk da yadda jaridun Sodangi da Daily Mail suka samu ɗaurin gindin gwamnati, suka riƙa yi wa ‘yan hamayya yarfe da zambo da farfaganda lokacin ba su da bakin da za su rama, ko kuma ba su da muryar da za su mayar da martani a ji su, hakan bai zama laifi ba sai da ‘yan hamayya suka samu dama suka mayar da martani sannan cibi ya zama ƙari.

Baya ga nuna jin zafi da gwamnati da magoya bayanta suka yi a cikin jaridar Sodangi, sun kuma buƙaci a riƙa hukunta duk wanda ya yi zagi ko yarfe ko a kira shi a titsiye shi sai ya faɗi ko da wa yake yi, kamar yadda jaridar take cewa:

“Mu abin da muka ga ya fi a kan irin wannan sheɗana a taƙaice shi, hukuma ko gwamnati ta sa a kawo mai irin wannan cin mutunci gaban komati a titsiye shi cikin lumana a tambaye shi cewa, ‘wa kake nufi da mai abu kazako mai yin abu kaza’. In ya ce wane nake nufi to, a ce ka rantse da Alƙur’ani? In ya ce ‘i’ to sai a je ya yi wanka a gani a kuma ga rantsuwarsa. In ya yi haka ya kuɓuta. In kuwa ya yi shiru ya yi iƙirari ke nan sai a hukunta shi a bisa yadda shari’a ta ce.”

(“Zage-Zage”, 1960).

 A nan idan aka duba, za a ga cewa irin abin nan ne da masu hikimar suke cewa; Baƙar magana ba zagi ba ce, amma ta ɗara zagi ciwo. Duk da cewa gwamnati da mahukunta da ‘yan jam’iyyar NPC mai mulki sun yi ta amfani da jaridar gwamnati wajen yaɗa farfaganda da yarfen siyasa ga ‘yan hamayya a tashin farko, wato kafin ‘yan hamayya su samu kafar da za su riƙa mayar da martani, amma da ya kasance an samu hanyar da ‘yan hamayyar za su yi magana muryarsu ta yi nisa kuma ta kai ga inda ake buƙata, sai abin ya riƙa yi wa masu mulki da ‘yan jam’iyya mai mulki ciwo, har suka fara neman hanyoyin dakushe muryoyin abokan hamayya. Suka riƙa kiraye-kiraye cewa a kashe jaridun yan hamayya ma baki ɗaya, domin a cewarsu zagin manya suke yi. An sani cewa kusan duk ‘yan siyasar da suke cikin jam’iyyar NPC mai mulki sarakuna ne da malamai da attajirai, wannan ya sa magoya bayan NPC suke ganin cewa jaridun suna zagin manyan ƙasa don haka bai kamata a bar su su ci gaba ba. Dubi abin da suka ce:

“Wannan jarida ana raina jama’a kuma ana wulaƙanta manyan malamai da shugabanni ƙiri-ƙiri Na tabbata duk wanda ba ya ƙaunar a raina na gaba ba zai so jaridun nan biyu ba: Nothern Star da Comet.”

(Kano, 1960).

An sani cewa, yawanci ‘yan siyasa kan yi amfani da gugar zana ne wajen sukan abokan hamayyarsu, wanda hakan ba zai hana a fahimci ko da wa suke yi kai tsaye ba, amma dai ba za a iya kama su da laifin cin mutuncin wani ko wata ba don ba su ambaci suna ba. Duk da haka jam’iyya mai mulki abin yana mata ciwo, shi ya sa ma ta fara neman hanyar da za a riƙa kama duk wanda ya yi wa masu mulki shaguɓe a tursasa su sai sun faɗi ko da wa suke yi. Daga ƙarshe jaridar Sodangi kasancewar ta ta gwamnati roƙo ta yi da cewa:

“Muna roƙon Gwamnatin jiha ta yi tunani matsananci ta duba maganar shawarar nan ta a ruguza Northern Star da Daily Comet. Abin da gwamnati ta ga ya fi shi za ta yi a kansu.”

(“Kashe Wasu Jaridu”, 1960)

Kasancewar jaridun guda biyu dukkansu na ‘yan hamayya ne, kuma ba su barin jam’iyya mai mulki da magoya bayanta su sha ruwa, wannan ya sa suka fara neman hanyar da za a kashe bakin tsanya, wato a dakushe muryar jam’iyyar NEPU wadda ta kasance ƙawar NCNC ce da kuma Jam’iyyar AG. Hakan bai samu ba kasancewar dukkan jam’iyyun sun zame wa jam’iyyar NPC ƙadangaren bakin tulu.

Tun a wuraren shekarar 1933-1938 aka samu littattafan zube na ƙagaggun labarai na Hausa na farko. A cikin wasu littattafan an samu waɗanda suke ɗauke da ɓurɓushin siyasa, duk da cewa dai ba shi ne babban saƙon da littattafan suke ɗauke da shi ba, amma dai an samu abin da za a faɗa, kuma a danganta shi da siyasa a cikin su. Alal Misali, littafin Ruwan Bagaja na Abubakar Imam ya hasko yadda siyasar gargajiya ta tsarin sarauta da shugabancin al’umma take. Shi kuma littafin Ganɗoki na Bello Kagara ya fito da irin yadda siyasar Turawan mulkin mallaka ta gudana, wadda ta shafi yaƙe-yaƙen da Turawa suka yi da sarakunan ƙasar Hausa wanda bayan cinye ƙasar Hausar ne suka kafa tsarin mulki irin nasu. Akwai littafin Magana Jari ce na Abubakar Imam a shekarar 1938, wanda a cikin labaru da dama na cikin littafin an nuna tasirin siyasar gargajiya da mulki da ƙarfin iko irin na sarakuna, da kuma yadda ake girmama su.

Da tafiya ta yi nisa, lokacin da aka fara hada-hadar karɓar mulkin kai, nan ma an samu tasirin siyasa ƙwarai cikin rubuce-rubucen adabin wannan lokacin, domin kuwa ɓullar jam’iyyun siyasa ya ƙara wa abin armashi, kasancewar kusan dukkan ayyukan adabi na wannan lokacin suna ɗauke da wannan ruhin. Bayan samun yancin kan Nijeriya a shekarar 1960 da kafa jumhuriyoyin siyasa tun daga jamhuriya ta ɗaya har zuwa ta huɗu, an ci gaba da samun littattafan zube na ƙagaggun labarai waɗanda suka fito da tasirin siyasar jam’iyyu a cikinsu. Alal Misali, Littafin Tura Ta Kai Bango na Sulaiman Ibrahim Katsina da Tsuntsu Mai Wayo na Bala Anas Babinlata da Kan Mage Ya Waye na Ibrahim Isa Jiƙamshi da Kowa Ya Bi na Abdurrashid Sani Isa da Dambarwar Siyasa na Aminiya-Trust da dai sauransu.

4.4.3 Rubutaccen Wasan Kwaikwayo Na Siyasa

Rubutaccen wasan kwaikwayo nau’in adabi ne da yake zuwa a cikin wani tsari na daban a rubuce cikin littafi, don samun abin karantawa a makarantu wajen koyar da ɗalibai ko a karanta don nishaɗi. (Umar, 2022: 70). Ta la’akari da wannan ma’anar za a iya cewa duk wasan kwaikwayon da ya ɗauki wannan sigar da aka kawo a sama kuma ya ƙunshi jigon siyasa a cikinsa shi ake kira rubutaccen wasan kwaikwayo na siyasa.

Rubutaccen wasan kwaikwayo gaba ɗayansa ya kasance baƙo idan aka kwatanta shi da sauran rassan adabi na rubutacciyar waƙa ko zube (Galadanci da wasu 1992:19; Malumfashi, 1984: 3). Rubutun Ajami shi ne ya fara zuwa ƙasar Hausa a ƙarni na 15, sannan sai rubutun boko ya biyo bayansa a ƙarni na 19. A ɓangare guda kuma rubutun Ajami ya zo ne tare da addinin Musulunci wanda bai ba wasa matsayi ba (Malumfashi, 1984: 19; ‘Yar’aduwa 2007: 35; Yusuf 2008: 88). A ɗaya ɓangaren kuwa rubutun boko ya zo ne tare da addinin kiristanci, musamman a kudanci da tsakiyar Nijeriya, wanda bai yi nasarar kawo wannan addini ba a ƙasar Hausa in ban da ilimin boko (Umar, 2022:70).

Tun a farkon ƙarni na 20 aka fara samun rubutattun wasannin kwaikwayo, sai dai ba a samu wasanni masu ɗauke da ruhin siyasar jam’iyyu kai tsaye ba sai a littafin Kukan Kurciya na Mahmud Barau Bambale wanda aka buga a shekarar 1993. Kodayake, kafin wannan lokaci an samu wasu wasanni da Malam Aminu Kano ya rubuta waɗanda ba a buga su ba, da suka shafi gwagwarmayar kawo sauyi ne da ‘yanta al’umma bisa aƙidar kawo daidaiton ajin matsayi na al’umma da siyasa da kuma gurguzu wato rayuwar bai-ɗaya(Umar, 2022:78). Daga cikin wasannin da ya rubuta akwai: Kai Wane Ne A Kasuwar Kano? , Da Gudumar Dukan En’en Kano da Ƙarya Fure Take Ba Ta ‘Ya’ya da Alhaji Kar Ka Ɓata Hajjinka A Banza da sauransu[3]. Duka waɗannan wasanni ya riƙa rubuta su yana sanya ɗalibansa suna aiwatarwa domin wayar wa da al’umma kai a kan aƙidun gwagwarmaya da fafutukar ƙwatar wa talaka ‘yanci daga mulkin danniya da zaluncin da sarakunan Arewa da Turawan mulkin mallaka suke yi masu. (Paden, 1968:276) da (Umar,2022:79). Malam Aminu Kano ya miƙa waɗannan wasannin ga jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo domin a buga su, amma kasancewar wasannin sun yi kakkausar suka ga manufofin gwamnati da sarakunan Arewa sai suka ƙi karɓa balle su wallafa. Daga baya-bayan nan aka samu littafin rubutaccen wasan kwaikwayo na siyasa mai suna Tutar Babu wanda Kabir Yusuf Anka ya rubuta a shekarar 2019.

Daga bayanan da aka kawo an fahimci cewa, wannan ɓangare na rubutaccen wasan kwaikwayo na siyasa bai samu tagomashi ba, musamman idan aka yi la’akari da sauran ɓangarorin rubutattun waƙoƙin siyasa da na zube.

4.5 Dalilan Da Suka Haifar Da Ƙamfar Wasu Ɓangarori Na Rubutaccen Adabin Siyasa.

Ayyukan adabi da suka shafi siyasa, musamman siyasar jam’iyyu, wani ɓangare ne mai muhimmanci a cikin aikin adabi, kasancewar siyasa ta zama tamkar jinin jikin ‘yan’adam, domin rayuwa ba ta yiwuwa sai da ita, kuma ana gudanar da ita ko cikin sani ko kuma cikin rashin sani. Wannan ne ma ya sa al’amuran siyasa suke bayyana a cikin kowace gaɓa ta rayuwa. Ke nan, ba za a yi mamaki ba idan aka gan ta ta bayyana tamkar rana lokacin Azahar a cikin ayyukan adabin al’ummar wannan zamanin. Duk da cewa siyasa ta riga ta yi ƙarfi a cikin wasu ɓangarori na adabi, duk da haka akwai ɓangarorin da aka samu ƙamfar rubutattun ayyukan adabin siyasa. Wannan kuwa ba zai rasa nasaba da wasu dalilai da wannan bincike ya gano ba, waɗanda ake ganin su ne suka hana wannan nau’in adabi bunƙasa. Daga cikin dalilan akwai:

4.5.1 Tasirin Ilimin Addinin Musulunci

Addinin Musulunci addini ne wanda al’ummar Hausawa suka karɓa, kuma suka yi imani da shi bayan samun cuɗanyarsu da Larabawa wanda ta hanyarsa ne aka samu hanyar rubutu na farko, wato Ajami. Addinin Musulunci ya yi tasiri ƙwarai wajen bunƙasar wasu ɓangarori na rubutaccen adabi, kuma ya taimaka wajen samun naƙasu ga wasu ɓangarorin. Alal misali, rubutacciyar waƙa ta girmi rubutaccen zube da wasan kwaikwayo, kuma ta fi karɓuwa a wajen al’umma a kan sauran takwarorinta. Wannan ba zai rasa nasaba da yadda malamai suka riƙa amfani da ita wajen yaɗa addini a lokacin jihadi ba. Waƙa ta samu karɓuwa a zukatan al’umma ta yadda kusan duk saƙon addini da ake son isarwa a lokacin jihadi akan yi amfani da ita, domin ta fi saurin shiga zuciya da ƙwaƙwalwa fiye sauran rassan adabi (Adamu, 2015:128).

Tun kafin zuwan Turawa ƙasar Hausa, an samu waƙoƙi masu ɗauke da ruhin siyasa wanda malaman jihadi suka rubuta. Wannan ya ƙara wa marubuta waƙoƙi ƙwarin gwiwa wajen samar da wasu waƙoƙin siyasa bayan zuwan Turawa da samuwar siyasar jam’iyyu, hakan ya sa rubutattun waƙoƙin siyasa suka yawaita, kuma aka samu bunƙasarsu fiye da sauran rassan adabi.

Ta fuskar rubutaccen zube, za a fahimci cewa, duk da akwai nau’o’in rubutaccen zube da addini bai ƙyamace su ba kamar saƙo a rubuce wanda ya shafi wasiƙa da akan aike wa sarakuna da masu mulki da makamantansu, da jawabi a rubuce da wa’azi wanda ya ƙunshi huɗubobi na malamai da dai sauransu. Abin da ya shafi rubutattun labaran ƙirƙira kuwa wannan bai samu tagomashi ba a karon farko. Kasancewar duk marubutan da suka samu ilimi a farko malamai ne masana ilimin addinin Musulunci, wannan ya sa suka kalli rubutun adabi na ƙagawa a matsayin ƙarya, ƙarya kuma babban laifi ne a cikin addinin Musulunci. Hakan ya sa wannan ɓangaren bai samu tagomashi sosai ba da farko. Daga bisani bayan zuwan Turawa sai aka fara samun irin wannan nau’in na rubutaccen adabi, sai dai ba a samu ,masu ɗauke da ruhin siyasa ba kamar yadda waƙoƙi suka samu karɓuwa sai daga baya. Kusan dai za a iya cewa shi ma wannan ɓngaren bai samu ayyukan siyasa sosai ba, saboda ƙyamar da addini yake da shi dangane ɗabi’ar ƙarya.

Idan kuwa aka dubi fannin wasan kwaikwayo za a ga cewa, malamai na addinin Musulunci a ƙasar Hausa suna da fahimtar cewa, addini baki ɗayansa bai zo da wasa ba. Don haka tun daga nan aka yi wa rubutaccen wasan kwaikwayo raunin da ya hana shi warkewa balle, ya tashi ya yi rawar gaban hantsi. Wannan shi ne babban dalilin da ya sa wannan ɓangare na rubutaccen adabin siyasa bai samu karɓuwa ba, kuma ya kasance shi ne mafi ƙamfa cikin ayyukan adabin siyasa a rubuce.

4.5.2 Mulkin Soja

Idan aka yi batun rubutattun ayyukan adabi musamman na siyasa za a tarar cewa, mafi yawa waɗanda aka samar cikin waƙoƙi da zube da wasan kwaikwayo duk zamanin mulkin farar hula aka samar da su. Wannan ba zai rasa nasaba da cewa soja suna da dokokinsu waɗanda suka sha bamban da na farar hula. Idan ana batun siyasa to tunani yakan karkata a kan mulkin farar hula ne ba soja ba, shi kuwa adabin al’umma yana nuna rayuwarsu ne, don haka in za a yi batun siyasa sai dai a yi ta a mulkin farar hula.

Idan aka duba za a ga cewa an samu wasu shekaru masu yawa da sojoji suka ɗauka suna mulki wanda za a iya cewa sun kawo wa rubutattun ayyukan adabin siyasa tarnaƙi. Wannan ne ya sa rubutattun waƙoƙin siyasa suka samu daga wuraren 1950 lokacin da aka fara siyasar jam’iyyu har zuwa 1966 lokacin da sojoji suka yi juyin mulki na farko wanda ya kawo ƙarshen jamhuriya ta ɗaya.

Haka kuma an ci gaba da samun rubutattun ayyukan adabin siyasa a tsakankanin shekarun 1979-83, wato zamanin jamhuriya ta biyu. Haka ma a rusasshiyar jamhuriya ta uku a shekarar 1993 lokacin da soja suka shelanta miƙa mulki ga farar hula shi ma an samu rubutattun ayyukan adabi na siyasa kama daga waƙoƙi da zuwa wasan kwaikwayo. A jamhuriya ta huɗu wadda ta fara daga 1999 zuwa yau an samu rubutattun ayyukan adabi da dama, kuma a kullum waƙa ita ce take ɗaukar kaso mafi tsoka a cikin rassan adabin na Hausa.

Lura da wannan bayanin za a ga cewa, tun daga juyin mulki na farko a shekarar 1966 zuwa farkon jamhuriya ta huɗu wadda muke ciki a yanzu, an samu sojoji sun shafe shekaru ashirin da takwas suna mulki. Ga jerin shugabannin mulkin soja da tsawon lokacin da suka ɗauka suna mulki kamar haka:

1- Manjo Janar Aguyi Ironsi (1966)

2- Janar Yakubu Gowon (1966 zuwa 1975)

3- Janar Murtala Ramat Mohammed (1975 zuwa 1976)

4- Manjo Janar Olusegun Obasanjo (1976 zuwa 1979)

5- Manjo Janar Muhammadu Buhari (1983 zuwa 1985)

6- Janar Ibrahim Badamasi Babangida (1985 zuwa 1993)

7- Janar Sani Abacha (1993 zuwa 1998)

8- Janar Abdulsalami Abubakar (1998 zuwa 1999)

Waɗannan su ne jerin sunayen shugabannin da suka mulki Nijeriya a ƙarƙashin mulkin soja. Kuma daga na farko zuwa ƙarshe idan aka lissafa za a ga cewa sun shafe kimanin shekaru 28 suna mulki idan aka lissafa tsawon lokacin da kowannen su ya shafe a kan mulki. Wannan kaɗai ya isa ya kawo wa rubutattun ayyukan adabin siyasa tsaiko, ya kuma haifar da ƙamfarsu.

4.5.3 Ɓullowar Finafinan Ƙasashen Waje

Kalmar fim tilo ce, jam’in kalmar shi ne finafinai. Fim na nufin haɗuwar ayyuka da maganganun mutane daban-daban da amfani da wasu abubuwa marasa rai ta hanyar kwaikwayo ko ƙagawa da suka yi a cikin hoton da ake kallo ta hanyar amfani da na’urorin ɗaukar hoto da nuna shi ga jama’a, wanda yake ɗauke da wani saƙo ko saƙonni zuwa ga al’umma da aka yi abin dominsu(Usman da Bunza, 2021).

Finafinan ƙasashen waje sun samu ne tun kafin samun ‘yancin kai. An samar da gidajen silima a ƙasar Hausa waɗanda Turawa suka riƙa amfani da su wajen yaɗa farfaganda da sunan ilimantarwa don su ci gaba da shimfiɗa mulkin mallaka a ƙasar Hausa (Na’Allah, 2004: 54). Na’Allah(2004:55) ya ci gaba da cewa, a farko Turawa sun riƙa amfani da silimar tafi-da-gidanka(mobile cinema) zuwa lungu da saƙo na ƙasar Hausa domin yaɗa farfagandarsu. Sun riƙa bi makarantu domin nuna finafinai ko wasannin kwaikwayo waɗanda marubuta irinsu Shakespeare suka rubuta, waɗanda littattafansu sun yi fice a tsakanin ɗaliban adabi.

Daga bisani an samu Turawan mulkin mallaka sun samar da gidajen silima a kusan dukkan manyan garuruwan ƙasar Hausa kamar Sakkwato da Kano da Kaduna da sauransu. Baya ga finafinan Turawa na yaɗa farfaganda, sai kuma aka samu finafinan Indiya da na Sin waɗanda ake nunawa a irin waɗannan gidajen na silima a kowace rana. An samu yaɗuwar waɗannan finafinan ne ta hannun ‘yan kasuwar ƙasashen Lebanon waɗanda su ne suka mallaki kusan dukkan gidajen silima da suke a yankin Arewacin Nijeriya a shekarun 1950. Finafinan Indiya su ne suka mamaye kusan dukkan gidajen silimar da ake da su a ƙasar Hausa tun daga wancan lokaci har zuwa shekarun 1990. Haka kuma su ne aka riƙa nunawa kowane dare a gidajen talabijin, sau shida a cikin kowane mako a duk faɗin Arewacin Nijeriya. (Ahmad, 2004: 154).

Waɗannan gidajen kallo sun ɗauke wa matasa hankali ta yadda suka juyar da tunaninsu ga kallon al’adun Turawa da na Indiyawa da na al’ummar ƙasar Sin. Kai hatta waƙoƙin da ake sanyawa a gidajen radiyo da talabijin sai ya kasance waƙoƙin Indiya sun kwashi kaso mafi tsoka, duk da cewa ba a fahimtar me suke faɗa a cikin waƙoƙin nasu maimakon waƙoƙin Hausa da aka sani. Wannan ya sanya tunanin rubuta adabin Hausa na siyasa bai shiga zuciyar matasa ba, abin da ya taimaka ƙwarai wajen dakushe samuwar rubutaccen adabin siyasa a ƙasar Hausa.

4.5.4 Tasirin Soyayya

Soyayya na nufin nuna ƙauna daga ɓangarori biyu na masu ƙaunar juna musamman mace da namiji (CNHN, 2006: 398). Bayan samuwar shirin bayar da ilimi bai ɗaya na gwamnatin tarayya (UPE) a shekarar 1976, an samu waɗanda suka samu ilimin zamani da dama musamman mata, waɗannan suka duƙufa wajen rubuce-rubucen littattafai na ƙagaggun labarai musamman na soyayya (Ahmad, 2004:155 da Malumfashi, 2018:409). Ke nan, samuwar ƙagaggun labaran soyayya ba zai rasa nasaba da samuwar ilimi da kuma cuɗanyar da aka samu tsakanin maza da mata a makarantun boko ba a lokacin. Ga kuma tasirin kallon finafinan Indiya waɗanda yawancinsu na soyayya ne. Kasancewar ‘yammata da samari sun haɗu wuri guda a makaranta sai aka riƙa samun shaƙuwa ta soyayya a tsakaninsu, wannan ya sa suka riƙa rubuta irin abin da suke ji na shauƙin soyayya a matsayin labarai.

Bugu da ƙari, samuwar na’urorin ɗab’i da kamfanonin ɗab’in ya taimaka wajen yaɗuwar litttafan soyayya, saɓanin a baya da kowane rubutu sai hukumar NNPC ta tace shi ta kuma aminta da shi kafin ta buga shi.

Kamar yadda finafinan Indiya yawanci ake gina su kan soyayya, sai ya zama waɗannan littattafan ma akan gina su kan soyayya da auren dole da matsalolin gida da dai sauransu.

Rubuce-rubuce na soyayya sun yi tashe ƙwarai a wuraren shekarun 1990, tun daga kan littattafai da wasiƙu tsakanin matasa, musamman ‘yammata da samari.

Duk da cewa an samu zamunnan siyasa mabambanta tun daga 1950 zuwa 1990, za a iya cewa marubuta zube ba su bayar da ƙarfi wajen rubuce-rubuce a kan siyasar ba, maimakon hakan, sun fi karkata ne kan rubuce-rubuce na soyayya, domin ita ce take tashe tsakanin matasa a wancan lokacin. Wannan ya haifar da naƙasu ga lamarin rubutaccen adabi Hausa na siyasa.

4.5.5 Ƙarancin Ilimin Siyasa Ga Matasa

Ilimi shi ne ƙashin bayan ci gaban kowace al’umma, kuma da shi ne ake iya sarrafa tunani domin samun kyautatuwar al’umma. Dukkan abin da za a gudanar matuƙar aka sanya ilimi a cikinsa to za a ga daidai, kuma za a samu nasarar wannan abin.

Ƙarancin ilimi yana daga cikin manyan dalilan da suka haifar da ƙamfar ayyukan rubutaccen zube na siyasa, wannan kuwa ba zai rasa nasaba da ƙyamar da aka nuna wa ilimin zamani tun a farko ba, wanda shi ma ya taimaka wajen samun ƙarancin ayyukan adabi rubutattu, ya kuma sanya rubutaccen adabi na siyasa bai samu tagomashi ba.

Rashin sanin ina siyasar ta dosa da rashin shigar matasa domin a dama da su a cikin harkokin siyasa ya ƙara taimakawa wajen ƙamfar rubutaccen adabin siyasa, domin sai ka san abu kafin ka iya yin rubutu a kansa. Alal Misali, kusan duk ayyukan adabin siyasar da aka samu za a tarar masu ido a kan siyasar suka rubuta su; ko dai ya kasance a cikin jaridu ko jawabai ko wasiƙu ko ƙagaggun labarai ko ma cikin wasanni kwaikwayo ko waƙoƙi. Idan aka ɗauki jaridu, za a tarar cewa dukkan rahotannin da aka kawo a ciki ko wasiƙun da aka buga a cikinsu ‘yan siyasa ne suka rubuto su, wasu ma ’yan jam’iyya ne suke kare jam’iyyunsu. A cikin ƙagaggun labarai kuwa idan aka dubi kamar littafin Tura Ta Kai Bango, 1983 an bayyana cewa marubucin har takara ya yi a jamhuriya ta biyu, amma bai yi nasara ba. Su kuwa marubutan wasannin kwaikwayon Kukan Kurciya, 1993 da Tutar Babu, 2019 sun samu ilimin siyasar ne, domin sun gani kuma a zamaninsu aka yi, duk da cewa ba takara suka yi ba, amma dai sun samu ilimi kan abubuwan da suka faru. Wannan ne ya ba su damar sanya alƙaminsu suka rubuta wasannin daidai da abin da suka ji ko suka gani ko kuma ya faru da su. Don haka rashin sanin abin da ya faru a baya da wanda yake faruwa shi ma ya haifar da ƙamfar rubutaccen adabin siyasa.

4.6 Dangantakar Siyasar Addini da Siyasar Jam’iyya

Kamar yadda aka bayyana a baya, siyasar addini ita ce aka fara samu a ƙasar Hausa kafin wani nau’in siyasa na daban ya samu. Haka kuma, siyasar addini ta samu bayan zuwan addinin Musulunci, sai dai ba ta samu tagomashi a rubuce ba har sai bayan jihadin gyaran halaye da aka gudanar a ƙasar Hausa ƙarƙashin jagorancin Shehu Usmanu Danfodiyo, lokacin da aka samu bunƙasar rubutaccen adabin Hausa daga almajiran Shehu.

Siyasar da aka gudanar lokacin jihadi siyasar Musulunci ne wanda yake tafe da ƙa’idoji da koyarwar addinin Musulunci, kuma an ci gaba da tafiyar da shi har bayan Zuwan Turawa. Za a iya cewa akwai wata dangantaka da za a iya gani tsakanin tsarin siyasun guda biyu, duk da cewa zaman ‘yan marina suka yi wa juna, wato kowa da inda ya fuskanta.

Dagantaka ta farko da za a iya gano a zahiri ita ce, kasancewar ‘yan siyasar farko irin su Malam Sa’adu Zungur sun jiyo ƙamshin ƙarshen ƙarni na sha tara, wannan ya sa siyasar su ta yi tsafta cikin riƙo da gaskiya da riƙon amana tamkar dai yadda aka gudanar da tsarin kafin zuwan Turawa.

Haka kuma kasancewar ilimin Larabci shi ne aka fara samu wanda shi ne ya haifar da hanyar rubutun Ajami, wannan ya sa ko da su Malam Sa’adu Zungur da Mudi Sipikin da irin su Malam Gambo Hawaja Jos da Malam Aminu Kano suka zo, sai ya kasance sun samar da ayyukan adabin siyasa cikin Ajami maimakon cikin boko wanda daga baya suka koya. Alal misali waƙoƙin siyasa da Malam Sa’adu Zungur ya rubuta kamar su “Jihadin Neman Sawaba” da “Arewa Jamhuriya ko Mulukiya” duk da Ajami ya rubuta su, daga baya aka juya su cikin haruffan boko. Hatta a baya bayan nan an samu marubuta adabin siyasa irin su Malam Garba Gashuwa da suka riƙa yin rubutun waƙoƙi cikin Ajami. Alal Misali, waƙar “ Munafurci Karen Ruwa Jam’iyyar A.P.P” da waƙar “’Yan Tagwayen Jam’iyyu SDP da NRC”, duk waƙoƙi ne da aka rubuta su cikin Ajami.

Dukkan abubuwan da aka riƙa amfani da su wajen jawo hankalin al’umma ko dai lokacin yaƙin neman zaɓe ko kuma wurin gudanar da mulki kamar su adalci da tsoron Allah da haƙuri da juriya da yi wa shugabanni biyayya da dai sauransu, abubuwa ne masu alaƙa da addini waɗanda sun samo asali ne tun daga zamanin jihadi, wato zamanin siyasar Musulunci.

Bayan zuwan Turawa, kafin kakkafa jam’iyyun siyasa tsarin da al’ummar ƙasar Hausa suka so a ɗore da shi wajen gudanar shugabanci shi ne tsarin da Musulunci ya tsara, wato ta hanyar ayyana shugaban da ya dace ba ta hanyar kaɗa ƙuri’a ba, wanda kuma zai ci gaba da jagorancin al’umma har mutuwarsa ko kuma lokacin da aka fahimci ya yi raunin da ba zai iya jagorancin ba sai a sake ayyana wani. Wannan yana da dangantaka da siyasar Musulunci wanda bai zo da zaɓe ko kaɗa ƙuri’a ko neman shugabanci ba.

Bayan Turawa sun fito da ‘yan boko, sun fito da tsarin kakkafa ƙungiyoyi waɗanda daga baya suka rikiɗe, suka zama jam’iyyun siyasa, sai ya kasance an riƙa amfani da aƙidun addini wajen gudanar da siyasa, ta yadda ya kasance an samu ɗariƙun Ƙadiriyya da Tijjaniyya sun kasance kamar ma su ne jam’iyyun siyasar ba waɗanda aka kafa kuma aka sani ba. Alal misali, ‘yan Ƙadiriyya an san jam’iyyar da suke, haka ma ‘yan Tijjaniyya an san tasu jam’iyyar. Kasancewar kowace ɗariƙa da Shehunnai da waliyyan da suka yarda da su, kuma suke masu biyayya, wannan ya sa ɗan wata ɗariƙa ba zai yarda ya bi wata ɗariƙa ba (Paden, 1968:312-313­).

Bugu da ƙari, kasancewar a ƙasar Hausa an amince cewa Shehu Usmanu babban malami ne kuma waliyyi, wannan ya sa duk wanda ya danganta kansa da shi ake yi masa kallon na kirki. Wannan dalilin ne ya sa wasu daga cikin ‘yan siyasar farko suka riƙa danganta kansu da shi domin jawo hankalin mabiya da kuma samun ƙarin mabiya a siyasance. Wani ɓangaren kuma wasu ‘yan siyasar sun riƙa danganta kansu da wasu manyan malamai na wasu ɗariƙu domin samun nasara.

Baya ga amfani da rigar addini, irin wannan tsarin ya ci gaba har zuwa yau, inda ‘yan siyasa kan yi la’akari da wasu mutane masu mutunci a idon al’umma ko waɗanda ake girmamawa, sai su riƙa danganta kansu da su a siyasance, ko da kuwa wannan mutumin ba ɗan siyasa ne ba.

Idan aka dubi waɗannan abubuwa da aka kawo za a fahimci cewa, siyasar adddini da siyasar jam’iyya suna da dangantaka tun da farko, kuma idan aka dubi siyasar addini za a iya ganin tasirinta a cikin siyasar jam’iyya, musamman idan aka yi la’akari da wasu abubuwa na addini da suka shigo cikin siyasar jam’iyya, da kuma waɗanda aka ɗauko su aka alaƙanta siyasun biyu da su.

4.6.1 Muhimmancin Ilimi A Cikin Siyasar Jam’iyyu

Kasancewar mafi yawan al’ummar da suke ƙasar Hausa Musulmi ne, wannan ya sa kusan dukkan al’amuransu na rayuwa sukan yi ƙoƙarin ɗora shi yadda zai dace da koyarwar addininsu. Kowane abu da ake gudanarwa a ƙasar Hausa akan ba shi gurbi domin ya samu gindin zama ko da ta hanyar yi masa kwaskwarima ne. Kasancewar tsarin siyasa musamman ta dimokuraɗiyya wadda ta ba da damar zaɓen shugaba ta hanyar gudanar yaƙin neman shugabanci da kuma zaɓe ta hanyar kaɗa ƙuri’a ta saɓa wa koyarwar addinin Musulunci, wannan ya sa da Hausawa suka shiga sai suka yi ƙoƙarin yi wa tsarin kwaskwarima. Wato dai irin abin da masu hikimar magana kan ce: ‘Da baƙi ƙirin, gara baƙi-baƙi.’

Idan aka dubi ‘yan siyasar farko-farko za a ga cewa yawancinsu suna da ilimin addini. Alal Misali, mutane irin su Malam Sa’adu Zungur da Malam Aminu Kano da Mudi Sipikin duk sun samu ilimin addini daidai gwargwado, wasu daga cikinsu ma sun haddace Alƙu’ani mai girma tun suna da ƙarancin shekaru. Wannan ya sa suke ƙarfafa cewa duk wanda zai jagoranci al’umma to wajibi ne ya zama ya fahimci ilimin addini, domin shi ne zai yi masa jagora a cikin sha’anin shugabanci ko jagorancin al’umma. Dubi abin da Malam Aminu Kano ya faɗa a cikin wani jawabi nasa:

 “ Shin kun ma san ma’anar kalmar Sarki? Sarki fa ba yana nufin mai rawani ne kaɗai ba. A’a, yana nufin shugaban muminai ne. Wannan yana nufin kowane sarki a ƙasarsa shi ne limami. Shin kun taɓa tunanin dalilin da ya sa Shehu ya bai wa Sulaimanu da Yakubu da Ummarun Dallaji tuta su je su shugabanci Kano da Bauchi da Katsina? To ya ba su ne don su je su zama shugabannin addini (saboda iliminsu), kuma hakan aka yi. Babu wanda zai ce shi liman ne kuma ya kasance ba shi da ilimin addini. Don haka a Musulunce jahili ba zai yi shugabanci ba Saboda haka shugabanni na ƙwarai suna da ilimin addini wanda ke yi masu jagora wajen sauke nauyin da addinin ya ɗora masu

(Paden, 1968:281).

A nan Malam Aminu Kano yana nuna muhimmancin nagartar shugaba ne ta fuskar ilimi. Bayaninsa ya nuna cewa, kowane shugaba wajibi ya kasance mai ilimin addini, wannan zai taimaka masa wajen kasancewa mai tsoron Allah wajen gudanar da al’amuran shugabancin da aka ɗora masa. Ya ba da misali da sarakuna shugabannin al’umma waɗanda Shehu Usmanu Danfodiyo ya ba su tutoci zuwa yankunan ƙasar Hausa, inda ya nuna cewa kowanne daga ciki almajirin Shehu ne, kuma babban malami ne masani, wanda zai kasance a cikin al’ummarsa shugaba, jagora, malami, alƙali kuma limamin gari. Ilimi kodayaushe yana yi wa mai shi jagora ne zuwa ga aikata daidai, da kuma yin hani da horo a duk inda suka kamata. Ta fuskar gadon sarauta da zaɓen ‘ya’yan sarakuna a cikin tsarin siyasa kuwa, Malam Aminu Kano ya nuna muhimmancin ilimi ga duk wanda za a naɗa sarki ko kuma a zaɓe shi wani muƙamin siyasa, inda a cikin jawabin nasa ya ci gaba da cewa:

Idan ya kasance ɗan sarki ba shi da ilimin Muhammadiyya to ya ja baya. In kuma akwai wanda a cikinmu zai iya kafa hujjar inda Allah ya faɗa ko Manzonsa ya faɗa a cikin hadisi inda ya halatta jahili ya jagoranci al’ummar Musulmi to muna sauraronsa

(Paden, 1968:282-283).

A nan yana magana ne kan tsarin gado na sarauta, inda yake nuna cewa babu wannan tsarin a Musulunci. In kuwa har ya kasance wani ɗa zai gaji mahaifinsa, to wajibi ne ya kasance ya yi karatu, kuma yana da ilimi kafin a ba shi. In kuwa ba shi da shi to sai dai a zaɓo wani a damƙa masa ragamar shugabancin ko da kuwa ba shi da gadonta. A tsarin siyasar jamhuriya ta farko, mafi yawa daga cikin masu riƙe da muƙaman siyasa musamman na jam’iyyar NPC, daga sarakuna sai ‘ya’yansu(Dudley, 1968:73). Wannan ya sa ‘yan hamayya suka riƙa sukar su ta wannan fuska, inda suke ganin cewa a tsarin gargajiya ma addini shi ne ya kamata ya zama jagora ga shugabanni, don haka a tsarin siyasar jam’iyya ma wajibi ne duk shugaban da za a naɗa ko a zaɓa ya kasance mai ilimi. Ke nan ilimi shi ne abu mafi muhimmanci wajen zaɓen shugaban da zai jagoranci al’umma.

Malam Sa’adu Zungur ya kawo irin wannan hujjar inda yake cewa, ilimin addini shi ne ginshiƙin shugabancin al’umma, inda a cikin waƙar Arewa Jamhuriya ko Mulukiya ya nuna cewa, maimakon a rushe tsarin tafiyar da mulki ƙarƙashin sarakuna ya kamata a yi wa tsarin gyaran fuska ne.

Irin wannan na muhimmancin ilimi a cikin siyasa ya ci gaba da bayyana a cikin ayyukan rubutaccen zube kamar yadda ya fito a cikin littafin Tura Ta Kai Bango, inda aka nuna cewa babu ma waɗanda ya kamata su shiga siyasa kamar malamai, domin kuwa su ne suke iya tantance fari da baƙi, kuma suna iya nusar da al’umma inda ya kamata ta dosa. Dubi abin da marubucin yake cewa:

“Na ga kana hanyar makaranta. Ina malamai ina shiga siyasa?”

“Malamai kuwa ai su ya kamata su yi siyasa. Suna da ilimi, don haka suna iya nuna wa mutanen kirki. Ai zuwana kamar da ƙasa.”

(Katsina, 1983: 3)

Muhimmancin ilimi ga al’umma tamkar makaho ne da ɗan jagora, ma’ana, duk wanda ya samu ilimi ba za a same shi yana tafiya ido rufe ba. Don haka waɗanda suka samu ilimi suna zama tamkar fitila ga al’umma waɗanda suke haska masu hanya don kada su faɗa inda bai kamata su afka ba. Shi ilimi fitila ne mai haske. Kamar dai yadda fitila kan haske ɗaki ko wani wuri mai duhu haka ma ilimi musamman na addini yakan haske duniya, ya daidaita al’amura wanda ya shafi jagorancin al’umma. A cikin ilimin addini ne ake samun tsoron Allah da adalci da sauran kyawawan ɗabi’u. Wannan ne ma ya sa ko a cikin siyasar aka bai wa ilimin addini muhimmanci domin samun kyakkyawan shugabanci. Ashe ke nan babu waɗanda suka dace su jagoranci al’umma kamar masu ilimin cikinta.

Duk da muhimmancin da ilimin addini yake da shi a cikin tsarin shugabanci, daga baya an yi wa wannan tsarin siyasa ta Arewacin Nijeriya riƙon sakainar kashi, ta yadda aka sanya a cikin kundin tsarin mulkin ƙasa cewa, babu wanda zai iya tsayawa takara a mataki kaza a zaɓe shi komai ilmin addininsa har sai ya mallaki shaidar kammala karatun boko a ƙalla na firamare, ya danganta da matakin da mutum zai yi takara a cikinsa. Wannan ya sa darajar ilimin addini a cikin siyasa ta fara komawa baya ana bai wa ilimin zamani muhimmanci. Dubi abin da marubucin littafin Da Bazarku yake cewa:

“ Mene ne dalilin da ya sa cikin kundin tsarin mulkin ƙasar nan za a sharɗanta cewa sai wanda ya yi karatun boko mai mataki kaza ne kawai kawai zai tsaya takara iri kaza, ko da kuwa shi hafizin Alƙur’ani mai girma ne kuma ya iya rubutu da karatu da larabci. Sannan kuma shi ne ya fi kowa cancanta saboda amanarsa, mutuncinsa, jama’arsa, gaskiyarsa da dai sauransu. Idan dai har bai yi bokon ba to ala tilas sai dai a ɗauki shin-mai-ruwa-uku a ɗora a kan wannan matsayin.”

(Surajo,2006:97)

A nan marubucin yana nuna takaicinsa ne kan yadda aka wofintar da ilimin addini a cikin siyasa, inda ake ganin in dai ba ka yi ilimin boko ba, to komai tumbatsar ka a cikin ilimin addini matuƙar ba ka da takardar shaida to ba za a amince da kai a zaɓe ka ba. Marubucin ya nunar da cewa akwai waɗanda malamai ne na addini mahaddata Alƙur’ani mai girma, kuma an yarda da mutunci da gaskiya da riƙon amanarsu a cikin al’umma, amma saboda ba su da ilimin boko sai a ɗauki muƙamin siyasa a bai wa waɗanda ba su cancanta ba maimakon su.

Ire-iren waɗannan misalai sun yi ta bayyana a cikin tarihin siyasar Nijeriya musamman a ƙasar Hausa, wanda a zamanin da ake ciki yanzu ma kusan ba a bai wa ilimin addinin muhimmanci kwata-kwata in dai a kan abin da ya shafi zaɓen ‘yan takara ne ko kuma naɗin muƙamai. Ko da kuwa muƙamin kwamishinan addinin Musulunci ko mai ba da shawara kan addinin Musulunci sai wanda yake da takardar kammala karatun zamani za a ba shi[4].

4.6.2 Aƙidu Da Matsayinsu A Fagen Siyasar Jam’iyyu

 Tun farkon siyasar Jam’iyyu a ƙasar Hausa an yi ta samun sa-toka-sa-katsi tsakanin manyan aƙidun Musulunci na wannan yanki na ƙasar Hausa. Ɓullowar jam’iyyun ya zo da wani sabon abu a cikin siyasar wannan yanki duk da cewa da ma akwai bambance-bambance na fahimta a tsakanin ɗariƙar Tijjaniyya da kuma ta Ƙadiriyya musamman ta fuskar waliyyansu.

Haka ma a cikin ɗariƙar ta Tijjaniyya akwai bambancin fahimta tsakanin ‘yan sadalu wato mabiya Shehu Umaru Futi da kuma ‘yan ƙabalu mabiya Shehu Ibrahim Inyasss. Waɗannan bambance-bambance sun yaɗu ƙwarai a ƙasar Hausa. Alal Misali, a lardin Zazzau inda wuraren shekarar 1950 Sarkin Zazzau Jafaru wanda Batijjane ne, ɗan ‘Sadalu’, ya yi adawa ƙwarai da ‘yan ‘ƙabalu’ mabiya Ibrahim Inyasss, har ya kai ga bayar da umarnin cewa duk wani ɗan ƙabalu ba zai yi limancin Juma’a ba(Paden, 1973: 122). Waɗannan bambance-bambance a cikin aƙidu sun taka muhimmiyar rawa a cikin siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa.

Kasancewar a kowane lardi na ƙasar Hausa akwai ɗariƙar da ta fi samun karɓuwa da yawan mabiya, wannan ya taimaka wa shugabannin siyasar wannan lokacin yin amfani da ɗariƙunsu wajen neman goyon bayan jama’a da kuma ƙarfafa hamayya tsakaninsu da wasu jam’iyyu. Alal misali, lardin Sakkwato inda nan ne cibiyar daular Usmaniyya, ɗariƙar Ƙadiriyya ce ta fi ƙarfi, saɓanin lardin Kano da mafiya yawansu mabiya ɗariƙar Tijjaniyya ne. Wannan dalilin ya sanya ko da aka samu ɓullar siyasar jam’iyyu, sai ya kasance mafi yawa na magoya bayan manyan jam’iyyu biyu na Arewacin Nijeriya, wato NEPU da NPC, suka kasance ‘yan Tijjaniyya ne da Ƙadiriyya, wato Tijjaniyya a Kano, Ƙadiriyya kuma a Sakkwato. Da irin wannan tsarin aka faro siyasar jam’iyyu a Arewacin Nijeriya[5].

An riƙa samun rikice-rikice tsakanin mabiya ɗariƙun biyu inda a wasu lokuta har akan samu hasarar rayuka da dukiya. Alal misali, an bayyana cewa akwai lokacin da sarkin Musulmi ya ba da umarni aka rushe masallatan ‘yan Tijjaniyya da dama a lardin Sakkwato, wanda hakan ya jawo masa zage-zage daga mabiya Tijjaniyya a cikin waƙoƙinsu, saboda nuna hamayya da yake da su. An kuma samu rikici tsakanin ‘yan Ƙadiriyya da Tijjaniyya a lardin na Sakkwato, kasancewar Sarkin Musulmi shi ne yake da alhakin naɗa limamai, sai ya riƙa naɗa ‘yan Ƙadiriyya a limanci. Wannan ya sa aka riƙa samun ta-da-ƙayar baya daga mabiya Tijjaniyya na Zamfara, wanda a wuraren shekarun 1950 rikici ya ɓarke a aƙidun biyu, har ya haifar da kisan wani limamin Ƙadiriyya a Zamfara (Scott, 1952: 2).

Irin wannan ya bayyana a cikin jaridar Daily Mail, inda aka bayyana irin wannan rikici tsakanin aƙidu kamar haka:

 “Mutane huɗu sun rasa rayukansu wasu da dama kuma sun samu raunuka sakamakon hatsaniyar da aka samu a Sakkwato makon da ya gabata. Rikicin da ya ɓarke tsakanin mabiya ɗariƙu, wanda ya fi tsanani shi ne wanda aka samu Issa da Zurmi da ke lardin Sakkwato. Wannan rikici ya ɓarke ne tsakanin mabiya Tijjaniyya da na ƙadiriyya. Rikicin farko ya tashi ne a Gidan Maizare wanda aka rasa rayukan mutum huɗu rikicin ya ɓarke ne sakamakon ‘yan Tijjaniyya da suka hana ‘yan Ƙadiriyya gudanar da sallar la’asar a garin Jangero An kama mutane da dama da suke da hannu cikin rikicin.”

(“Mutane Huɗu sun Rasa Rayukansu”, 1956)

Idan aka dubi irin waɗannan rikice-rikice za a ga cewa suna da alaƙa da siyasa ƙwarai da gaske duba da yadda aƙidu a addini suka yi tasiri ƙwarai a cikin siyasar jam’iyyu a farko. Rikicin siyasa tsakanin jam’iyyu ba sabon abu ba ne a wancan lokacin, sannan kuma jam’iyyun siyasa a ƙasar Hausa a wancan lokacin an danganta su da wasu aƙidun addini wanda kusan duk wanda yake cikin jam’iyya kaza an san ɗan wace aƙida ce. Kasancewar Sakkwato nan ne tushen Ƙadiriyya a ƙasar Hausa, wannan ya sa duk limamin da sarkin Musulmin zai naɗa a ƙasar Sakkwato zai naɗa ɗan Ƙadiriyya ne wadda ake dangantawa da jam’iyyar NPC a wancan lokaci. Su kuwa ‘yan hamayya na jam’iyyar NEPU waɗanda yawancinsu ko ma baki ɗayansu ‘yan Tijjaniyya ne sai suke ganin ba a yi masu adalci ba, domin akwai saɓanin fahimtar addini a tsakanin. Wannan abin da ya faru ya sanya jam’iyyar hamayya ta NEPU a wancan lokacin ta shirya wata muhawara wadda za ta gudana a birnin Landan, domin tattauna batun ‘yancin gudanar da addini a Arewacin Nijeriya. Kuma don nuna goyon baya ga waɗanda aka kama aka tsare sakamakon wannan rikici, matasan NEPU da dama sun tafi Sakkwato a matsayin mabiyan Tijjaniyya domin nuna fushinsu kan tsare matasan Tijjaniyya a can.

Wasu suna ganin cewa ainihi idan aka yi maganar aƙida to ana nufin Musulunci ne baki ɗaya, duk kuwa wanda ba shi da aƙida to ba Musulmi ba ne. Idan aka ɗauki wannan fahimtar, za a ga cewa a cikin siyasar jam’iyyu musamman siyasar jamhuriya ta farko kowace jam’iyya tana iƙirarin ita ce jam’iyyar Musulunci, duk wadda ba ita ba ta kafirai ce. A kan wannan aƙidar aka gina siyasar ƙasar Hausa a wancan lokaci. Dubi wannan misalin:

“ ya jawo hankalin duk mai hankali na Arewa da Najeriya su rungumi NPC hannu bibbiyu don ita ce zata tabbatar mana addininmu na Musulunci ta kuma ƙyale masu bin wata hanya su ta bin abarsu da kuma ƙarfafa sarakunanmu na addini ”

(“A. G. Na Maganin Mutuwa A Arewa”, 1959).

Idan aka dubi wannan misalin za a ga cewa, kira ake yi ga jama’a a kan su rungumi jam’iyyar NPC don ita ce za ta tabbatar da addinin Musulunci, saɓanin sauran jam’iyyu da ba za su kula da addinin ba. Haka kuma idan aka lura a cikin misalin ana nuna cewa za a bar duk wani mai aƙida ya yi aƙidarsa ba tare da an hana shi ba, sannan kuma za a ƙarfafa sarakunan gargajiya waɗanda ya kira su da sarakunan addini don dai nuna cewa aƙida da siyasa fa ba a raba su.

An sake samun wani rikicin tsakanin ‘yan Tijjaniyya da ‘yan Ƙadiriyya a lardin Sakkwato wanda aka bayyana cewa har ‘yan doka goma sha ɗaya aka kashe yayin kwantar da tarzoma. Dubi labarin da jaridar Daily Express ta buga ranar 2 ga Afrilu 1965:

“ the disturbance broke out in Yeldu District between Tijaniyya and Kadiriyya suppoters in Toranke, Jankuka, and Jaja, a group of villages 60 miles North-East of Argungu.”

Fassarar marubuci:

“ hatsaniya ta ɓarke a ƙasar Yeldu tsakanin magoya bayan Tijjaniyya da na Ƙadiriyya a Toranke da Jankuka da Jaja, wasu rukunin ƙauyuka kimanin mil 60 Arewa Maso Gabas da Argungu.”

(Paden,1973: 122).

 A cikin wannan rikicin da aka samu tsakanin mabiya aƙidun biyu, shi ma yana da alaƙa da siyasa ƙwarai da gaske domin kuwa jaridar Morning Post ta ruwaito cewa:

“The Sultan of Sakkwato later denied that the riot was between Qadiriyya and Tijaniya, throughout the country and more especially in big towns, live amicably without interference in each other’s religious belief. He referred to the rioters as ‘Yan Wazifa’ who are going beyond their bounds to them even prayer five time a day was forbidden.”

Fassara:

“Sarkin Musulmi ya ƙaryata batun rikicin da ya faru tsakanin Tijjaniyya da Ƙadiriyya, waɗanda suke zaune lafiya a duk faɗin ƙasar musamman ma a manyan garuruwa, inda ya bayyana cewa waɗansu masu neman wuce gona da iri ne; masu cewa sallah biyar a wuni haramun ne, waɗanda ake kira ‘yan wazifa suka tayar da rikicin.”

(Paden,1973: 122)

Idan aka dubi misalin da yake sama za a ga cewa siyasa ce a ciki domin kuwa wanda ya yi maganar Baƙadire ne duk da cewa kai tsaye ba a ayyana shi a matsayin ɗan Jam’iyyar siyasa ba, amma dai yana goyon bayan gwamnati mai mulki na lokacin wadda ta jam’iyyar NPC ce. Kalmar ”Yan wazifa” kuma tana nufin ‘yan Tijjaniyya, kalma ce ta wulaƙanci da ake faɗa wa ‘yan ƙabalu na wasu ƙauyuka a wajen lardin Kano, kamar yadda Paden (1973: 199) ya bayyana. ‘Yan Wazifa su ma ‘yan Tijjaniyya ne, bambancinsu shi ne, su waɗanda aka kira ‘Yan Wazifa su ne ‘Yan Faila, masu tafiya suna zikiri, mabiya Shehu Ibrahim Inyass. Su kuma ɗayan ɓangaren ‘yan Tijjaniyyar da ba su ba, su ne mabiya ɗariƙar Shehu Umaru Futy. A nan ya nuna cewa ‘yan Tijjaniyya ne (NEPU) suka tayar da rikici ba ‘yan Ƙadiriyya (NPC) ba.

Irin wannan dangantaka tsakanin aƙidun Musulunci da siyasa ya ci gaba da bayyana a cikin rubutaccen zube, inda aka riƙa nuna muhimmancin aƙida a cikin siyasa, wanda hakan yake sa dagantaka ta yi daɗi idan ‘yan siyasa biyu suka zama mabiya aƙida guda, ko kuma a samu akasin haka idan ya kasance an samu bambancin aƙidar addini. Wani lokaci akan samu ‘yan siyasa biyu a jam’iyya guda masu mabambantan aƙidun addini, sai dai abu kaɗan zai iya gittawa da ya shafi aƙidar ya ɓata alaƙa a tsaninsu, kasancewar aƙida a addini abu ne da aka ɗauke shi da muhimmancin gaske, domin ya shafi imanin mutum ne baki ɗaya. Dangantakar Sardauna da Sarkin Kano ta yi tsami wanda har ya kai ga an cire shi daga sarauta domin bambancin aƙida, kasancewar Sarkin Kano mabiyin ɗariƙar Tijjaniyya ne kuma makusancin Shehu Ibrahim Inyasss, wannan ya haifar da rashin fahimta tsakaninsa da Firimiyan Jihar Arewa wanda ya kai ga cire sarki Muhammadu Sanusi daga sarauta duk kuwa da kusancin da suke da shi. Dubi abin da awolowo ya faɗa a cikin wani rahoto:

“ kafin a sanya dokar ta-ɓaci a jihar Yamma an sanar da ni cewa dangantaka ta yi tsami tsakanin Sarkin Kano wanda yake ɗan Tijjaniyya ne da kuma Sardaunan Sakkwato wanda ba ɗan wannan aƙidar ba ne.”

(Paden, 1973 : 311)

Wannan yana nuna irin yadda aƙidu suke da muhimmanci musamman a siyasar jamhuriya ta farko. Daga abin da aka gani cikin misalan da suke sama za a fahimci cewa, abin da ya haifar da tsamin dangantakar ba wai bambancin jam’iyya ba ne, domin jam’iyya guda suke wato NPC, amma aƙidun da suke a cikin addinin Musulunci daban-daban ne, wato Sardauna ɗan Ƙadiriyya ne, shi kuwa Sarkin Kano Muhammadu Sanusi ɗan Tijjaniyya. An bayyana cewa, ziyarar da Shehu Ibrahim Inyasss ya kawo Nijeriya a shekarar 1962 zuwa Kano da kuma ziyarar Sardauna zuwa Kano a rana guda su ne suka rura wutar rikicin da haifar da tsamin dangantakar da ta yi sanadiyyar cire sarkin daga kujerarsa. An nuna cewa, maimakon Sarkin Kano ya je ya taro Sardauna (Baƙadire) sai ya tafi wurin Shaihinsa Ibrahim Inyasss(Batijjane)[6]. Idan aka dubi waɗannan bayanan za a yarda cewa lallai aƙidar addini ta taka muhimmiyar rawa a cikin siyasar Nijeriya.

Mabiya aƙidun addini sun ci gaba da bayyana matasayarsu a cikin tarihin siyasar jam’iyyu, inda wasu sukan fito da sunan wata aƙida su nuna ɗan takarar da suke goya wa baya, ko kuma su yi kira da a goya wa wannan ɗan takarar baya. A wasu lokutan wasu ba su amfani da sunan jam’iyyar da suke goya wa baya, sai dai su dubi ɗan takara da suka natsu da shi, sai su yi kira da a goya masa baya. Irin haka ya faru a jamhuriyar da ake ciki wato jamhuriya ta huɗu, inda malamai daga mabambantan aƙidu suka yi kira ga mabiyansu kan wanda ya kamata su zaɓa. Alal misali, ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Iƙamatis Sunnah wadda aka fi sani da Izala ta goya wa tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari baya a lokacin zaɓen 2019, kamar yadda ya bayyana a cikin jaridar Daily Nigerian:

“Fitacciyar ƙungiyar Addinin Musulunci ta Nijeriya wadda ke da rassa a ƙasashen Nijar da Kamaru ta yi kira ga mabiyanta da su zaɓi shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a zaɓen da shugaban ƙasa da za a yi nan gaba a wata mai kamawa.”

(Jafar, 2019).

Idan aka dubi wannan misali za a ga cewa wannan umarni ne na daga ƙungiyar masu aƙidar Izala zuwa ga mabiyanta a kan su zaɓi wani ɗan takara na wata jam’iyyar siyasa. Duk da cewa ba lallai ne kowane mabiyin aƙidar ya karɓi wannan kira ya kuma zaɓi ɗan takarar da suka ayyana ba, amma dai za a samu wasu kaso da za su bi wanda shugabancin aƙidarsu ta addini ta ayyana masu, kuma wannan yana nuni ne ga irin tasirin da aƙidun addini suke da shi a cikin siyasar jam’iyyu. Har ila yau, akan samu inda mabiya wasu aƙidun da suke da saɓanin fahimta da Izala su ma su ce ba za a zaɓi ɗan takarar da suka ayyana ba, domin nuna ɗan takarar da ƙungiyar ta yi ya nuna cewa yana tare da wannan aƙidar ke nan. Don haka su kuma ba za su zaɓe shi ba. Ga misali:

“Shahararren malamin addinin Musulunci kuma shugaba Darikatul Tijjaniya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya yi kira ga mutanen yankin Bogoro/Dass/da Tafawa Balewa a jihar Bauchi da su zabi kakakin majalisan wakilai, Yakubu Dogara. Ya bayyana hakan ne yayin da kakakin ya kaiwa babban malamin ziyara gidansa inda yayi kira ga jama'a kada su zabi malaman da suke amfani da addini wajen raba kan al'umma. Ya ce Yakubu Dogara bai nuna bangarancin addini, yana son zaman lafiya, kuma ya cancanci ya wakilci jama'a domin cigaba da ayyukan kwarai da yakeyi.”

(Mudathir, 2019).

Duk da cewa a cikin wannan misalin malamin bai kama sunan wata aƙida kai tsaye ba, amma ya yi ishara da cewa kada a zaɓi malaman da suke amfani da addini wajen raba kan al’umma, wanda wannan fitacciyar shaida ce da wasu aƙidun Musulunci suke yi wa masu aƙidar Izala. Bugu da ƙari, kasancewar Yakubu Dogara Kirista ne, shi kuwa abokin takararsa a lokacin, Sheikh Ɗalhatu Abubakar Hakimi, malami ne mabiyin aƙidar Izala, kuma shaihin na ɗariƙar Tijjaniyya ya goyi bayan a zaɓi Kiristan maimakon Musulmi ɗan Izala, har ma ya yi kira ga mabiyansa. Wannan ya sa ake ganin cewa bambancin aƙidarsa ta Tijjaniyya da Izala ce ta haifar da hakan. Ke nan, wannan ma wani tasiri ne na aƙidun addini a cikin siyasa da za a iya gani a fili, wanda kuma za a iya alaƙanta shi da irin rashin jituwar da aka yi ta samu tun farkon samuwar siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa a wuraren shekarun 1950.

Idan aka dubi dukkan bayanan da aka kawo a sama za a fahimci cewa, tun farkon siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa aƙidun addini sun riƙa taka muhimmiyar rawa a cikinta. Haka kuma tasirin waɗannan aƙidun a cikin siyasar ya taimaka wajen ɗorewar siyasa a cikin tsawon zamani, domin ya samar da wani salon hamayyar siyasa mai ɗauke da ruhin addini. Haka kuma siyasa ba ta kasancewa sai da hamayya, domin shi ne sinadarinta.

4.6.3 Danganta ‘Yan Siyasa Da Masu Mulki Da Manyan Madogaran Addinin Musulunci

A cikin tarihin siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa masu mulki da ‘yan siyasa sun riƙa danganta kansu da manyan turaku na addinin Musulunci wajen cim ma manufofinsu na siyasa. Kamar yadda aka sani ne, babu wani mutum a cikin al’umma wanda zai so a danganta shi da wani abu na banza ko kuma mutanen banza, kowa yana so a yabe shi, kuma a danganta shi da abin ƙwarai ko mutanen kirki. Wannan ya sa ‘yan siyasa a kodayaushe sukan riƙa danganta kansu, ko neman kusanci da wasu abubuwa masu ƙima da daraja a idon mutane, da kuma danganta kansu da mutanen da suke ganin masu ƙima ne a idon al’umma.

Alƙur’ani shi ne babban littafin da kowane Musulmi yake taƙama da shi, littafi ne mai daraja da ƙima a idon kowanne Musulmi, domin shi ne litafin shari’ar Musulunci da Allah ya saukar wa Annabi Muhammadu (S.A.W) zuwa ga mutane. Kowane Musulmi yana girmama Alƙu’ani kuma yana tattalinsa, ba ya kuma ƙaunar ganin ko yaya an wulaƙanta shi, domin wulaƙanta shi wulaƙanta addinin Musulunci ne. Wannan ya sa idan aka ce Alƙur’ani shi ne babban madogaran addinin Musulunci to ba a yi kuskure ba. Baya ga Alƙur’ani wanda yake maganar Allah ne kai tsaye, babu wani kuma wani abu da Musulmi suke girmamawa kamar maganganu da ayyukan Annabi (S.A.W.) waɗanda aka tattara su cikin hadisansa. Waɗannan su ne manyan madogaran kowane Musulmi wajen gudananar da addini, kuma duk yadda aka wulaƙanta su dole zuciyar kowane Musulmi ta sosu.

A zamanin siyasar jamhuriya ta ɗaya, an samu lokacin da shugaban jam’iyyar AG wato Awolowo ya gudanar da yaƙin neman zaɓe inda ya riƙa watso takardu da suka shafi manufofin siyasarsa. Magoya bayan wasu jam’iyyu a Arewa sun soki wannan tsari nasa, inda suka ce a cikin wannan takardar da ake watsowa daga jirgin sama akwai ayoyin Alƙur’ani da hadisai a ciki. Dubi abin da jaridar Sodangi ta buga:

“Mun sami wani labari daga Alhaji Salihu Durumin Iya cewa yana so mutane su gane kuskuren shugaban jam’iyyar AG Awolowo da yake watso wasu takardu daga jirgin samansa cikin takardun da yake watsowa akwai masu ayoyin alƙur’ani da kuma hadisai wannan wulaƙanta ayoyin Alƙur’ani da hadisai ne wannan ta’adda da awolowo ya yi ta ɓata wa Musulmi rai ƙwarai da gaske don haka ba Awolowo ba ko Dujal ne muka ga yana wulaƙanta addini sai mun nuna masa kuskurensa muna roƙon kada kowa ya ya yarda ya zaɓi AG jam’iyyar Awolowo”

(“Kuskuren Awolowo”, 1959).

A cikin jaridar an nuna cewa, Awolowo ya tafka babban kuskure, ta hanyar watso takardun da suke ɗauke da ayoyin Alƙur’ani da hadisai. ‘Yan hamayya sun ce wannan cin mutuncin addinin Musulunci ne, kasancewar mafi yawan al’ummar yankin Arewa Musulmai ne, wannan ya sa suka nuna fushinsu ƙwarai da gaske. A cikin jaridar sun bayyana cewa ba awolowo ba, ko Dujal ne ya tafka irin wannan ɗanyen aikin sai sun nuna masa kuskurensa, kuma suka yi kira da cewa kada jama’a su kuskura su zaɓi jam’iyyar AG ta Awolowo.

Idan aka duba za a ga cewa, an danganta wasu manyan madogaran addinin Musulunci ne da siyasa. Da ma jam’iyyun siyasar Arewa suna kallon jam’iyyar AG a matsayin ‘yar hana ruwa gudu ce, domin tana ta ƙoƙarin kiran mutane su bi jam’iyyarta wanda hakan zai raunata sauran jam’iyyun Arewa ta hanyar rage masu magoya baya. Samun wannan kuskuren na Awolowo tamkar sara ne a kan gaɓa, domin sun siyasantar da abin, suka kuma nuna cewa ya ci mutuncin addini kasancewarsa ba Musulmi ba don haka kada a zaɓi jam’iyyarsa.

Haka kuma, irin mutanen da za a iya kiransu da madogaran addini da ‘yan siyasa sukan danganta kansu da su sukan kasance ba ‘yan siyasa ba ne, suna dai da alaƙa ta kusa da al’umma ta fuskar zamantakewa ko aƙida ko kuma ma addinin Musulunci baki ɗayansa. Wasu sukan kasance malaman addini ne waɗanda ake ganin girmansu da ƙimarsu da kuma darajarsu, a wasu lokutan ma wasu akan ɗauke su a matsayin waliyyai ne, domin mabiyansu suna ganin cewa sun kai wannan matsayin duba da irin ɗimbin iliminsu, da tawali’unsu da gudun duniya da tsantsainin da suke da shi, wannan ya sa ake ganin suna da kusanci da Allah, wanda ya sa ake ganin girma da ƙimarsu a cikin al’umma. A wasu lokutan ma akan samu waɗanda kan danganta kansu da tsatson Annabawa. Irin waɗannan mutane kowa zai so a ce yana da kusanci da su, kasancewar su bayin Allah ne mutanen kirki. Irin wannan ya fito a cikin tarihin siyasar ƙasar Hausa, domin kuwa Paden, (1973: 310) ya bayyana cewa:

“A lokacin zaɓen 1961 ‘yan siyasa da dama sun riƙa ƙoƙarin yin amfani da biyayyar da mabiya wasu aƙidu na addini suke wa shugabanninsu domin samun goyon baya. Irin wannan yanayi ya ƙaru a cikin shekarun 1961 zuwa 1964.”

Masanin ya nuna, ‘yan siyasa sun yi amfani da biyayyar da mabiya wasu aƙidu ko ɗariƙu suke yi wa malamai ko shugabanninsu wajen neman goyon bayan al’umma, musamman daga shekarun 1960 zuwa 1964 kamar yadda ya bayyana. Ba daga nan kawai abin ya tsaya ba, an ci gaba da amfani da irin wannan hanyar a cikin siyasar ƙasar Hausa, inda irin wannan ya fito a cikin ayyukan rubutaccen zube na Hausa.

Tarihi ya nuna cewa, manya kuma fitattun ‘yan siyasa a jamhuriya ta farko sun bi irin waɗannan hanyoyin domin samun goyon bayan al’umma domin samun nasara a zaɓuɓɓuka. Ba samun nasarar ko rashinta ne abin da wannan batu ya karkata a kai ba, an dubi irin yadda akan ƙulla alaƙar ce domin duniya ta gani, kuma domin masoya ko mabiyan waɗannan muhimman mutane su yarda, su kuma aminta da wanda suka gani tare da mutumin da suke girmamawa. Alal misali, a jamhuriya ta farko an samu wani rahoto da jaridar Daily Comet ta ruwaito a kan ziyarar da shugaban NEPU Malam Aminu Kano da wasu manyan ‘yan jam’iyyar suka kai wa Shaihin Malamin nan kuma jagorar ɗariƙar Tijjaniyya na Afirka, Shehu Ibrahim Inyasss kamar haka:

“Babban shugaba kuma jagoran NEPU, Alhaji Aminu Kano ya bar Ikko a jirgin sama zuwa Senegal domin ziyara ta kwanaki bakwai ga babban Malamin addinin Musuluncin nan Shaikh Ibrahim Niass a Kaulaha. A cikin tawagar akwai muhimman mutane biyar da suka masa rakiya, waɗanda suka hada da: Babban sakataren NEPU, Abubakar Zukogi, uban jam’iyyar NEPU na kasa kuma wakili a majalisar wakilai ta Arewa, Alhaji Salihu Nakande, da mataimakin ma’ajin jam’iyya na kasa Alhaji Ahmadu Trader, da kuma Alhaji Sharif Ali fitaccen malami mai wa’azi a lardin Sakkwato. A ziyarar da za su je Kaulaha, Malam Aminu da ‘yan rakiyarsa za su gana da Shaikh Ibrahim Kaulaha tare da gudanar da wasu ayyukan ibada tare da shi.”

(“Aminu Kano da Tawagarsa”, 1964).

Duk da cewa Malam Aminu Kano mabiyin ɗariƙar Tijjaniyya ne, amma idan aka duba za a ga akwai siyasa cikin ziyarar, domin kuwa ko daga abokan rakiyar tasa wato shugabannin jam’iyyar NEPU za a fahimci haka. Haka kuma, ko daga yadda aka buga labarin aka kuma watsa shi, an yi ne don mabiya Shehu su san cewa manyan jagororin NEPU fa sun ziyarce shi, ko ba komai za su ƙara samun gamsuwa da sallamawa ga jam’iyyar da shugabanninta suka ziyarci shaihinsu. Ziyarar za ta ƙara wa jam’iyyar NEPU farin jini a wajen mabiya ɗariƙar Tijjaniyya, sannan za ta ƙara mata yawan magoya baya. Ke nan, idan aka duba a nan an yi amfani da darajar Shehu Ibrahim Inyasss wajen ƙara wa jam’iyyar NEPU da shugabanninta da kuma ‘yan takararta magoya baya.

Ba jam’iyyar NEPU kaɗai ce ta yi amfani da wannan salon ba, wasu jam’iyyu ma sun yi amfani da shi da manufar samun goyon bayan jama’a domin samun nasarar jam’iyyarsu a wurin zaɓe. Wani ƙarin misali shi ne, yadda jam’iyyar AG ta yi amfani da wasu ‘ya’yanta domin kai wa Shehu Ibrahim Inyasss ziyara domin samun tubarraki. Ga misalin:

“A ƙoƙarin Obafemi Awolowo na jam’iyyar AG da Ibrahim Imam na samun goyon bayan Ibrahim Niass a zaɓen 1961, an tattauna batun a cikin shari’ar Awolowo a 1962 A shaidar da Ibrahim Imam ya bayar ya ce, ‘ na ziyarci Senegal har sau biyu na ziyarci Shehu Ibrahim Inyass a Kaulaha a 1956, sannan kuma lokacin da ni da wasu muka raka ka wata ziyara a Ghana a 1961 mun haɗu da shi (Ibrahim Inyass) a can ni ne na yi maku tafinta tsakaninka da Shehu don ina jin Larabci shi ne shugaban ɗariƙar Tijjaniyya. Na faɗa maka cewa yana da mabiya sosai a ɓangarori da dama na Afirka ciki har da Nijeriya inda yake da mabiya da dama a duk faɗin ƙasar. Kuma yana da ɗimbin mabiya a yankin Arewa domin a nan ne Musulmi suke da yawa fiye da ko ina ban taɓa tattaunawa da kai cewa idan muka samu Shehu ya umarci mabiyansa suka goya mana baya jam’iyyarmu za ta yi ƙarfi a Arewa ba. abin da kawai muka tattauna shi ne buƙatar addu’ar Shehu Inyass addu’ar da Shehu zai yi mana ta neman nasarar jam’iyyar AG ce da kuma kai kanka ”

(Paden, 1973: 310)

Idan aka dubi waɗannan bayanai za a ga cewa sun ƙunshi neman kusanci da wani muhimmin mutum ne mai daraja domin samun nasara a siyasance. A cikin bayanin an nuna cewa, ‘yan siyasar guda biyu suna so su yi amfani da darajar Shehu Ibrahim ne su samu jama’ar da za su goya wa jam’iyyarsu ta AG baya a lokacin zaɓe wanda hakan zai iya sa su samu nasara.

Idan aka dubi bayanan da Ibrahim Imam ya yi wa shugaban AG wato Awolowo, ya nuna masa cewa Shaihin malamin yana da ɗimbin mabiya a duk faɗin Afirka ciki kuwa har da Nijeriya. Ya nuna masa muhimmancin yankin da shi Ibrahim Imam ɗin ya fito wato yankin Arewa, inda ya nuna masa cewa mafi yawan ‘yan Arewa Musulmi ne mabiya ɗariƙar Tijjaniyya, wanda idan suka samu sanya bakin shaihin za su samu ƙarin magoya baya sosai daga yankin. Ko ma dai shaihin bai sa baki a cikin lamarin siyasar kai tsaye ba, an nuna cewa ana buƙatar ya yi wa jam’iyyar AG addu’a da kuma ɗan takararta wato Awolowo domin samun rinjaye a zaɓen da suke tunkara a wancan lokacin. Shi kansa wannan neman sa albarkar daga wurin muhimman mutane ko Shehunnai, wani salo ne da za a iya nuna wa magoya baya cewa ai Shehu ya sanya wa jam’iyya kaza albarka don haka ita ya kamata a zaɓa.

A jamhuriya ta biyu ma an samu irin wannan fasalin na danganta ‘yan siyasa da manyan madogaran addini domin samun goyon bayan al’umma. An samu daga Jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo cewa, jam’iyyar PRP ta Malam Aminu Kano ta riƙa amfani da hoton Shehu Ibrahim Kaulaha domin neman magoya baya. Ga abin da ta ce:

An yi kira ga Hukumar Zaɓe ta ƙasa da ta duba yadda jam’iyyar PRP take yin amfani da hoton Shehu Ibrahim Kaulaha wanda aka rubuta harufan PRP a ciki, saboda neman magoya baya Alhaji Musan Sati ya ce, dokar tsarin mulki ta ƙasar nan ta haramta yin amfani da addini a cikin harkokin siyasa, amma kuma ga shi PRP tana cusa addini don neman magoya baya.”

(“Jam’iyyar PRP Na Ci Da Addini”, 1979).

Idan aka dubi wannan batu da yake sama za a ga cewa, a kakar zaɓe na jamhuriya ta biyu, wato shekarar 1979, an yi amfani da darajar shugabannin addini wajen nemen magoya baya a jam’iyyun siyasa. A cikin wannan misalin an nuna cewa jam’iyyar PRP ta yi amfani da hoton Shehu Ibrahim Inyass domin jawo hankalin al’umma su goyi bayan jam’iyyar. Jam’iyyar sun yi amfani da hoton shaihin malamin mai ɗauke da haruffan PRP a ciki, kasancewarsa babban jigo ne a cikin ɗariƙar Tijjaniyya, wannan zai sa duk wani Batijjane ya ji ya gamsu da tafiyar da aka sanya Shehu Ibrahim Inyass a cikinta. A cikin misalin an bayyana cewa, tsarin mulkin mulkin Nijeriya ya haramta amfani da addini a cikin siyasa. Don haka ake kira ga hukumar zaɓe da ta hukunta jam’iyyar don ta karya doka.

Irin wannan salo ya ci gaba da gudana a cikin tarihin siyasar Arewacin Nijeriya, inda da zaran an kaɗa gangar siyasa ‘yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban sukan riƙa kai ziyara da sunan neman albarka ga manyan malamai. Irin waɗannan ziyarce-ziyarce da neman sanya albarka akan yi su ta hanyar bin wasu malaman har gidajensu ko wuraren ibada, kamar masallatan Juma’a ko makarantu ko kuma majalisun da suke bayar da karatu. Yawancin ‘yan siyasa sukan yi wannan ne domin samar da wata alaƙa da za a nuna wa duniya cewa suna tare da irin waɗannan fitattun malaman. Wannan zai sa su samu goyon bayan mabiyan malamin ko wani kaso daga cikinsu. Ga misali:

“A daya daga cikin hotunan ziyarar tasa wanda tuni suka karade shafukan sadarwa, an gano Tinubu durkushe a gaban jigon na darikar Tijjaniyya yayin da shi kuma ya dafa kansa sannan ya saka masa albarka tare da yi masa tofin addu’o’i.”

(Musa, 2022)

Sanin irin darajar babban Shaihin da kuma yawan mabiyansa a matsayinsa na babban jigo a ɗariƙar Tijjaniyya kamar yadda jaridar ta ruwaito shi ne dalilin da ya sa ɗan siyasar ya ziyarce shi. Kamar yadda jaridar ta nuna cewa shi ne babban jigo a wannan ɗariƙa yana da ɗimbin mabiya waɗanda ake sa rai su goyi bayan ɗan takaran kasancewar sun gan shi tare da shaihinsu. Ke nan har a yau irin wannan siyasar ta neman tabarruki daga manyan madogaran addini tana tasiri a cikin siyasa.

A wani misalin na daban kan yadda ‘yan siyasa sukan riƙa danganta kansu da manyan shugabannin addini, Jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo ta ruwaito cewa, ɗan takarar shugabancin Nijeriya na Jam’iyyar PDP ya kai wa Shehu Ɗahiru Bauchi ziyara. Dubi abin da jaridar ta ruwaito:

“Dan takaran shugaban kasa karkashin tutar jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar (Wazirin Adamawa), ya kai wa fitaccen malamin addinin Islaman nan dake Bauchi Sheikh Dahiru Usman Bauchi ziyara a gidan sa dake Bauchi. Atiku Abubakar ya ziyarci jihar Bauchi a ranar Laraba shi da wanda yake masa takaran mataimaki, gwamnan jihar Delta Ifeanyi Okowa.

(Isah, 2022)

 Duk da cewa jaridar ba ta bayyana dalilin kai ziyarar ba, amma dai za a iya fahimtar cewa duk abu ɗaya ake yi wa kai da kawo, wato goyon bayan mabiya wanda ake fakewa da cewa neman albarka aka je. Duk da cewa an san malamai mutane ne masu tsoron Allah da kuma kusanci da shi, wannan ya sa ake sa rai addu’arsu ta kasance ta fi saurin karɓuwa fiye da waɗanda ba su ba, amma dai ko da neman addu’ar ‘yan siyasa suke zuwa suna kuma la’akari da yawan mabiya, domin kuwa wannan ya samo asali cikin tarihin siyasar ƙasar Hausa. Akan riƙa neman kusanci da wani don a ribaci yawan mabiyansa da kuma yadda yake da ƙarfin faɗa a ji.

Irin wannan rige-rigen samun karɓuwa ga mabiya ya sa kowane ɗan siyasa a yau, idan bai je wurin manyan malamai da Shehunnai sun sa masa albarka duniya ta gani ba sai a ga kamar ba ya tare da wannan malamin. Shi kansa ɗan takaran ba zai samu natsuwa ba in bai je ɗin ba, domin zai ga cewa zai rasa goyon bayan mabiyan wannan babban malami addinin.

Watakila wannan dalilin ne ya sa shi ma ɗantakarar Shugaban ƙasa na Jam’iyyar LP a zaɓen shekarar 2023 ya garzaya shi ma kamar yadda jaridar Legit Hausa ta ruwaito kamar haka:

“Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour na kara tsawon kafa da hannu wajen tallata kansa a fadin kasar nan gabanin zaben 2023 Obi da abokin gaminsa, Dr Yusuf Datti Baba-Ahmed sun kai wata ziyara a jihar Bauchi, inda suka gana da babban malamin addini na Afrika, Sheikh Dahiru Usman Bauchi.”

(Ibrahim, 2022).

A nan shi ma Peter Obi ne da mataimakinsa suka kai ziyara kamar yadda takwarorinsu na sauran jam’iyyu suka kai wa Shaihin. Irin wannan ziyarce-ziyarcen ‘yan siyasa sun mayar da su kamar dole a cikin al’amuran siyasa, domin kuwa a yayin ziyarar in ba a roƙi mabiya su zaɓa kai tsaye ba za a roƙi Shehu ya yi addu’a don neman goyon bayan al’ummar ƙasa da kuma samun nasara.

4.6.4 Amfani Da Daraja Ko Matsayi Wajen Tallata Ɗan Takara

Amfani da daraja ko matsayin wasu mutane wajen tallata ɗan takara abu ne wanda ya samo asali a cikin tarihin siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa. ‘Yan siyasa kan yi ƙoƙarin nuna wa al’umma darajarsu ko matsayinsu a cikin al’umma. Sukan yi amfani da alaƙa ta jini ko kusanci da take tsakaninsu da wani mutum ko wasu mutane masu daraja a wajensu domin samun goyon baya daga gare su. Sanannen abu ne a ƙasar Hausa ana girmama nasaba da kuma tsatson da mutum ya fito daga cikinsa. Wannan ya haifar da bambanci tsakanin ɗan wane da kuma ɗan ba kowa ba. Irin wannan bambancin da aka samu shi ne kuma ya samar da waɗanda ake kira masu shi da marasa shi, ko masu mulki da talakawa da sauransu.

Tun kafuwar siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa a wuraren shekarun 1950 an riƙa samun irin wannan siyasar, wato ta amfani da darajar ko matsayin wajen tallata ɗan takara, kuma wannan tsarin fito da dangantakar ta yi tasiri ƙwarai ga ‘yan takara da dama, kasancewar da dama cikin ‘yan siyasar da suka fara shugabanci a farkon siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa sarakuna ne da ‘ya’yan sarakuna. Wannan ya sa dangantakarsu da matsayin da suke kai na sarauta sun taka muhimmiyar rawa wajen tallata su ga al’umma. Alal misali, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi da Sarkin Zazzau Jafaru da Sardauna Sakkwato dukkansu ‘ya’yan gidan sarauta ne, kuma manya daga cikin ‘yan siyasar farko-farko waɗanda suka riƙe manyan muƙaman siyasa a ƙasa, kuma dukkansu da ma wasu ‘ya’yan sarakunan Arewacin Nijeriya da dama sun ci alfarmar gidajen da suka fito wajen samun muƙaman siyasa.

Irin wannan alfarma ta ci gaba da gudana a fagen siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa, wanda har aka kai ga ana tallata ‘yan takarar siyasa da su. Paden (1973: 312) ya bayyana cewa:

“ A lokacin yaƙin neman zaɓen shekarar 1964 an ga tasirin daular Usmaniyya a Kano, inda aka sanya addini ya shiga harkokin siyasa fiye da yadda aka saba a baya. Ya kasance hotunan da jam’iyyar NPC ta yi amfani da su domin yaƙin neman zaɓe suna ɗauke da hoton Sardauna ne haɗe da nasabarsa da aka jero wanda aka nuna ya samu asali ne tun daga Annabi Muhammadu (S.A.W) Su ma NEPU sai suka ɗauki wannan salon a cikin birnin Kano, inda manyan hotunan yaƙin neman zaɓensu suke ɗauke da hoton Malam Aminu Kano tare da Shehu Ibrahim Inyasss a Kaulaha.”

A nan idan aka duba za a ga cewa masanin ya yi bayani ne kan yadda ‘yan siyasa suka fara amfani da matsayinsu ko darajarsu a wurin al’umma wurin tallar siyasarsu da ‘yan takararsu. Alal misali, jam’iyyar NPC ta yi amfani da nasabar Sardauna ta wurin kakansa Shehu Usmanu aka ƙulla nasabar har zuwa ga Annabi Muhammadu (S.A.W) domin nuna cancantar jam’iyyarsu, domin duk wanda ta tabbata ya fito daga wannan tsatson to lallai ya fito daga tsatso mafi girman daraja. Don haka suna nuna idan aka zaɓi jam’iyyar NPC an zaɓi jam’iyyar mutanen kirki. Ta wata fuskar za a ga cewa, ai ko ba a danganta shi zuwa ga tsatson gidan Annabta ba, kakansa Shehu Usmanu shi ma hujja ne na kyakkyawar tsatso. Ke nan, in ma don Shehu za a yi zaɓe to jam’iyyar NPC ta kai, domin dai jam’iyyar jikokin waliyyai ce.

Tarihi ya nuna cewa, a ɓangaren ‘yan hamayya ma an samu irin wannan. An faɗa cewa ana tsaka da yaƙin neman zaɓe, shugaban NEPU Malam Aminu Kano ya kira Sardauna a wayar tarho ya ba da shawara kan raba addini da siyasa, inda a ganinsa yake ganin bai dace ba[7]. Da suka lura da irin salon da aka shigo da shi, sai su ma suka ce in kiɗa ya sauya to dole rawa ma ta sauya. Nan da nan su ma sai suka ɗauki wannan salon ta hanyar haɗa hoton Malam Aminu Kano da na Shehu Ibrahim Inyasss, inda aka riƙa tallar jam’iyyar NEPU da hoton Malam Aminu haɗe da Shehu. Su ma a ɓangarensu suna ganin wannan zai taimaka wa mabiyan Shehu su rungumi ɗan takarar da jam’iyyar take tallatawa, kuma su zaɓe shi.

Duk da wannan salon tallatar ‘yan takara da martabar gida da kuma matsayi, sai da ‘yan hamayya suka kushe wannan tsari da jam’iyyar NPC ta zo da shi, inda suka riƙa kushe nasabar abokan hamayya da kuma matsayin da al’umma suke ganin su da shi, kuma suka riƙa cewa, ai Sardauna ma ba jikan Shehu ne ba kamar yadda ake yaɗawa. Dubi wannan misalin:

“Aminu ya ce wai Sardauna ba jikan Shehu ne ba, kuma wai Sardauna Jahili ne cikin Musulunci. Mu kam mun amince Sardauna jikan Shehu ne kuma ba jahili ne ciki cikin Musulunci ba.”

(Salihu, 1959).

A nan idan aka duba za a ga cewa wani daga cikin magoya bayan NPC ne yake ƙalubalantar shugaban NEPU kan zargin da ya yi kan nasabar shugaban NPC, inda ya ce ai ƙarya ake wa mabiya da dangantakar jini, wai shi ba ma jinin Shehu Usmanu ne ba, domin Shehu babban malamin Musulunci ne, shi kuwa Sardauna ba shi da wannan ilimin, inda ya kira shi jahili a cikin Musulunci kamar dai yadda aka gani a cikin misalin da yake sama.

‘Yan hamayya na jam’iyyar NEPU sun kuma ci gaba da kushe ‘yan jam’iyyar NPC mai mulki cewa suna ta ƙoƙarin danganta kansu da Shehu wanda hakan ba shi da wani amfani ga talakawa, inda suka nuna cewa ai ko ma dai shi jikan Shehu ne, ba Shehun ne za a zaɓa ba. Don haka in don Shaihu za su yi zaɓe in ji Malam Aminu Kano to Shehu ya mutu. Dubi abin da yake cewa:

 “Aminu Kano ya zargi Sardauna da ƙumbiya-ƙumbiya cewa wai shi jinin Shehu ne, ga shi kuwa Shehun ya mutu. Wai don haka in ji Aminu Kano bai ga ta yadda za a yi mutane su zaɓi jinin mutumin da ya mutu ba, idan dai ba jihala mutanen suka sa a ransu ba.

(Salihu, 1959).

A nan idan aka duba za a ga cewa, ƙoƙarin da jam’iyyar NPC take yi ne na tallata ‘yan takararta da alfarmar Shehu Usmanu, musamman ma Sardauna, shi ne ‘yan hamayya suka ƙoƙarin dakushe hasken wannan dangantakar tun da sun ba da shawarar cewa a cire wannan tsarin na haɗa addini da siyasa, amma ba su yi nasara ba.

A wani misalin na daban da ya fito a cikin jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo ta ranar 20 ga Nuwamba, 1959, an nuna yadda wakilin da jam’iyyar NPC ta tura domin yaƙin neman zaɓe a Sakkwato daga lardin Kano, ya nuna irin dangantakar da take tsakanin Shehu Usmanu Ɗanfodiyu da ‘yan NPC waɗanda ya ce ‘yan NEPU suna zaginsu. Dubi abin da jaridar ta ruwaito:

“Malam Sabo ya ci gaba da cewa, ga shi jam’iyyar NEPU tana ta yaba wa da aikin Shehu Usman Ɗan Fodiyo sosai, amma kuma ga shi tana ta zagin jikokinsa. Idan dai da jam’iyyar NEPU tana son Shehu Usman Ɗan Fodiyo sosai da kuwa ba ta riƙa tozarta jikokinsa. Domin fa Hausawa sun ce maso uwa ya so ɗanta. Malam Sabo Bakin Zuwo ya ce kure ne mutum ya so Annabi amma ya riƙa zagin jikokinsa.”

(“Sabo Bakin Zuwo Ya Yi Nasarar Yaƙin Zaɓe”, 1959).

A nan Malam Sabo Bakin Zuwo yana ƙoƙarin nunawa dangantakar shugabannin NPC ne da Shaihu Usmanu Ɗafodiyo. Inda ya nuna cewa, ko don alfarmar Shaihun bai kamata ‘yan NEPU su riƙa zagin jikokinsa ba, wato su Ahmadu Bello Sardauna. Haka kuma, dangantakar Shaihu Usmanu ta jini ce har zuwa ga Manzon Allah (S.A.W). Don haka duk masoyin Manzon to ya zama wajibi ya so duk wani wanda ya dangance shi. Bai kamata mutum ya riƙa iƙirarin cewa yana son Annabi ba bayan kuwa yana tozarta jikokinsa. Don haka ya zama dole in dai mutun yana ƙaunar Annabi to ya so Shaihu Usmanu. Wanda kuwa yake son Shaihu Usmanu to dole ya so Sardaunan Sakkwato, kasancewarsa jikan Shaihu Usmanu.

 Irin wannan ya ci gaba da fitowa a cikin ayyukan zube na Hausa inda aka riƙa amfani da matsayi ko dangantaka wajen tallata ‘yan takara, ko kuma a yi amfani da wannan a matsayin hanyar da ake bi domin nuna cancantar ‘yan takara. A jamhuriya ta huɗu da ake ciki yawancin ‘yan takara ba cancantarsu ce take sa a tsayar da su a ƙarƙashin tutar wata jam’iyya ba. Akan yi amfani da matsayinsu, ko dai ya zama matsayinsu a jam’iyyance ko kuma matsayin abin arziƙinsu wato abin hannunsu. Sau da dama akan samu ɗan takara ya cancanta, amma saboda ba shi da abin hannu ko kuma ba wani matsayi mai girma yake da shi a cikin al’umma ba, sai a ce ai bai cancanta. Misali, irin wannan ya fito a cikin Littafin Tura Ta Kai Bango, inda Shugaban jam’iyyar Riƙau Alhaji Harambe yake jawabi a wajen yaƙin neman zaɓe. Dubi abin da yake cewa:

“ lallai kar ku sake ɗan da bai gaji arziƙi ba ya jawo maku bala’i. In kuwa kun sake za ku yi da na sani wata jam’iyya ce wadda ko sunanta ba zan faɗa ba cikin sharrukanta da ta tanada sun haɗa da lalata darajar sarakunanku. Su sa talaka ya raina mutane masu martaba ”

(Katsina, 1983: 8).

Wannan misali ya fito da hoton tallata ɗan takara ne ta hanyar amfani da matsayi ko daraja, domin an nuna cewa talaka bai isa ya yi shugabanci ba, domin wanda bai gaji arziƙi ba ana nufin talaka ne, kuma zaɓensa tamkar jawo wa kai bala’i ne. An ci gaba da nuna cewa jam’iyyar da ba tasu ba tana da sharri sosai, domin za ta lalata darajar sarakuna domin su ne masu matsayi da daraja a cikin al’umma, sannan kuma wannan jam’iyyar za ta sa talaka ya raina mutane masu martaba. Idan aka duba za a ga, shi talaka dai a nan ba shi da wata daraja da martaba, wannan ya sa suke ganin cewa masu hannu da shuni, waɗanda suka gaji arziƙi da masu mulki ko sarakuna ko kuma jininsu su ne waɗanda ya kamata su ci gaba da zama a sama, shi kuma talaka ya ci gaba da biyayya.

A wani misalin na daban an nuna cewa, jagororin jam’iyyar hamayya da mabiyansu talakawa ne waɗanda ba su da wata daraja ko matsayi a cikin al’umma. Don haka ba su cancanci a zaɓe su ba. Dubi wannan misalin:

“Ni ai da ma na san wannan yaron bai gaji arziƙi ba. Ubansa fa Na-Torami har ya mutu itace yake sarowa yana sayarwa ”

 

“Yo shi Garban fa? Ubansa ba mahauci ba ne karen lahira?”

(Katsina, 1983: 21-22).

A nan shugabannin jam’iyyar Riƙau ne suke kushe jagororin jam’iyyar Sauyi, inda suke nuna cewa ai dukkansu ba ‘ya’yan kowa ne ba. Kamar yadda suke nuna cewa ai shi jagoran jam’iyyar ma wato Hassan, ubansa itace yake zuwa daji ya saro ya sayar. Shi kuwa abokinsa Garba ubansa mahauci ne, ba wani ƙima ko matsayi suke da shi da har suka cancanci a bi jam’iyyarsu ko a zaɓe su a wani matsayi ba. Irin wannan shi ne abin ya riƙa faru a jamhuriya ta farko ma, domin yawanci ‘yan jam’iyyar hamayya talakawa ne da msu ƙananan sana’o’i kamar maɗinka da majema da masassaƙa da sauransu. Ita kuwa jam’iyya mai mulki sarakuna ne da attajirai a cikinta.

Ke nan idan aka duba, irin wannan salon na amfani da dangantaka yana da asali a cikin siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa, domin kuwa shi ne ya riƙa bayyana a cikin ayyukan adabin Hausa musamman na zube kamar yadda aka ba da misalai da su.

4.7 Tallata ‘Yan Siyasa Da Ɗaukaka Ko Martabar Shugabannin Siyasa

Kamar yadda aka yi bayani a sama cewa ‘yan siyasa suna amfani da matsayi ko darajar wani mutum wajen tallata kansu ko kuma magoya bayansu su riƙa tallata su a wurin al’umma. Waɗannan masu matsayin kan kasance ko dai ta fuskar addini ne ko nasaba ko kuma matsayinsu a siyasance.

Tarihi ya nuna cewa, bayan wucewar jamhuriya ta ɗaya da aka riƙa amfani da darajar manyan waliyyai da Shehunnai, an ci gaba da amfani da ƙima da matsayin manyan shugabannin siyasa waɗanda suka shuɗe, ana amfani da abubuwan alherin da suka aiwatar ana tallata ‘yan takara da sunansu. Alal misali, an sha jin ana kiran ‘yan siyasa da magajin Sardauna ko magajin Malam Aminu Kano, wannan kuwa ba zai rasa nasaba da irin siyasar da suka gudanar da kuma ayyukan alherin da suka dasa waɗanda har yanzu ana cin gajiyarsu ba.

Irin waɗannan abubuwan alheri da manyan ‘yan siyasan suka gabatar lokacin rayuwarsu ya sa ake ganin cewa duk wanda ya ce zai bi turbarsu, ko kuma turbarsu ma yake bi, to ana sa rai zai gaji irin kyawawan manufofinsu ne wajen shimfiɗa nasa jagorancin idan ya yi nasara. Alal misali, a jamhuriya ta biyu, Malam Abubakar Rimi da Malam Balarabe Musa sun samu nasarar zama gwamnonin jihohin Kano da Kaduna ne a jam’iyyar PRP wadda Malam Aminu Kano ne jagoranta. Haka kuma Alhaji Shehu Shagari ya yi nasarar lashe kujerar shugabancin Nijeriya a Jamhuriya ta biyu, a ƙarƙashin tutar Jam’iyyar NPN, wadda ake yi wa kallon gyauron NPC ta su Ahmadu Bello Sardauna, kamar yadda ake yi wa PRP kallon gyauron NEPU ce ta su Malam Aminu Kano.

Tarihi ya ci gaba da maimaita kansa, inda a jamhuriya ta huɗu ma an lura cewa ‘yan siyasa suna amfani da wannan alfarma ta shugabannin siyasa wajen tallata kansu ko kuma ‘yan takararsu. Misali, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso yana alaƙanta tsarin siyasarsa da ta Malam Aminu Kano, inda yake nuna cewa, turbarsa suke bi wato da shi suke koyi. Tun daga yanayin sanya tufafinsa da kuma aƙidar ‘yanta talakawa. Da wannan ya riƙa amfani har zuwa lokacin da ya kafa tasa ɗariƙar siyasar wadda aka kira ta Kwankwasiyya, inda shi ma a yanzu wasu ‘yan siyasar suke raɓuwa da sunansa don cim ma burinsu a siyasance.

Wani babban misali da za a iya gani a zahiri dangane da yadda ‘yan siyasa sukan riƙa danganta kansu da wasu manyan ‘yan siyasa su shiga rigarsu don su samu alfarmarsu shi ne, yadda ‘yan siyasa suka riƙa danganta kansu da tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari tun daga shekarar 2007 domin samun nasara a zaɓe. Dubi wannan misali:

“ a yau a Nijeriya, ambaton sunan Buhari ya zama tamkar ambaton wani aikakken umurni ne, ba a ja da shi, ba a muzanta shi kuma ba a aibanta shi. Hasali ma yawa-yawan wasu ‘yan takara da hotunan Janar Buhari suke kamfe. Sai ka ga irin waɗannan ‘yan takara sun buga posta (poster) ɗauke da hotunansu da Buhari, don amincewa da Buhari, don cin albarkacinsa ko tubarrakinsa ko kuma don shuga inuwarsa, abubuwan da gaskiyarsa(shi Buharin) suka jawo masa.”

(Ibrahim, 2007).

Idan aka dubi wannan bayani da jaridar Aminiya ta kawo za a fahimci yadda aka riƙa tallata ‘yan siyasa da martabar shugabannin siyasa. Janar Buhari ya zama wani tauraro a fagen siyasar zamaninsa, wanda kowane ɗan takara yake so ya danganta kansa da shi domin ya ci albarkacinsa. Wannan ba zai rasa nasaba da yadda farin jinin Buharin ya ratsa lungu da saƙo na ƙasar Hausa ba. Ya kasance sunan shi ne shi ne ake ji a ko ina. Ba a ja da duk wani abu da aka danganta shi da shi, ba a musu da duk wani abu da aka ce daga wurinsa aka ji, ba a kuma kushe shi ko aibanta shi a bainar jama’a. Wannan ya sa ‘yan takara da dama suka suka riƙa haɗa hotunansu da na Buharin domin nuna cewa sun amince da tsarinsa kuma suna tare da shi, suna goyon bayansa. Sukan yi hakan ne domin cin albarkacinsa da samun shuga inuwarsa don su samu karɓuwa ga jama’a. Jama’a a wancan lokacin sun yi imani cewa janar Buhari mai gaskiya ne, kuma duk waɗanda suke tare da shi su ma haka ake sa rai su zama. Wannan ya sa suka samu farin jini sosai a dalilinsa.

Baya ga ‘yan jam’iyyar Janar Buhari ta ANPP a wancan lokacin da tarihi ya nuna cewa sun shiga inuwarsa domin samun karɓuwa, an ci gaba da amfani da irin wannan salon har zuwa kakar zaɓen shekarar 2015. ‘Yan takara na jam’iyyu daban-daban baya ga jam’iyyar APC wadda Janar Buhari yake ciki, sun riƙa amfani da hotunansa, inda sukan haɗa da nasu duk da cewa ba jam’iyya guda suke ba, domin samun tubarrakinsa. Wannan ne ma ya sa jam’iyyar APC a wancan lokacin suka tsawatar wa ‘yan jam’iyyar hamayya cewa su daina amfani da farin jinin ɗan takarar jam’iyyarsu domin neman jama’a. Dubi abin da jaridar Aminiya ta ruwaito:

Jam’iyyar APC a Jihar Katsina ta gargadi masu takara da suka fito daga wasu jam’iyyu su daina hada hotunansu da na dan takararta na Shugaban kasa Janar Muhammadu Buhari. Shugaban jam’iyyar, Dokta Mustafa Inuwa ne ya yi wannan gargadi a waurin taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar ta yi a otel na Liyafa a ranar Litinin inda ya ja hankalin ’yan takarar wasu jam’iyyu da ke lika hotunansu da na Buhari su daina yin haka nan take ko su fuskanci matakin shari’a.”

(Mustapha, 2015)

Kasancewar wannan ɗan siyasa mai matuƙar farin jini a zamaninsa, wanda har aka bayyana cewa shi ne ɗan siyasa mafi farin a kaf faɗin Nijeriya, kamar yadda Jaridar Blueprint Hausa ta ranar 26 ga Afrilu ta ruwaito. A zamaninsa an kai ga ba ma ‘yan jam’iyyarsa kaɗai suke haɗa hotonsa da nasa ba, har ‘yan jam’iyyun hamayya sun lura da irin farin jininsa a lokacin, sai suka riƙa haɗa hotunansu da nasa duk da cewa su suna neman takara a wata jam’iyyar ce daban ba jam’iyyarsa ta APC ba. Irin wannan ɗaukaka ta Buhari ta sa ‘yan siyasa a kowane lungu da saƙo sun riƙa tallata kansu da farin jinin Buhari. A wasu wuraren ma har magoya bayansu sukan yi masu laƙabi da ‘Buharin wuri kaza’. Alal Misali, ana kiran wani ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙaramar hukumar Lere a jihar Kaduna da suna ‘Buharin Lere’ wanda ire-irensa suna da dama. Irin wannan tallata ‘yan siyasa da farin jini Buhari da wasu ‘yan siyasa musamman na wasu jam’iyyun da ba nasa ba suka riƙa yi ya kai ga har jam’iyyar APC ta yi barazanar kai ƙarar dukkan masu tallata kansu da farin jinin Buharin kotu idan ba su bari ba, kamar dai yadda aka gani a cikin misalin da yake sama.

Bayan kammala zaɓuɓɓukan shekarar 2015, an bayyana cewa Muhammadu Buhari shi ne ɗan siyasar da mutane suka riƙa mutuwa don murnar samun nasararsa a zaɓen da aka gudanar. A wannan lokacin sauran ‘yan takara da ba a kai ga yin zaɓen su ba, kamar gwamnoni da ‘yan majalisar jihohi, sai suka ci gaba da haɗa hotunansu da na Shugaba Buharin. Ya kai ga ko takarar kansila mutum ya fito sai ya haɗa hotonsa da na Buhari don ya samu farin jininsa. Dubi wannan misalin da yake ƙasa:

Wannan bawan Allah shi ne wanda ya fi kowa farin jini a tarihin ƙasarmu Nijeriya. Ɗaruruwan mutane sun rasa ransu saboda murnar zaɓen da ya ci a shekarar 2015. An yi lokacin da ko takarar kansila mutum ya tsaya sai ya haɗa hotonsa da na Buhari don ya ɗosani farin jini. ‘Yan siyasa bila’adadin sun ci zaɓe a sanadiyyar ɗaga hannunsu da Buhari ya yi, tun kafin ya ci nasa zaɓen a shekarun baya tsakanin shekarar 2003 zuwa 2011 Allah kaɗai ya san adadin mutanen da shugaba Buhari ya ɗaga wa hannu suka kai labari.”

(Giwa, 2023).

A cikin wannan misalin, an nuna yadda ‘yan siyasa suka riƙa danganta kansu da martabar shugabannin siyasa, domin samun karɓuwa a wurin al’umma tun daga shekarar 2003 lokacin da Buhari ya fara fitowa takarar shugabancin Nijeriya zuwa saukarsa a 2023. Allah ne kaɗai ya san adadin mutanen da suka ci zaɓe da alfarmarsa, domin tun ma kafin shi ya ci nasa zaɓen, wato daga 2003 zuwa 2011, mutanen da ya ɗaga masu hannu ko ya yi umarni da a zaɓe su kuma aka zaɓe a jam’iyyun APP da ANPP da CPC kuma suka yi nasara Allah ne kaɗai ya san adadinsu. Ba ma shi Buharin kansa ba, tsintsar farin jininsa ya sa a shekarar 2015 kaso mafi tsoka na waɗanda suka fito takara a jam’iyyarsa ta APC sun lashe zaɓe ba tare wata wahala ba, sai don albarkacin sun fito a jam’iyyar Buhari.

Inda wannan martaba tasa ta fito fili shi ne, inda shugabannin jam’iyyar APC suka riƙa gargaɗin ‘ya’yan jam’iyyar lokacin da zaɓen shekarar 2023 ya gabato, wato lokacin da wa’adin mulkin Buhari ya zo ƙarshe. A lokacin sun riƙa faɗa wa ‘yan jam’iyyar tasu cewa dole fa kowa ya shiga taitayinsa, ya koma mazaɓarsa ya nemi jama’a domin wannan karon Buhari ba ya cikin jerin ‘yan takara. Dubi wannan misalin da yake ƙasa:

“John Udoedeghe ya ce zuwa babban zaben 2023, lokacin da mutane za su shige inuwar shugaban kasa Muhammadu Buhari ya wuce. A 2023 ne shugaba Buhari zai kammala wa’adinsa na shekaru takwas. Ana tunanin cewa APC ta na samun damar lashe zaɓuɓɓuka a matakai da dama saboda sunansa. Sanatan na jihar Edo ya gargadi magoya bayan jam’iyyar da cewa, a zaben 2023, shugaba Muhammadu Buhari ba zai fito a cikin masu takara ba.”

(Malumfashi, 2023).

A wannan misalin an nuna cewa, duk masu shantakewa su fake da sunan Buhari su lashe zaɓe yanzu dai lokaci ya wuce, don haka kowa ya koma mazaɓarsa ya san na yi. Kamar yadda aka gani ciki misalin, jam’iyyar APC tana lashe zaɓuɓɓuka a matakai da dama ne saboda sunan Buhari, kuma ga shi ya kammala wa’adinsa ba zai sake yin wani takara ba.

Idan aka dubi waɗannan misalai da aka kawo za a fahimci cewa, amfani da matsayi ko martaba na shugabannin addini ko na siyasa abu ne wanda za a iya cewa ya samo asali tun daga lokacin da aka fara siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa, kuma irin wannan salon kaska raɓi mai jini ya ci gaba da tafiya har zuwa wannan zamanin siyasar da muke ciki wato jamhuri huɗu, inda ake amfani da daraja ko matsayi ko kuma sunan wasu mutane da ma na wasu ‘yan siyasar domin samun cim ma nasara a siyasance.

4.8 Matsayin Mata A Cikin Siyasar Jam’iyyu

A ƙasar Hausa mata suna da matsayi na musamman wanda addini da al’ada suka ba su. Mafi akasarin mata a ƙasar Hausa a ƙarƙashin iyaye ko mazajensu suke rayuwa. Duk wata ɗawainiya tasu takan fara ne daga kan iyaye, bayan sun yi aure kuma sai nauyinsu ya koma kan mazajensu. Kasancewar mafi yawan al’ummar ƙasar Hausa Musulmi ne, waɗanda kuma suke da al’adu da ɗabi’u waɗanda ba su yi takin saƙa da addininsu ba, musamman bayan jihadin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo, wannan ya sa ake ganin akwai wasu abubuwa da suka keɓanta da maza kaɗai, wasu kuma mata.

Dangane da abin da ya shafi siyasa musamman ta jam’iyya da ake magana a Arewacin Nijeriya kuwa, tun da farko mata ba su samu wani matsayi a cikinta ba. Duk al’amuran siyasa a farko maza ne suke gudanar da ita, kuma babu inda aka sanya mata a cikin kowane sha’ani. Manyan ‘yan Siyasar Jamhuriya ta farko irin su Malam Sa’adu Zungur da Malam Aminu Kano su ne suka yi ta faɗi-tashin ganin an sanya mata a cikin siyasa, a cewarsu su ma mata ya kamata a ba su haƙƙinsu. Wannan ya sa suka yi ta ƙalubalantar tsarin masarautun gargajiya, wanda a cewarsu su ne suka hana mata rawar gaba hantsi a cikin al’amuran siyasa ta hanyar rufe su a cikin gida ba tare da ba su ‘yancin shiga al’amuran al’umma a dama da su ba.

Paden, (1973:290-291) da Yakubu (1999:B.Sh) sun bayyana irin wannan tsari na danniya a cikin ayyukansu, inda suka nuna cewa Malam Sa’adu Zungur ne ya yi ta gwagwarmaya kan lallai sai an bai wa mata ‘yancin samun ilimi mai zurfi da kuma damar shiga siyasa.

Abubuwan da aka fi mayar da hankali a kansu a wuraren shekarun 1950 su ne ƙalubalantar tsarin masarautu kan batun bai wa mata dama su shiga cikin siyasa da batun iko da kuma faɗa aji. Wannan shi ne batun da Malam Aminu Kano ya bai wa ƙarfi lokacin da ya tafi tsangayar Ilimi a London kamar yadda ya bayyana a cikin rubuce-rubucensa.

Wanda ya fi shahara kan batun matsayin mata a cikin al’umma shi ne Isa Wali wanda ya yi rubutun da ya ta da ƙura a cikin jaridar Nigerian Citizen. A cikin rubutunsa ya bayyana yadda Musulunci ya bai wa mata ‘yanci, da kuma irin gudummawar da mata za su iya bayarwa a cikin al’umma, kamar yadda yake cewa:

“As for public life, there is nothing in Islam which preventsa woman from following an pursuit she desire. There is no distinct prohibition agaist her taking part in public leadership – as Aisha the prophet’s widow and her leading women colleagues (the “Mother of Believers”) har demonstrated Moslem history, in fact, is full of the account of Moslem women in many countries who had been glorious rulers, counsellors, jurist and great public servants. They commanded armies, and, when necessity arose, fought as soldiers as they did in early Islam – before the end of tenth century.”

Fassarar marubuci:

“A cikin zamantakewa ta yau da kullum babu inda Musulunci ya hana mata bin tsarin rayuwa daidai da su kuma yadda suke buƙata. Babu inda aka haramta wa mace shiga harkar shugabancin al’umma kamar yadda Aisha (Uwar Muminai) matar Manzon Allah ta nuna a cikin jagoranci da ta yi wa mata Tarihin Musulunci a cike yake da bayanan mata daga ƙasashe daban-daban, waɗanda suka zama shugabanni da masu faɗa a ji da masu ilimi da kuma manya hadiman al’umma.wasu ma sun jagoranci rundunoni idan ma buƙata ta taso sukan shiga a fafata da su a matsayin sojoji kamar dai yadda suka a farkon Musulunci kafin ƙarshen ƙarni na goma.”

(“The True Position of Women in Islam”, 1958)

A nan ya bayyana irin yadda addini ya bai wa mata ‘yanci ne na shiga al’amuran yau da kullum waɗanda suka haɗa har da siyasa da shugabanci wanda masarautun ƙasar Hausa suka hana mata wannan ‘yancin. Shi kuma ya nuna cewa akwai mashahuran mata da aka yi su a tarihi tun daga kan Uwar Muninai Nana A’isha, da ma wasu mata da aka yi su a cikin tarihi waɗanda sun bayar da gudummawa a cikin harkar shugabanci wanɗanda kuma tarihi ya ambaci sunayensu kuma ba zai taɓa mantawa da su ba.

Ba ma shugabanci ko jagorancin a addini ba, a jamhuriya ta farko hatta shugabancin mata na jam’iyyar NPC a jamhuriya ta farko tarihi ya nuna cewa namiji aka baiwa, don dai kada a bai wa mace ya zama kamar an ‘yanta su, sai aka bai wa namiji wanda shi ne zai riƙa tattaunawa da su, kuma ya kai rahoto ga uwar jam’iyya. Irin wannan bayani ya fito a cikin wata wasiƙa, inda aka yi ƙorafin cewa hakan da aka yi bai dace ba. Ga abin da wasiƙar take cewa:

 “Idan Edita ya yarda ina son ɗan fili a cikin jaridarka mai ƙaunar dangi don in nuna wani kuskure da aka yi na nada namiji shugaban matana NPC na Kano. A haƙiƙar gaskiya wannan ba dacewa ne kawai bai yi ba har ma da shirme na tabbata dukkan matan NPC ba za su goyi bayan a ce duk cikinsu a rasa shugabar mata mace ba, sai kurum a ce ga wani mutum shi ne shugabanku kullum zai riƙa kiranku kwamiti.”

(Yakasai, 1960).

Daga jin abin da wannan wasiƙar ta ƙunsa za a fahimci matsayin mata a siyasar ƙasar Hausa a farko, domin bayanin ya nuna yadda kwata-kwata ba a bai wa mata wani matsayi a cikin siyasar jam’iyyu a Arewacin Nijeriya ba. Yawanci ana faɗin cewa ciwon mace na ‘ya mace ne. Ta yaya za a bai wa namiji jagorancin mata ba tare da tunanin cewa akwai abin da ba za su iya tattaunawa da namiji ba sai ‘yar’uwarsu mace? Wannan ya nuna cewa ita kanta muryar matan ba son jin ta ake yi ba, shi ya sa aka sanya wanda ba za su iya kokawa har a ji amon muryar tasu ba a matsayin shugabansu, wato namiji, domin akwai wasu abubuwan da idan suka kai kuka wurinsa shi kuma ya ga cewa har da shi abin zai shafa, ba zai kai koken nasu ba.

Da yawa mata sun yi ta kokawa kan rashin ilimi da ba a ba su damar yi ba, ko kuma ba su samun yin mai zurfi, wannan kuwa ba zai rasa nasaba da irin yadda aka hana matan motsin ƙarfi ba. Da gangan aka yi hakan domin dai duk wanda ya yi ilimi to yakan iya bambance abin da ya dace da shi da wanda bai dace da shi ba, sannan kuma yakan san haƙƙoƙinsa. Idan kuwa aka bari matan suka samu ilimi da kansu ma za su nemi a ba su wasu haƙƙoƙi nasu da aka hana su. Shi kansa ilimi a farko ba a bai wa mata dama ba, akan bar su kaɗai su san abin da ya kamata su sani na ibada ne, wasu ma ko na gudanar da ibadar ba su samu gatan yi ba.

Ilimin boko kuwa wanda a lokacin mazan ma ba sun gama yarda da shi ba ne balle a sanya mace. Wannan ya sa duk waɗanda suka yi karatu mai zurfi a farko maza ne, kuma da yawansu ‘ya’yan gidan sarauta ne, kuma ‘yan jam’iyyar NPC. An kuma sani cewa a gidajen sarauta a ƙasar Hausa mata ba a ba su wata dama ba, an dai bar su a cikin gida ne kawai a matsayin masu yi wa sarakuna hidima, ba su da wani aiki sai dai a biya buƙata da su, su kuma yi sauran hidimomi. Su kuwa talakawa na jam’iyyar NEPU suna ganin hakan bai dace ba, shi ya sa ma suke ta fafutukar sai an bar mata sun samu ilimi don su ma a dama da su.

  Daga baya, mata waɗanda suka ɗan fara samun ilimin zamani sun yi ta kiraye-kiraye ga mata ‘yan uwansu a cikin jaridu cewa, su tashi su nemi ilimi don su ma a dama da su, don sun fahimci cewa gwamnati a wancan lokacin ba ta son su san halin da ake ciki, shi ya sa ba ta ba su damar neman ilimi ba. Dubi wannan misalin:

“ saboda haka nake ganin cewa babban abinda ya kamata mu mata na jihar Arewa mu yi shine mu zage mu ba kanmu ilimi ta kowane fanni, kada mu tsaya muyi jiran malalciyar gwamnatin NPC mata ba abin da ba za mu iya ba matukar an koya mana. Babu ko wanda ya danne mu wajen ci gabanmu har matan jihohin gabas da yamma suka wuce mu irin NPC wadda Sardauna yake ja.”

(“Mata ‘Yan Uwana Mu Nemi Ilimi”, 1961).

Wannan bayanin ya nuna cewa, gwamnatin NPC ba ta bai wa mata ‘yanci ba ta kowace fuska. Idan aka yi la’akari da abubuwan da suke cikin wannan misalin za a ga cewa wasu matan sun fara fahimtar cewa suna da amfani a cikin al’umma. Sun fara fahimtar cewa in suka samu ilimi za su iya yin wasu abubuwa kamar yadda maza suke yi, ciki har da shiga harkokin siyasa da shugabanci a dama da su. A cikin misalin kuma in aka duba za a ga cewa an ɗora alhakin rashin ilimin nasu a kan gazawar gwamnatin NPC wanda su kansu ‘yan hamayya suke ta fafutukar sai an bai wa matan dama.

Tarihi ya nuna cewa, hatta jefa ƙuri’a tsarin sarakunan ƙasar Hausa bai ba wa mata damar yi ba. Maza ne kaɗai suke jefa ƙuri’a a lokacin zaɓuɓɓukan da aka yi a jamhuriya ta farko, duk kuwa da irin kiraye-kiraye da su Malam Sa’adu Zungur suka yi ta yi. Ba a samu wannan damar ba sai a jamhuriya ta biyu a wuraren 1979 lokacin da aka bai wa mata damar jefa ƙuri’a, kamar yadda Yakubu(1999: B.Sh) ya bayyana:

“A baya masarautu sun hana mata ‘yancinsu na yin zaɓe da sauran haƙƙoƙi da wasu damammakinsu na rayuwa da wasu al’amuran yau da kullum. Wannan yana cikin irin fafutukar da Sa’adu Zungur ya yi ta yi domin gina sabuwar Nijeriya.”

(Yakubu, 1999: B.Sh)

A Jamhuriya ta biyu, Jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo ta ranar 9 ga Yuli, 1979 ta buga hoton wasu mata a Sakkwato, a jere bisa layin jefa ƙuri’a a zaɓen da aka gudanar a wannan shekarar. Wannan ya nuna cewa mata ba su samu ‘yancin yin zaɓe ba sai a Jamhuriya ta biyu kamar yadda Malam Aminu Kano ya faɗa a cikin wani jawabinsa bayan zaɓen da aka gudanar a jamhuriya ta biyu. Dubi abin da ya ce:

“ mun fuskanci kamu da tsarewa da duka da nau’o’in azaba da muka bayar da shawarwari a ƙyale mata su yi zaɓe, sai da aka ce a tuntuɓi imaninmu a matsayin Musulmi aka zarge mu da’ kauce hanya’. Amma ku duba yadda duk aka fahimci abubuwa, hakan ba nasarar PRP ba ce?”

(Jega da wasu, 2002:38).

Wannan ci gaba ce aka samu a ciki tsarin siyasar jam’iyyu, musamman idan aka kwatanta da yadda aka fito a jamhuriya ta ɗaya. Kafin samun wannan cigaban, Malam Aminu Kano ya ce ‘yan jam’iyyar NEPU sun fuskanci nau’o’in azaba da suka shafi kamu da ɗauri da duka duk don sun bayar da shawarar a bar mata su yi zaɓe, har sai da ta kai ga ana ganin ma sun kafirce wa addini inda aka ce a binciki imaninsu, sai dai a ƙarshe ya nuna cewa an samu nasara, tun da an bai wa mata ‘yancin yin zaɓen.

A ci gaba da fito da matsayin mata a cikin siyasar jam’iyyu a cikin tarihi, Malam Aminu Kano a jawabinsa na kafa jam’iyyar PRP a jamhuriya ta biyu, ya bayyana cewa sun daɗe suna gwagwarmayar samo wa mata ‘yanci tun a zamanin NEPU, kuma za su ci gaba har sai an kai ga nasara. Dubi abin da yake cewa:

“A ci gaba da gwagwarmayar da muke game da mata kuwa, a wannan jam’iyyar za mu ci gaba da wannan ƙoƙari har sai mun ci nasara. Idan za ku iya tunawa, a shekarun baya mun yi gwagwarmaya domin samo wa mata ‘yanci don su shiga harkokin ƙasa, wannan gwagwarmaya ta fara haifar da nasara. Ba za mu gajiya ba har sai mun ci nasara baki ɗaya.”

(Jega da wasu, 2002:18).

A cikin bayanin nasa, ya nuna cewa gwagwarmayar nema wa mata ‘yanci da jam’iyyarsa take fafutuka ya haɗa har da ba su dama su shiga cikin harkokin ƙasa, wanda ya shafi mulki da shugabanci da aikin gwamnati, inda ya nuna cewa, wannan fafutukar tasu ta fara samun nasara. A ƙarshe an bai wa matan dama ciki har da na jefa ƙuri’a da shiga harkokin siyasa kamar yadda aka bayyana a sama.

Daga cikin mata da suka shahara a fagen siyasa tun daga jamhuriya ta ɗaya har zuwa jamhuriya ta biyu akwai Hajiya Gambo Sawaba. Tana cikin ajin farko a ɓangaren mata da suka shiga siyasar jam’iyya. Ta taka rawar gani, musamman wajen fafutukar ƙwato haƙƙin mata ta fuskar damar samun ilimi da jefa ƙuri’a da kuma shiga zaɓuɓɓuka. Duk da cewa ba ta samu damar yin ilimin boko ko wani ilimi mai zurfi ba, amma dai gudummawar da ta bayar a fagen siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa abu ne da tarihi ba zai manta da ita ba. Ita ce mace ta farko da fara zama shugabar mata ta ƙasa ta jamiyyar NEPU.

An zaɓi Gambo sawaba da wasu sauran mata 18 na jam’iyyar NEPU a kan muƙamai daban-daban da suka shafi mata a shekarar 1958[8]. Wannan ya nuna cewa jam’iyyar NEPU ce ta fara bai wa mata damar shiga harkokin siyasa a aikace kamar yadda jam’iyyar take ta kiraye-kiraye.

Wani cigaba da aka samu kan abin da ya shafi shigar mata cikin al’amuran siyasar jam’iyyu shi ne, yadda matan suka riƙa kakkafa ƙungiyoyi na siyasa, kuma suka ci gaba da fafutukar neman a ba su dama musamman a jamhuriya ta biyu, inda suka samu damar yin zaɓe da shiga al’amuran da suka shafi jam’iyyun siyasa. Dubi jawabin sakatariyar ƙungiyar matan PRP ta ƙasa inda ta ce:

“Ba ƙaramar nasara ba ce don an kafa wannan ƙungiya ta matan Ceton Al’umma, wanda a cikinta muna da damar tatttauna abubuwan da ya kamata a cikin jam’iyyar Shekaru da dama da suka wuce, ayyukan ci gaban ƙasa da gudanarwa duk yana danƙe a hannun maza, tun ma ba a nan jihohin Arewa ba. Yau a ƙarƙashin Jam’iyyar Ceton Al’umma, mun sami dama kuma mun ɗaura niyyar kawar da wannan tsari ”

(“Sakatariyar Jam’iyyar PRP”, 1979).

Ba zaɓe ne kaɗai mata suka samu damar yi a jamhuriya ta uku ba, har da shiga harkokin siyasa a dama su. Kamar yadda wannan misalin da yake sama ya nuna, mata sun kakkafa ƙungiyoyi na siyasa ƙarƙashin jam’iyyu, inda matan jam’iyyar PRP ma suka kafa tasu. Wannan ƙungiyar kamar yadda sakatariyarta ta bayyana za ta ba su damar tattauna al’amuran siyasa da suka shafi jam’iyyarsu ta PRP. Sun nuna cewa, dukkan wani abu da ake gudanarwa maza ne suke riƙe da shi musamman a Jihohin Arewa. Sun lashi takobin kawar da wannan tsarin na danniyar maza kamar yadda suka ce, tun da sun samu damar shiga cikin siyasar su ma a dama da su.

Wannan ya nuna cewa, mata suna da ƙishirwar son shiga cikin siyasa da gudanar da al’amuran jama’a tun daga jamhuriya ta farko inda fafutukar ta soma, wanda sai a yanzu ne suka samu cikakkiyar dama. Sakatariyar ta ci gaba da nuna cewa, a cikin tarihin ginuwar siyasar a ƙasar Hausa, akwai mashahuran mata da suka ba da gagarumar gudummawa. Dubi abin da ta ce:

A cikin tarihin Nijeriya, ba za mu manta da muhimman abubuwan da manyan mata kamar Sarauniya Amina ta Zariya wadda ta yaƙi ƙasashe, kamar Nana Asma’u Ɗanfodiyo wadda ta yi iyakacin ƙoƙari cikin al’amuran siyasa. Waɗannan mata sun yi iya ƙoƙari wajen ayyukan ci gaban ƙasa, kuma sun kafa mana tushe don matan da za su taso, amma saboda irin mulki na son danniyar hana mata ci gaba, mazanmu suka kashe ƙoƙarin da mata suke yi. Yau a cikin ƙungiyar nan ta matan Jam’iyyar Ceton Al’umma, mun dawo da mu tabbatar da wannan cin nasara.”

(“Sakatariyar Jam’iyyar PRP”, 1979).

A nan ta nuna cewa mashahuran mata irin su Sarauniyar Zazzau Amina, da Nana Asma’u ‘yar Shaihu Usmanu Ɗanfodiyo sun ba da gagarumar gudummawa wajen ginuwar siyasa da sha’anin mulki a ƙasar Hausa. Sun yi ƙoƙari wajen ayyukan ci gaban ƙasa kamar yaɗa ilimi da sauran muhimman al’amura, wanda ya zama madubi ga mata masu tasowa. Duk da haka maza sun hana mata bayar da irin tasu gudummawar, saboda son danne haƙƙi wanda ya hana a ga ƙoƙarinsu. Sun bayyana cewa, a cikin ƙoƙarin wannan ƙungiya tasu, za su tabbatar sun farfaɗo da irin wannan tsari na magabata, kuma su tabbatar an yi nasara.

 A siyasar jam’iyyu kusan tun da aka bai wa mata damar shiga da jefa ƙuri’a, duk abin da ya shafe su a cikin siyasar su matan ne suke gudanarwa. Alal misali, akan naɗa mata su shugabanci mata, lokacin yaƙin neman zaɓe ko tallata jam’iyya, duba da yanayin tsarin ƙasar Hausa, matan su ne suke shiga gida-gida wajen mata domin tallar jam’iyya da kuma neman ƙuri’arsu. Wannan ya bayyana a ciki littafin Tura Ta Kai Bango kamar haka:

“Haka kuma a sami mace ko kuma matan da za su jawo mata cikin jam’iyyar.”

(Katsina, 1983: 18).

Mata ne akan sanya musamman lokacin tallata jam’iyyu ko ‘yan takara su riƙa bi gida-gida don jawo ra’ayin mata a cikin siyasa, kamar yadda aka gani a cikin wannan misalin da yake sama, inda ‘yan jam’iyyar Sauyi suke shawarar sanya matan da za su bi mata har gidajensu domin jawo ra’ayinsu ga jam’iyyarsu. Irin wannan ya ci gaba har zuwa yau, inda akan riƙa amfani da mata ‘yan jam’iyya domin karkato hankalin mata zuwa ga jam’iyya ko ɗan takarar da ake buƙatar tallata masu.

Irin fafutukar da mata suka riƙa yi wajen ganin an ba su damar shiga cikin siyasa domin su ma a dama da su ya ci gaba da bayyana a cikin rubutaccen zube na Hausa. A cikin littafin Mace Mutum an fito da irin wannan fasalin, inda aka riƙa nuna cewa an hana mata damar shiga siyasa, don haka ya zama dole su tashi tsaye domin kada a ci gaba da barin su a baya, kasancewar su su ma suna da haƙƙi. Dubi abin da marubuciyar take cewa:

Aikin da zan ƙara shi ne zage damtse don nemo wa mata gurbinsu a siyasa Ba shugaban ƙasa ko matar shugaba ko na’ibi muke nema ko shugabar majalisa ba. Don ba albashi muke nema ko suna ba, muna neman kujerun duk abin da mata suka fi naƙasa ne a kansa. Kujerar kwamishina ko ministan ilimi dole mu nema ba za mu guji gwamnati ba don mu ma mutane ne.

(Majid, 2006: 415)

A nan ɗaya daga cikin ‘yan ƙungiyar ‘Ya’yan Godiya ne, wato Habiba, wadda ta samu ilimi fannin siyasa take bayanin yadda za su gudanar da fafutukar nema wa mata ‘yancin shiga siyasa domin su ma a dama da su. Ta nuna cewa za ta yin amfani da ƙwarewarta wajen nema wa mata gurbi a cikin siyasa, domin a tafi tare da su. A cikin misalin da yake sama, ta nuna cewa, ba burinsu ne su shiga siyasa domin neman kuɗi ko suna ba, sai dai domin share wa mata hawaye kan matsalolin da suka fi addabar su, kamar rashin ilimi. Wannan ne ya sa ta ce ya zama wajibi su miƙe su nemi kujerar kwamishina ko ma na ministan ilimi. Wannan ya nuna cewa, a baya ba a bai wa mata damar riƙe manyan muƙaman gwamnati ba, hakan ya sa suka tashi domin fafutukar neman sanya su cikin gwamnati domin su ma suna da irin gudummawar da za su bayar.

Tarihi ya nuna cewa, bayan bai wa mata damar jefa ƙuri’a da kuma damawa da su a cikin al’amuran siyasa a jamhuriya ta biyu, bincike ya nuna tun daga wancan lokaci zuwa jamhuriya ta huɗu, mata su ne suka fi jefa ƙuri’a da kashi sittin cikin ɗari, kamar yadda jaridar Leadership Hausa ta nuna:

“Kaso 60 na waɗanda suke kada ƙuri’a mata ne don haka yan da kyau mata su gane cewar juya akalar zaɓe na hannun mata. Saboda dayawan masu kada ƙuri’ar matan ne, amma da zarar an ci zaɓe da wuya ka ji wani abu da ya shafi rayuwar mata a matsayin ƙudurin da za a gabatar a majalisun ƙasar nan.”

(Usman, 2023).

A nan an nuna cewa mata su ne suka ɗauki kaso mafi tsoka na masu kada ƙuri’a a yau, domin sun ɗauki kaso sittin ciki ɗari na masu zaɓe. Wannan ya nuna cewa, mata suna da rawar da za su taka a cikin siyasa. Haka kuma duk da yawan kason da suka na masu zaɓe, matan ba su cika fitowa takarar siyasa ba idan aka kwatanta su da maza. In ma sun fito ba su cika yin nasara ba. Wannan ba zai rasa nasaba da koyarwar addinin Musulunci ba, wanda shi ne addini mafi rinjaye ga al’ummar ƙasar Hausa.

A yau matsayin mata a cikin siyasa a ƙasar Hausa ya wuce su tsaya ga jefa ƙuri’a ko ƙungiyoyin mata kaɗai, inda har ya kai mata sukan shiga takara don a zaɓe su, kuma sukan yi takara da maza a wasu matakai, ko kuma a ba su wasu muƙamai a siyasance waɗanda a da maza ake bai wa su. Alal misali, an samu mata da dama da suka zama kwamishinoni a wasu yankunan Arewacin Nijeriya, inda suka riƙe ire-iren waɗannan muƙaman a ma’aikatu da dama. An hasko irin wannan bayani a cikin littafin Mace Mutum kamar haka:

“A taƙaice na yanke shawarar yin takara tare da na’iba mace wadda za ku ba ni daga cikin ku. Sa’annan akwai kujerar ministoci guda huɗu da na ware domin bai wa mata ganin cewa a wannan sashi ne suka fi samun tawaya. Waɗannan kujeru su ne, ministar mata, ministar kiwon lafiya, ministar ilimi da ministar al’adu in kun yarda da wannan tsari sai mu yi a rubuce, mu haɗa ƙarfi mu nemi ƙuri’a, mu yi yaƙin neman zaɓe tare.”

(Majid, 2006: 505).

A cikin wannan misalin da yake sama, shugaban ƙasa ne yake tattaunawa da ‘yan ƙungiyar ‘Ya’yan Godiya ƙarƙashin jagorancin Habiba wadda ta kasance ‘yar siyasa a cikinsu, inda ya bayyana masu cewa ya yanke shawarar ɗaukar wadda za ta zama mataimakiyarsa a takarar shugaban ƙasa da zai sake tsayawa daga cikin mata ‘ya’yan wannan ƙungiyar. Baya ga kujerar mataimakiyar shugaban ƙasa kuma zai ba su muƙamin ministoci guda huɗu waɗanda suka haɗa da na ilimi da lafiya da al’adu da kuma harkokin mata, waɗanda a cewarsa mata sun fi buƙatarsu ne domin suna da tawaya a waɗannan ɓangarorin. Kamar yadda misalin ya nuna, duk da cewa an ba su gurbin mataimakiyar shugaban ƙasa da kuma ministoci, sai kuma ana ka nuna wa matan cewa za su fito a yi fafutukar neman ƙuri’a tare da su.

A baya bayan nan, an samu mataimakiyar gwamna a jihar Kaduna wadda suka tsaya takara kuma suka yi nasara. Haka kuma a Arewacin Nijeriya (Jihar Adamawa) mace ta yi takarar gwamnar jihar a jam’iyyar APC, kuma an kai-ruwa-rana da ita duk da ba ta yi nasara ba. An naɗa mata ministoci da dama daga ƙasar Hausa, waɗanda bayan samun ilimi mai zurfi suka shiga siyasa don a dama da su kamar yadda aka yi ta fafutuka a baya.

4.9 Takura Wa Abokan Hamayya        Hamayya a cikin siyasa tamkar gishiri ne a cikin miya, wanda muhimmancinsa akan ce in babu shi babu miya, wato miyar ba za ta yi daɗi ba. Siyasa musamman ta jam’iyya ba ta yiwuwa sai da hamayya tsakanin jam’iyyu. Kowace jam’iyya tana ƙoƙarin ganin ta yi nasara a kan abokiyar hamayyarta, idan kuma ta samu nasarar ɗarewa kan madafun iko to za ta yi duk yadda za ta yi domin ganin ta ɗore a kan mulki, kuma jam’iyyar hamayya ba ta samu dama ba.

Kamar yadda tarihi ya nuna, tun daga farkon kafa siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa, an samu jam’iyyun da aka kafa waɗanda suka yi hamayya da juna, wanda a ƙarshe wadda ta yi nasara wato NPC ta ɗare mulki, NEPU kuwa ta zama jam’iyyar hamayya wadda a kullum take ganin masu mulki ba su iya ba, ko kuma suna yin wasu abubuwa ba bisa tsari ko ƙa’ida ba. Irin wannan kuwa yakan zama al’ada ce ga kowane abokin hamayya domin ya nuna fagen gazawar abokin hamayyarsa. Jam’iyyun biyu sun ci gaba da nuna tsananin hamayya ga juna, inda ‘yan hamayya kan riƙa sukar gwamnati da masu riƙe da madafun iko ta kowace fuska. Ita kuwa gwamnati a nata ɓangaren sai ta riƙa amfani da ƙarfin mulki wajen yaƙar ‘yan hamayya ta hanyar ɗauri da tara da dai sauransu.

‘Yan NPC sun sha yin iƙirarin cewa sarki da alƙali duk nasu ne, don haka duk wanda ya faɗa masu magana marar daɗi za a miƙa wa alƙali ya yi masa hukunci, wanda ba su wuce duka ko ɗauri ko kuma tara ba. Wannan kuwa ya bayyana a cikin wasu rahotanni da suka fito a cikin jaridun Arewacin Nijeriya waɗanda suka riƙa bayyana yadda shari’o’in kotunan lardi suke gudana, musamman tsakanin mabiya jam’iyyar hamayya da ta masu masu mulki. A cikin wasu jaridun tun daga kanun labarai za a nuna irin mutanen da aka yi wa shari’a ko aka yanke wa hukunci. Dubi wannan misalin:

“Umaru Aska wanda ya yi jifa a Ofishin Alƙali ya samu ɗaurin wata ashirin da ɗaya. Wanda ya haddasa abin kuma har ya tuɓe zai bugi dogarin alƙali ya samu ɗaurin wata goma sha takwas.

Malam Abdu Tela kuma shugaban wannan taro ya sami wata takwas a gidan yari. Bayan waɗannan kuma an sami mutane takwas masu ɗaurin wata tara tara. Mutane ashirin da ɗaya kuma duk an ɗaure su wata bakwai bakwai.”

(“Shari’ar ‘yan NEPU a Katsina”, 1957).

A wannan rahoton na jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo, tun daga kanun labarin wato “Shari’ar ‘yan NEPU a Katsina” za a fahimci inda aka dosa, wato ba laifin ko masu laifin ake kallo ba, jam’iyyar siyasar da suke ra’ayi ake duba. In kuwa haka ne ashe da wuya komai gaskiya ɗan hamayya a iya yi masa adalci. Haka kuma, idan aka dubi yadda ake yanke masu watanni masu yawa a kan laifin da bai taka kara ba balle ya karya, za a fahimci irin halin da ‘yan hamayya suka shiga a wannan lokaci.

Hujjoji na tarihi sun nuna cewa, an samu lokacin da hatta alamar jam’iyyar hamayya ta NEPU idan aka ga wani da ita to kashinsa ya bushe, domin tana iya ja masa ɗauri a gidan kaso. A cikin wata wasiƙa da babban Sakarataren NEPU Malam B. M. Dzukogi ya aike wa Razdan na Katsina, ya yi ƙorafi tare da nuna ɓacin rai kan yadda ake takura wa ‘yan NEPU a Katsina, inda ya nuna cewa an ɗaure ‘yan jam’iyyar da dama don kawai sun sanya alamar NEPU a gidajensu. Dubi abin da aka tsakuro daga cikin wasiƙar:

“I am directed to protest to you against the recent order of the Katsina N. A. banning the display of this Party’s symbol in Katsina Division. This party Understands that already many of it’s members and supporters in Katsina have been convicted only for posting of our symbols in front of their houses. I am to point that our part’s symbol, a five pointed sta, has already been registered officially with the Federal Electoral Commission and we take a serious view of any attempt by which ever quarter to refuse the displaying of this symbol there is no reason why you should back the Katsina Native Authority to make an order banning the display of opposition party’s symbols during an election of great importance to the whole nation.”

Fassara:

“An umarce ni da in rubuta wannan takarda domin nuna ɓacin rai kan umarnin da hukumar En’e ta bayar na hana amfani da tutar jam’iyyarmu a yankin Katsina. Jam’iyyarmu ta fahimci cewa, akwai ‘ya’yanta da magoya bayanta da dama da aka ɗaure saboda kawai sun sanya tutar jam’iyyarmu a ƙofar gidajensu. Ina ƙara jaddada cewa, jam’iyyarmu mai alamar tauraro an riga an yi mata rajista da hukumar zaɓe ta ƙasa, don haka babu wani dalili da zai hana mu bayyana alamominta babu wani dalilin da zai sa ka goyi bayan Hukumar En’e ta Katsina domin sanya dokar hana bayyana alamar jam’iyyar hamayya a irin wannan lokaci na zaɓen da yake da matuƙar muhimmanci ga ƙasa baki ɗaya.”

  (Abba, 2000:95-96).

Idan aka duba nan za a ga cewa, ‘ya’yan jam’iyyar NEPU a Katsina sun riƙa kafa tutocin jam’iyyarsu a ƙofar gidansu domin nuna cewa su magoya bayan jam’iyyar ne, amma sai aka riƙa amfani da ƙarfin iko wajen hana su kafawa ta hanyar tsorata su da kamu da ɗauri a gidan kurkuku, domin dai a hana jam’iyyar tasu yin tasiri.

Kasancewar gwamnati ita take da iko a kan kotun alƙali da na sarki, wannan ya sa da zaran ‘yan hamayya sun yi laifi ko yaya sai a yanke masu tara mai girma ko kuma ɗauri a gidan kurkuku, wani lokacin ma akan haɗa masu da duka na nau’o’in azaba iri-iri har ma da kisa. Irin wannan ya fito a cikin wani jawabi da Malam Aminu Kano ya gabatar, inda yake cewa:

“Mun fara a matsayin samari matasa tsayayyu wajen yaƙi da zaluncin sarakunan Arewa sai muka tsaya wajen yaƙi da su, an ɗaure mu an doke mu an hana m,u abubuwa da dama yana da kyau mu san cewa duk wata hanyar tsanani da azaba da kashe waɗansu daga cikinmu ba zai wadatar ba, da yawa mutanenmu sun rasu irin su Aminu Sudawa da Ɗalha Ɗanƙasa da sauransu, ba za mu taɓa tsorata ba ”

(Jega da wasu, 2002: 59-60)

A nan idan aka duba za a ga cewa tun farkon fara siyasar jam’iyyu ba a bar ‘yan hamayya sun sha ruwa ba, domin kuwa daga wannan misalin da yake sama za a fahimci irin halin matsi da ƙuncin da aka jefa ‘yan hamayyar wancan lokacin wanda hakan bai sa sun karaya sun ja da baya ba. An nuna cewa an riƙa dukan ‘yan hamayya da gana masu azaba da ɗauri, inda har abin kan kai ga rasa rai. Duk wannan ‘yan hamayya sukan ɗora laifin a kan masu mulki ne, domin su ne suke da wuƙa da nama, kuma ba su son suka da ‘yan hamayya suke yi masu.

A wasu wuraren kuma akan samu inda a kan ɗai laifin da bai taka kara ya karya ba sai a kama abokan hamayya a ci su tara. Don kawai wani abu ya haɗa su da ɗan jam’iyya mai mulki, sai a bai wa abokin rigimar tasa ɗan jam’iyyar hamayya rashin gaskiya har a ci tararsa, kamar yadda ya zo a wannan misalin da yake ƙasa:

 “Mun samu labarin wai wani ɗan NEPU mai suna Ya’u mutumin Sumaila ta Kano, an yi masa tara fam 20 saboda ƙin halartar kotu. Daman dai an samu Ya’u Sumaila ne da laifin cin mutuncin wani ɗan NPC mai suna Ɗanladi na Alhaji Inuwa. Har wa yau kuma an sami Ya’u da laifin yin wasu abubuwa da za su haddasa fitina.”

(“An Yi Wa Ɗan NEPU Tarar €20”, 1960).

A nan kamar yadda jaridar ta ruwaito, an yanke wa ɗan NEPU tarar fam 20 ne don ya ci mutunci wani ɗan NPC, kuma an kira shi kotu ya ƙi zuwa, sannan aka ce wai kotu ta same shi da laifin ƙoƙarin haddasa fitina. Ire-iren waɗannan abubuwan na tarihi da suka shafi takurawa da ƙuntata wa ‘yan hamayya sun yi ta bayyana a cikin rubutaccen zube tun daga farkon siyasar jam’iyyu. Ba ma wai sai an taɓa ɗan jam’iyya mai mulki ne kaɗai irin waɗannan abubuwa na ƙuntatawa kan taso ba, akan iya amfani da kowane irin dalili ko ma babu gaira babu dalili matuƙar dai mutum ya kasance ɗan hamayyar gwamnati ne. Alal misali, a wata wasiƙa da aka aika wa jaridar Sodangi an nuna cewa ko maras lafiya ne ɗan jam’iyyar hamayya ba a ba shi kulawa a asibiti don kasancewarsa ɗan hamayya kamar yadda wannan misalin ya nuna:

“ ana nuna bambancin siyasa a asibiti, wato dai idan ɗan NEPU ya ji rauni ko ya kai mai ciwo sai Alhaji Rabi’u ya ƙi karɓa don shi mai shawara da kansa an yi masa haka.”

(“Majalisar Birnin Kano”, 1960).

A cikin wannan misalin an nuna cewa, asibitin gwamnati ne, su kuwa ma’aikatan gwamnati ce ta ɗauke su, kuma da umarninta suke aiki. Wannan ya sa ko dai ya kasance an bai wa ma’aikacin lafiyar umarnin cewa kada ya duba ‘yan hamayya, ko kuma shi ma da kansa ɗan hamayyar ne wannan ya sa ba zai duba su ba domin zafin hamayya. Marubucin wasiƙar ya ce idan ɗan NEPU ya samu rauni ko ba shi da lafiya ba a duba shi, domin shi hakan ya faru da shi a karan kansa. Idan aka duba, za a ga cewa, dangane da halin da ‘yan hamayya suka shiga, musamman a jamhuriya ta farko hali ne na takura, ko dai ka bi jam’iyya mai mulki, ko kuma ko yaya wata matsala ta haɗa ka da masu riƙe da madafun iko kashin ka ya bushe.

Ta wata fuskar kuma ‘yan jam’iyya mai mulki ta NPC suna ganin cewa, duk kumfar bakin da NEPU take yi cewa ana takura wa magoya bayanta da azabtar da su, su ne suke ja wa kansu, don haka ma suka ce ai ba ɗaure su ake yi ba, su ne suke ɗaure kansu, kamar yadda aka samu daga jaridar Sodangi cewa:

“ sau da yawa nakan ji ana faɗi a rediyo ko kuma nakan karanta a jaridu cewa mutanen NEPU suna ta yin surutai barkatai wai hukuma na yawan ɗaure su kuma tana yawan wulakanta su. Bisa gaskiya mutanen NEPU su ne suke ɗaure kansu suke kuma wulaƙanta kansu da kansu. Gama a Najeriya ba jam’iyyar da ke keta doka kamar jam’iyyar NEPU.

(“NEPU Ke Daure Kan Ta”, 1960).

A wannan misalin ‘yan NPC suna ganin cewa babu wata jam’iyyar da take keta doka kamar NEPU, duk kuwa wanda ya keta doka to ya kamata doka ta yi aiki a kansa. Akwai tsare tsaren gwamnati da dama da NEPU ba ta amince da su ba. Alal misali, biyan haraji da noman gandu da sauran wasu nauye-nauye da jam’iyyar NPC take da alhakinsu, abubuwa ne da jam’iyyar hamayya take yaƙi da su ƙwarai. A ganin su bai kamata talaka ya biya haraji a ƙasarsa ba, kuma in har za a nome wa sarki gonarsa, to ya kamata ya ɗauki ‘yan ƙwadago ne su yi masa ya biya su ba wai a sa mutum ya yi na dole kuma babu ko sisi da za a biya shi ba, hasali ma, sai dai bayan talakawa sun gama nome gandun sarki su je fada su yi gaisuwa su yi godiya su koma gidajensu. Duk waɗannan NEPU tana yaƙi da su. Wannan ya sa ake ganin cewa sun raina hukuma, don haka idan suka shiga hannu ba za su ji daɗi ba.

Tarihi ya nuna cewa, lokacin da Turawan mulkin mallaka suka shigo ƙasar Hausa sun bai wa sarakunan ƙasar ƙarfi sosai ta hanyar haɗa kai da su wajen danne talaka, kamar yadda Malam Aminu Kano ya bayyana a cikin jawabinsa:

“ a lokacin da Turawan mulki suka zo sun ɗaga darajar sarakuna a kan ta kowa suka yi amfani da su wajen rashin gaskiya ”

(Jega da wasu, 2002: 59-60)

Ke nan, Turawa sun yi amfani da sarakuna wajen cimma burinsu a ƙasar Hausa, ta hanyar amfani da ƙarfin faɗa-aji da sarkuna suke da shi da kuma ƙarfin iko suka shimfiɗa ikonsu yadda suka so. Kasancewar jam’iyyar NPC ita ce take mulki, su kuma Turawa su ne a sama wajen bayar da umarni, sannan kuma duk sarakuna suna karɓar umarni ne daga Turawa, sannan kuma sarakunan su ne ‘ya’yan jam’iyyar ta NPC, wannan ya sa suke da ƙarfin iko a gargajiyance da kuma a siyasance. Da wannan dalilin ne ya sa sarakuna ba su bar ‘yan hamayya sun shaƙata ba, musamman idan aka samu shari’a ta haɗa su da mai goyon bayan jam’iyya mai mulki. A cikin wanna misalin da yake biye za a ga irin wannan yanayin ya fito a cikinsa. Ga misalin:

“Kuma sai ga shi sarakunan NPC sun fito sosai suna nuna ƙiyayyar su ga jam’iyyar hamayya sun dage suna yi wa NPC aiki sosai ta wajen daure abokan hamayya da danne su wajen sharia da nuna bambanchi da laftawa talaka harajin da ya fi karfinsa da dai dukkan abubuwan da bai kyautu wanda yake sarki ba ya yi.”

(Kano, 1961).

A shekarar 1961, jaridar Daily Comet ta buga wannan wasiƙar da aka tsakuro a sama, inda a ciki aka bayyana cewa sarakuna sun nuna ƙarara cewa jam’iyyar NPC mai mulki suke yi, babu ruwansu da jam’iyyar NEPU. A ganin abokan hamayya ai sarakunan ma aiki suke wa jam’iyya mai mulki ta hanyar ɗaure abokan hamayya da danne masu haƙoƙƙinsu a wajen shari’a ta hanyar nuna bambanci tsakanin ɗan jam’iyyarsu da wanda ba ɗan jam’iyyarsu ba, maimakon su yi shari’a bisa adalci ba tare da nuna sani ko sabo ba.

Har ila yau, a cikin wasiƙar tasa ya nuna cewa, sarakunan suna sanya wa talaka haraji mai yawa da ya fi ƙarfinsa, wanda yake ganin hakan bai dace ba. A cewarsa a matsayinsu na sarakuna iyayen al’umma, ya kamata su kasance suna tare da kowane ɓangare ba tare da nuna bambanci ba. Wannan bambancin da suke nunawa ne ma ya sa ya kira su da sarakunan NPC, maimakon sarakunan gargajiya.

A wata tattaunawa da aka yi da fitacciyar ‘yar siyasa Hajiya Maryam Inuwa wadda aka fi sani da Asabe Reza ta bayyana yadda aka riƙa gallaza masu don kawai suna goyon bayan jam’iyyar hamayya. Ta bayyana yadda aka yi ta ɗaure ta a gidan yari don kasancewarta ‘yar Jam’iyyar NEPU, da irin yadda aka riƙa azabtar da su. Dubi abin da jaridar Aminya ta ruwaito:

“Wallahi duk kurkukun da ke kewaye da garuruwan nan namu babu wanda ba a taɓa kai ni ba. Daga caji ofis a kai ka kurkuku, daga kurkuku a kai ka basikel wanda ake kwana a tsaye Ba mu da wata dama a lokacin NEPU sai shan duka da ɗaukar kashi a ka ”

(Ayuba, 2010).

A cikin bayaninta kan irin ƙalubalen da ta fuskanta kasancewarta ‘yar jam‘iyyar hamayya ta NEPU, ta bayyana cewa duk kurkukun da ke kewaye da su babu wanda ba a kulle ta a ciki ba. wani lokaci ba a ma batun zuwa kotu, daga an kama ɗan hamayya an kai shi ofishin ‘yansanda sai a wuce kurkuku a ɗaure. A kurkukun ma har akan kai su ɗakin da ake cewa ‘basikel’, wanda ba zama balle kwanciya, a tsaye mutum zai kasance duk daɗewar da zai yi a cikin wannan ɗakin. Duk wannan azabar don sun kasance ‘yan hamayya ne.

Baya ga ɗauri a gidan kurkuku, akan lakaɗa wa ɗan hamayya duka a wancan lokacin kan abin da bai kai ya kawo ba. Kamar yadda wannan ‘yar siyasa ta faɗa kamar haka:

“Akwai wani mutum maɗinki da aka samu labarin ɗinkin rigunan da ya yi wa Malam Aminu Kano, sai da aka je har zauren gidansa aka kama shi, aka yi ta duka kamar za a kashe tun daga garin Ringim za a ɗauro mutum, a yi masa ƙuƙumi, sannan a kawo shi gidan kurkukun Kano a ɗaure. Za ki ga mutum bai aikata wani laifi ba, don kawai ya faɗi kalmar sawaba, sai a ɗaure shi a jikin doki, ɗan doka da ke kan dokin ya riƙa jan sa da igiya mun sha tafiyar ƙafa ga duka. A yanzu haka jikina duk yanka ne na wajen damben rigima da gwagwarmaya. Kai har yanzu akwai tabo a kaina ”

(Ayuba, 2010).

Idan aka dubi wannan misalin za a ga cewa, a cikin tsawon tarihin siyasar jam’iyyu, ‘yan hamayya sun sha tsanani a wajen masu mulki musamman a jamhuriya ta farko, wanda ya shafi kowane irin nau’i na azaba da ɗauri da duka kamar yadda Asabe Reza ta ambata cikin bayananta. A wancan lokacin babu wata alaƙa da za ta haɗa ka da wani abu da ya shafi NEPU in dai kana so ka zauna lafiya. Ko da sana’a kake yi ba za ka yi wa ɗan NEPU ba, sai dai in ra’ayinta kake yi. Kamar dai yadda ta ce tela ya yi wa Malam Aminu Kano ɗinki, hakan ya sa aka zo har gida aka yi masa duka kamar za a kashe shi. A wancan lokacin, ambaton kalmar sawaba kaɗai ya isa ya sa a maka tsattsauran hukunci.

Daga bayanan da aka gani za a lura cewa, ba maza ne kaɗai suka fuskanci irin wannan takurawa daga jam’iyya mai mulki ba, mata ma sun ɗanɗana. Su ma sun yi gwagwarmaya a nasu ɓangaren wajen ganin sun samu dama a siyasance da kuma wasu fannoni na zamantakewar rayuwa ta yau da kullum.

Irin wannan takura da ake yi wa ‘yan hamayya ta ci gaba har zuwa jamhuriya ta biyu. An samu wasu misalai irin waɗannan da suke nuna cin zarafin ‘yan hamayya da kuma take masu haƙƙi wanda jam’iyyar hamayya ta PRP ta koka kan yadda ake kama ‘ya’yanta ana tsarewa ba tare da wata ƙwaƙƙwarar hujja ba.

 “ NPN yanzu ta ƙyanƙyashe sabuwar maƙarƙashiya, mun fahimci cewa sun rubuta wasiƙa zuwa Legas suna zargin magoya bayanmu da abubuwa na ƙarya, har waɗansu daga cikin mutanenmu irin su Yusuf Kududdufawa an kama su daga umarnin gwamnatin jiha, saboda wannan dalili na rubuta wasiƙa zuwa ga shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo domin a sako mana mutanenmu, Muhammadu Abubakar Rimi da Isa Ibrahim ne suka kai wasiƙar.”

(Jega da wasu, 2002:29-30).

Malam Aminu Kano ya bayyana cewa, jam’iyyarsu ta PRP ta gano wata maƙarƙashiya da jam’iyyar NPN take shirya masu, wanda ake kama ‘ya’yanta bisa zarge-zarge marasa tushe ana ɗaurewa tun ma kafin a kai ga gudanar da zaɓe, domin a karya lagonsu. Wannan ya sa Malam Aminu ya rubuta wa shugaban ƙasa wasiƙa don ya sanar da shi kokensu.

Ire-iren waɗannan abubuwan da suka shafi takura wa abokan hamayya ya zama ruwan dare a cikin al’amuran siyasar Arewacin Nijeriya, kuma yawanci ‘yan siyasar da suke da ɗaurin gindin gwamnati ne suke samun wannan damar domin su hana abokan hamayyarsu rawar gaban hantsi. An samu tabbacin irin wannan salon siyasar a cikin tarihin ginuwar siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa, ashe ba abin mamaki ba ne idan aka samu marubutan ƙagaggun labarun Hausa sun tsara labarin da ya fito da irin wannan fasalin. Alal misali, an nuna yadda aka riƙa kama magoya bayan jam’iyyar Sauyi ana ɗaure su ba tare da wani ƙwaƙƙwaran laifi ba, kamar yadda ya bayyana a cikin littafin Tura Ta Kai Bango kamar haka:

“ ba wannan kawai ke damun su Ta-gyare da Hassan ba, sai magoya bayansu da ake ta kamawa ana jefawa kurkuku a bisa raunannun dalilai, shi kansa Hassan an taɓa kulle shi kwana biyu a Kabobi da sunan cewa ya yi lacca ba tare da izini ba. Jiya kuma aka sallamo Garba bayan wata uku a kurkuku da zargin cewa ya ingiza wasu mutane sun tayar da hankali shi da abokanensa a nan Ƙoramu.”

(Katsina, 1983: 70).

Idan aka dubi wannan misali za a ga cewa, tamkar hoto ne na siyasar jamhuriya ta farko da ta biyu, domin kuwa kamar yadda aka riƙa kama mutane ana ɗaure su a kurkuku bisa dalilan da ba su kai na ɗauri ba, haka ma aka nuna yadda su Hassan da Ta-gyare suka riƙa nuna damuwarsu kan hakan. A ganinsu an takura masu ne don kawai suna hamayya da jam’iyyar Riƙau. An bayyana cewa shi kansa Hassan a matsayinsa na shugaban jam’iyyar Sauyi na yankinsu an taɓa kama shi an kulle da sunan ya yi lacca ba tare izinin hukuma ba, sai abokinsa Garba shi ma an ɗaure shi wata uku bisa laifin tunzura wasu mutane a lokacin da ya yi wani jawabi shi da abokansa. Irin wannan idan aka duba hotunan abubuwan da suka riƙa faruwa ne a cikin tarihin ginuwar siyasar Arewacin Nijeriya.

Bugu da ƙari a wani misalin an nuna yadda ake ƙulla wa ‘yan hamayya sharri da cewa sun raina hukuma ko sun raina sarakuna, sai a kai su kotu a yanke masu tsattsauran hukunci, kuma babu wanda zai ce an yi ba daidai ba, sai dai su ‘yan hamayyar su nemi hanyar da za su fitar da fushinsu ga al’umma domin a san halin da ake ciki. Dubi abin da marubucin littafin Tura Ta Kai Bango yake cewa:

“ wani mutum da ake kira Buwai da ya yi wa su Alhaji galari, nan da nan aka ƙulla masa sharrin cewa wai ya zazzagi maigari. Da haka alƙali ya ɗaure shi wata biyu. Ga shi kuwa da mata da ‘ya’ya shida.”

(Katsina, 1983: 51).

Kasancewar su Alhaji Kaukai ‘yan jam’iyyar Riƙau, wani abu ya haɗa su Buwai ɗan jam’iyyar Sauyi har suka yi tankiya, sai suka ƙulla masa cewa ya zagi maigari. Bai zagi maigari ba, ƙage suka masa Haka kuma alƙali bai yi la’akari da cewa yana da iyali da ‘ya’ya shida ba, ko kuma tunanin wa zai kula da su ba, ya yanke masa hukuncin ɗaurin wata biyu a gidan yari.

Irin wannan ya biyo tsawon tarihi har zuwa siyasar jamhuriya ta huɗu. A jamhuriya ta huɗu abin ya sauya fasali, domin bayan an yi amfani da wannan salon na takura wa abokan hamayya, ta hanyar kamu da ɗauri da dai sauran abubuwa, sai kuma aka yi amfani da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Zambar Kuɗaɗe (EFCC) don ta zama wata hukuma da ake firgita ‘yan hamayya ko kuma duk wani wanda yake takun saƙa da jam’iyya mai mulki. Akan tura ma’aikatan hukumar da sunan binciken almundahanar kuɗi don a kama mutum a ɗaure ko kuma a hana shi yin wani amfani mai ƙwari musamman idan kakar zaɓe ya zo. Domin tabbatar da wannan batu, dubi abin da aka tsakuro daga jaridar Aminiya:

“Tuni dai wasu suka masu fashin baƙi suka fara hasashen cewa, Gwamnan ya canja sheƙar zuwa jam’iyyar PDP ne saboda ya sami mafaka daga tuhumar da hukumar nan mai yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC).

(“Na Bar ANPP Ne Saboda”, 2007).

Gwamna Adamu Aleiro na jihar Kebbi ɗan jam’iyyar hamayya ta ANPP ne wanda hukumar hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙi zagon ƙasa wato EFCC ta tuhume shi da almundahana a gab da ƙarshen wa’adin mulkin shugaba Obasanjo a shekarar 2007. Kasancewarsa ɗan jam’iyyar hamayya, kuma hukumar ta tuhume shi ne lokacin da aka fara shirin babban zaɓen ƙasa. Ana ganin cewa hukumar ta yi haka ne domin ta tsorata a mastayin ɗan jam’iyyar hamayya. Kwatsam, sai aka ji ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar PDP mai mulki. Wannan ya sa aka fara tunanin ya yi hakan ne domin guje wa binciken da hukumar za ta yi masa, inda ya shiga ƙarƙashin inuwar jam’iyya mai mulki domin samun mafaka. A wancan lokacin an yi zargin cewa, gwamnati tana amfani da hukumar a matsayin karen farauta, domin takura wa ‘yan hamayya.

Wata hujja da ta nuna cewa masu hamayya da gwamnati ne ake takura wa ta hanyar amfani da hukumar EFCC ita ce, batun da shugaban majalisar dattawa ya yi na cewa ya kamata fadar shugaban ƙasa ta tsame hannunta daga al’a muran hukumar. Domin kuwa tsoma bakinta zai iya gurgunta dimokuraɗiyyar ƙasar. Ga abin da ya ce:

“Shugaban majalisar dattawa ya yi Allah wadai da yunƙurin da fadar shugaban ƙasa ke yi na dakushe ‘yancin da hukumar EFCC ke da shi, domin kuwa a tsarin dimokuraɗiyya irin wannan hukumar dole ne ta zama mai cin gashin kanta ba ta zama a ƙarƙashin fadar shugaban ƙasa ba dokar da ta kafa hukumar EFCC ba ta amince wa hukumar ta miƙa sunayen mutanen da take zargi ga fadar shugaban ƙasa ba, sai dai ta gabatar da su gaban kotu domin a hukunta su Matuƙar yaƙin da ake yi da cin hanci da rashawa zai karkata ne ga waɗansu ‘yan siyasa da ake zargi da cin hanci ba duka waɗanda ake zargi ba, ‘yan Nijeriya za su ci gaba da nuna shakku a kan adalcin EFCC ɗin.”

(“An Baddala Sunayen da EFCC ta Fitar”, 2007).

Gwamnatin Obasanjo ta yi amfani da wannan hukuma ƙwarai da gaske domin samun goyon baya ko ta halin ƙaƙa daga ‘yan jam’iyyarsa da kuma ‘yan hamayya. Domin kuwa a wannan lokacin duk wanda ya nuna ba ya tare da gwamnati ko kuma yana hamayya da ita sai a tura irin waɗannan hukumomi su bincike shi. Kamar yadda wannan misalin da yake sama ya nuna, Hukumar EFCC ta fitar da sunanyen waɗanda take zargi da cin hanci, maimakon a miƙa su kotu ta hukunta su, sai aka kai sunayen fadar shugaban ƙasa. Shugaban majalisar dattawa ya nuna cewa hakan ba daidai ba ne, domin ya saɓa wa dokar da kafa hukumar. Ya bayyana cewa in dai ba a daina zaɓen ‘yan siyasar da za a tuhuma a bar wasu ba, bayan kuwa dukkansu ana zargin su, to hakan zai iya ci gaba da karya guiwar ‘yan hamayya a kan adalcin hukumar. Wannan tsoma bakin da fadar shugaban ƙasa ta yi a kan aikin hukumar ya sa da dama cikin masu hamayya da gwamnati suka yi biyayya ba don suna so ba, wasu kuma suka ja bakinsu suka yi shiru, musamman waɗanda suke riƙe da muƙamai ko kuma suka taɓa riƙewa a baya, domin gudun kada allura ta tono garma.

An ci gaba da bin irin wannan hanya ta takura wa abokan hamayya har zuwa shekarar 2010, lokacin ana gab da kakar zaɓe na shekarar 2011. An riƙa amfani da hukumar EFCC wajen tuhumar duk wani da aka san mai faɗa a ji ne a siyasance, wanda kuma zai iya kawo wa jam’iyya mai mulki ta PDP matsala a siyasance. A lokacin da aka fara tunanin haɗewar jam’iyyu a shekarar 2010 don su ƙalubalanci jam’iyyar PDP a zaɓen 2011 ma an samu irin wannan fasali na takura wa abokan hamayya. Dubi wannan misalin:

Kamun da aka yi wa Bafarawa, bayan shekaru biyu da saukarsa daga kujerar mulki da kuma shari’ar da ta biyo baya a babbar kotun jihar Sakkwato, musamman a daidai lokacin da ya fito fili ya funjima on gama kan jam’iyyun hamayya wuri ɗaya, al’amari ne da masu kula da al’amuran yau da kullum ke gani a wani abu na taɓarɓarewa ga Hukumar ta EFCC, ta yadda ta zama karen farautar Jam’iyyar PDP wajen wulaƙanta da kuma ɓata sunan mutanen da gwamnati ke ganin su a matsayin ‘yan hamayya.”

(“Hukumar EFCC Da Tsoffin Gwamnoni”, 2010).

A cikin wannan misalin, an alaƙanta kamun da hukumar EFCC ta yi wa tsohon gwamnan jihar Sakkwato a shekarar 2010 a matsayin hamayyar siyasa. An nuna cewa, ba a kama shi ba sai bayan da shekara biyu da sauka daga kujerar gwamnan jihar, kuma sai da ya fito fili ya nuna aniyarsa ta haɗe kan jam’iyyun hamayya domin su tunkari jam’iyya mai mulki a zaɓen shekarar 2011. Daga nan sai aka ji hukumar EFCC ta kama shi tare da tuhumarsa kan almundahana. Wannan dalilin ya sa al’umma sun ci gaba da yi wa hukumar kallon wadda ake amfani da ita wajen takura wa ‘yan hamayya da ɓata masu suna a siyasance.

Tarihi ya nuna cewa, a lokacin da rikice-rikice suka dabaibaye jam’iyyar PDP, wasu suka riƙa ficewa daga cikinta suna komawa jam’iyyun hamayya. Wasu daga cikin ‘yan jam’iyyar PDP ɗin da ba su fita ba, amma suka riƙa nuna kurakuran jam’iyyar, sai aka yi masu barazana da hukumar ta EFCC idan ba su kame bakinsu ba. jaridar Aminiya ta kawo wannan bayanin kamar haka:

“Gwamnan jihar Jigawa Alhaji Sule Lamiɗo ya ce sabon yankan rake a siyasa za a firgita ba irinsu da suka goge a fagen siyasa ba, inda ya ce babu wanda zai yi musu barazana da EFCC don su daina faɗin gaskiya.”

(Majeri, 2013).

A nan gwamnan ya nuna yadda aka riƙa masu barazana ne da hukumar ta EFCC don suna faɗin gaskiya a kan jam’iyyarsu ta PDP. Ya ce su ba ‘yan koyo ne a siyasa ba, ƙwararru ne kuma gogaggun da barazana ko tsoratarwa ba za ta yi tasiri a kansu ba. Don haka ba za su daina faɗin gaskiya dangane da jam’iyyar ba. Idan aka duba za a ga cewa, a jamhuriya ta huɗu ba ma ‘yan hamayya kaɗai ba, duk wanda ba zai yi wa gwanati biyayya ido rufe ba, ma’ana ba tare da yana ganin kuskuren yana nunawa don a gyara ba, to gwamnatin za ta sa ƙafar wando ɗaya da shi. Za ta yi amfani da hukumar EFCC don a dankwafe shi, ko kuma a hana shi motshi baki ɗaya a siyasance.

Irin wannan ya ci gaba har zuwa lokacin da jam’iyyar hamayya ta APC ta karɓi ragamar shugabancin ƙasar, shugaba Buhari ya yi ƙoƙarin yaƙi da rashawa kamar yadda gwamnatin nasa ta ayyana. Kamar dai yadda siyasar ta gada, yawanci irin wannan yaƙin kan ƙare ne a kan ‘yan hamayya, domin su ne za su zama waɗanda za a riƙa farauta da takura da kuma firgitarwa. Wannan ya sa ma duk wanda yake so ya tsira daga irin wannan matsin na gwamnati, sai ya koma jam’iyyar gwamnati a tafi tare da shi.

4.10 Yarfe Ga Abokan Hamayyar Siyasa

Ƙage da Ƙazafi kalmomi ne da suke da makusantan ma’anoni da juna ko ma a ce ma’anarsu guda, sai dai kowacce da asalinta, kuma ana iya amfani da wata a maimakon wata. Kalmar Ƙage Bahaushiyar kalma ce, tana ajin suna ne mai ɗauke da jinsin namiji. Tana nufin a ce mutum ya yi abin da bai ji ba, bai gani ba ko kuma a ƙulla masa sharri (CNHN, 2006: 273). Ƙazafi kuwa kalma ce da take da asali daga Larabci wato ‘Ƙazaf’, wadda Hausawa suka ara suka yi mata ƙarin -i a ƙarshenta ta koma ƙazafi. Ma’anar kalmar a Hausa da Larabci duk abu guda take nufi. Kalmar Ƙazafi suna ne mai ɗauke da jinsin namiji, kalmar tana nufin laƙa wa mutum laifi ko yi masa sharri (CNHN, 2006: 279).

Kalmar Yarfe Bahaushiyar kalma ce, tushen kalmar shi ne [yarf-], da aka yi mata ɗafin [-a] a ƙarshenta sai ta koma [yárfà] wadda take kalmar aikatau ce mai ɗauke da karin sautin sama-ƙasa, daga gare ta ne aka samo kalmar [yarfe] bayan an shafe wasalin ƙarshe [-a] aka yi wa tushen kalmar ɗafin [-e] a ƙarshenta, sai ta koma [yárfé] wanda ya sa karin sautinta ya sauya zuwa sama-sama maimakon sama-ƙasa a kalmar ‘yarfa’, sai kuma sauyawar karin sautin ya haifar da sauyawar ajin nahawun kalmar daga aikatau zuwa suna[9].

Ƙamusun CNHN (2006: 479-480) ya bai wa kalmar yarfe ma’anoni guda biyar kamar haka:

i- Maka ko daka

ii- watsa

iii- ƙaga

iv- aika da, musamman na zagi

v- amfani da hannu don share wani abu.

Daga cikin waɗannan ma’anonin, ma’ana ta biyu da ta uku ne suke da alaƙa kai tsaye da wannan aikin, domin a ƙarƙashin ma’ana ta biyu an ba da misali da ‘na watsa masa taɓo’ kuma duk abin da aka watsa masa taɓo to an ɓata wannan abin, domin zai nuna alamomi a wurare da dama a jikinsa. Ita ma ma’ana ta uku daga cikin ma’anonin an ba da misali ƙarƙashinta kamar haka: ‘Sun ƙaga masa laifi’. Ke nan kalmar yarfe tana nufin ƙaga wa wani mutum wani laifi kamar yadda aka bayyana ta a sama. Idan aka ƙaga wa wani mutum wani laifi wanda bai ji ba, bai gani ba yakan zubar masa da ƙima ko ya rage masa ƙima a idon mutane. Idan magoya bayansa ne sai a samu wasu su dawo daga rakiyarsa.

Don haka, kalmar tana nufin a sanya wani baƙon abu a jikin wani ta yadda zai iya yin ɗigo-ɗigo a jikinsa har ya fito a gani. Alal misali, kamar a samu farar tufa a yarfa mata manja ko wani baƙin mai wanɗa zai zama an ɓata wannan tufar. Manufar yarfe a siyasance ita ce ɓatawa, kamar yadda aka yarfa wa wannan farar tufar wasu launuka don a ɓata ta.

Kalmomi biyu na farko wato ‘ƙage’ da ‘ƙazafi’ dukkansu kalmomi ne da ake amfani da ma’anarsu a cikin harkokin yau da kullum, kuma in aka yi amfani da su suna iya dacewa da ko wa aka jefa da su. Akan iya cewa an yi wa wane ƙage, ko an yi wa wane ƙazafi, amma kalmar yarfe ta kasance kalma ce da ta keɓanci siyasa. A siyasance ba a cewa an yi wa mutum ƙage ko ƙazafi, sai dai a ce an yi masa yarfe[10]. Ke nan, daga bayanan da suka gabata za a fa himci cewa, kowane yarfe, ƙage ko ƙazafi ne, amma ba kowane ƙazafi ko ƙage ne yarfe ba.

Yarfe wani yanayi ne da abokan hulɗar siyasa sukan ɗauko wani abu su ɗora wa wani wanda bai ji ba bai gani ba don kawai a ɓata shi a siyasance.

Yarfe zai iya kasancewa a tsakanin ‘yan jam’iyya guda masu hamayya da juna, waɗanda sukan ƙirƙiri wani abu su jingina shi ga wani abokin hulɗar siyasarsu na jam’iyya guda don su musguna masa. Akan kuma samu yanayin da jam’iyya guda ake, amma ana ƙarƙashin wani uban gida na siyasa, sai a yi wa juna yarfe don neman samun gindin zama a wajen iyayen gidan nasu. A wani gefen kuma yakan iya zama ba jam’iyya guda ‘yan siyasar suke ba, sai a ƙirƙiri wani abu a jefa wa abokin hamayya don mutane su dawo daga rakiyarsa, don neman samun nasara a kan jam’iyyar da ake hamayya da ita[11]. Alal misali an ga yadda aka riƙa yamaɗiɗi da wani batu da ake cewa wai ‘ɗan takarar shugabancin Nijeriya a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya ce, Allah ba ya karɓar addu’ar talakawa’, amma kuma duk wanda aka tambaye shi yaushe ya faɗa? A ina ya faɗa? Babu wanda zai iya kawo hujjar muryarsa, ko hoto mai motsi, ko kuma a rubuce, sai dai a ce kawai haka aka ce. Wa ya ce? Shi ma a nan sai kuma a fara ‘yan kame-kame. Ma’ana dai yarfe ne aka yi masa wanda kuma ya yi tasiri ƙwarai a zukatan al’ummar ƙasa. Akwai ire-iren waɗannan misalai da dama da aka riƙa samu a cikin siyasar jam’iyya, sai dai waɗanda wannan bincike ya taƙaita a kansu su ne waɗanda aka samu a cikin rubutaccen zube kaɗai ban da na baka.

A taƙaice, kalmar Yarfe bisa fahimtar wannan aikin tana nufin faɗin wani abu da bai tabbata ba, tare da danganta shi da abokan hamayyar siyasa ko jam’iyyar siyasa ko ɗan siyasa, wanda zai sa jama’a su ga baƙinsu.

Jam’iyyun siyasa sun shahara ƙwarai wajen yi wa juna yarfe, kasancewar kowacce tana so ta ɗaukaka a kan abokiyar hamayyarta, wannan ya sa abokan hamayyar siyasa sukan riƙa ƙaga aibu ga ‘yan’uwansu suna faɗa wa jama’a don su guje su, ko da kuwa daga baya za a fahimci cewa wannan abin da aka danganta jam’iyyar ko ɗan siyasar da shi ba gaskiya ba ne.

A lokacin da aka fara siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa, jam’iyyu biyu ne aka kafa a ƙasar Hausa kuma suka yi tashe, sannan kuma dukkansu sun yi gwagwarmayar neman mulki, inda ɗaya ta yi nasara, ɗaya kuma ta zama jam’iyyar hamayya. Al’adar siyasa ce dole in za a tallata jam’iyya ko ɗan takara, bayan an yi amfani da yabon abin da ake tallatawa, wajen faɗin ingancinsa, sai kuma a kushe abokin haɗinsa ko abokin hamayyarsa domin a sake fito da hasken abin da ake tallatawa ya fito fili, al’umma su karɓe shi, su kuma guji wanda ba shi ba. A wurin wannan kushen ne ake samun yarfe ga jam’iyyun siyasa.

Tun daga jamhuriya ta farko an riƙa samun irin waɗannan bayanai a cikin rubutaccen zuben Hausa, inda jam’iyyu biyu masu hamayya suka yi ta yi wa juna yarfe a tsakaninsu. A wasu lokutan ma ba tsakanin jam’iyyun kaɗai yake tsayawa ba, har ma da ‘yan jam’iyya, inda akan kama suna, wani lokaci kuma sai dai a yi ishara. Jam’iyyar NEPU da Jam’iyyar NPC sun yi suna wajen irin wannan siyasar, wadda za a iya cewa daga gare su ne tsarin siyasar jam’iyya ya ginu a ƙasar Hausa. Irin waɗannan misalai na yarfe sun fito a cikin rubutaccen zube na Hausa, waɗanda suka yi nuni da irin wainar da aka toya a fagen siyasar Jam’iyyu a wancan lokacin. Daga bisani, an ci gaba da samun yarfe a cikin rubutattun ayyukan zuben Hausa waɗanda suka ci gaba da fito da hoton yadda siyasar jam’iyyu ta gudana har zuwa yau.

Dangane da wannan bincike an raba yarfen siyasa zuwa gida uku, sannan an ɗauki kowanne an yi bayaninsa tare da misalan da suka dace kamar haka:

4.10.1 Yarfe Na Addini

A fahimtar wannan aiki, addini hanyar rayuwa ce ta ɗan Adam, wadda ake bi ta hanyar yarda da saudaukar da kai da kuma bauta domin samun biyan buƙata ko kariya ko kuma tsira a gaban Ubangiji.

A siyasance addini yana taka muhimmiyar rawa wajen neman shugabanci da kuma tafiyar da shi, kasancewar shi ne hanyar rayuwar da ‘yan Adam suke bi kuma suka amince da shi. Ita kuwa siyasa ta kasance ginshiƙi a rayuwar ɗan adam wadda yake gudanar da ita da saninsa ko ba da saninsa ba. Wannan ya sa ‘yan siyasa suka riƙa amfani da addini wajen cimma burikansu na siyasa ta fuskoki da dama.

Yarfen siyasa yana daga cikin abubuwan da aka riƙa amfani da addini wajen gudanar da shi, inda aka riƙa amfani da wasu abubuwa na addini domin daƙile tafiyar abokan hamayya. Kasancewar addini yana da tasiri ƙwarai a wajen masu shi ko mabiyansa akan samu wasu ‘yan siyasa su yi amfani da shi wajen shafa wa abokan hamayya wani mummunan abu wanda zai sa a ga baƙinsu, a ƙyamace su.

Tarihi ya nuna cewa ‘yan siyasa sun riƙa yi wa abokan hamayyarsu yarfe ta hanyar amafani da addini kamar yadda Paden (1973: 122) ya kawo bayanai a kan irin rikice-rikicen da aka riƙa samu a tsakanin mabiya aƙidun Tijjaniyya da Ƙadiriyya har suka riƙa yi wa juna yarfe kamar haka:

 The Sultan of Sakkwato later denied that the riot was between Qadiriyya and Tijaniya, throughout the country and more especially in big towns, live amicably without interference in each other’s religious belief. He referred to the rioters as ‘Yan Wazifa’ who are going beyond their bounds to them even prayer five time a day was forbidden.

Fassarar marubuci:

Sarkin Musulmi ya ƙaryata batun rikicin da ya faru tsakanin Tijjaniyya da Ƙadiriyya, waɗanda suke zaune lafiya a duk faɗin ƙasar musamman ma a manyan garuruwa, inda ya bayyana cewa waɗansu masu neman wuce gona da iri ne; masu cewa sallah biyar a wuni haramun ne, waɗanda ake kira ‘yan wazifa suka tayar da rikicin.

Tarihi ya nuna ce, a farkon kafuwar siyasar jam’iyyu, aƙidun Addinin Musulunci sun taka muhimmayar rawa a a cikin siyasar ƙasar Hausa, duk kuwa da cewa shaihunnan waɗannan ɗariƙu ba ‘yan siyasa ne ba, kuma ba su da alaƙa da ita, amma an yi amfani da darajarsu da na aƙidunsu a cikin siyasar wancan lokacin, inda suka kasance tamkar ma su ne jam’iyyun a karon farko. Idan aka yi la’akari da magoya bayan kowace jam’iyya za a ga cewa akasarinsu mabiya aƙida guda ne, duk da cewa akan samu wasu ‘yan kaɗan da suke da bambancin aƙidar. Alal misali, Jam’iyyar NPC ta su Ahmadu Bello Sardauna kaso mafi tsoka na mabiyanta ‘yan Ƙadiriyya ne, haka ma dukkan manyan masarautun ƙasar Hausa ɗariƙar Ƙadiriyya suke bi in ban da fadar Kano a wancan lokacin zamanin Sarki Abdullahi Bayero wanda shi mabiyin ɗariƙar Tijjaniyya ne[12]. Ita kuwa jam’iyyar NEPU ta su Malam Aminu Kano mafi yawa na mabiyanta a wancan lokacin ‘yan Tijjaniyya ne. Wannan dalilin ne ya sa ko da aka riƙa samun rikice-rikice tsakanin aƙidun biyu sai aka riƙa danganta shi da siyasa.[13] Dangantakar siyasar da take tsakanin aƙidun biyu ya sanya suka riƙa yi wa juna yarfen siyasa a tsakaninsu.

Idan aka dubi bayanin da yake sama za a fahimci cewa, kasancewar Sarkin Musulmi Baƙadire kuma a wancan lokacin dukkan sarakuna suna goyon bayan jam’iyyar NPC ne, wannan ya sa ya yi wa ‘yan NEPU waɗanda suke ‘yan Tijjaniyya ne galibinsu yarfe da cewa sun ce sallah biyar a wuni haramun ne kamar yadda misalin ya nuna. Duk da cewa a cikin bayaninsa bai fito ƙarara ya ce ‘yan Tijjaniyya ba, amma ya yi amfani da kalmar “Yan Wazifa” wadda kalma ce ta ƙasƙanci da ake faɗa wa ‘yan Tijjaniyya a wajen Lardin Kano.[14] Idan aka duba za a ga cewa wannan yarfe ne na addini domin kuwa ‘yan Tijjaniyya ba su haramta sallah ba, sai dai kawai za a ga hakan a matsayin wanin salo ne na rage wa aƙidar da ma mabiyanta magoya baya waɗanda suka kasance ‘yan NEPU a wancan lokacin domin raunana siyasarta.

Irin wannan ya ci gaba da bayyana a cikin ayyukan rubutaccen Hausa na zube, inda ‘yan siyasa suka riƙa yi wa abokan hamayyarsu yarfe don mabiya su ji cewa jam’iyyar da suke bi ba ta cancanci su bi ta ba. Galibi a siyasa irin waɗannan abubuwa da akan yi yarfe da su ƙaga su ake yi ba tare an ji ko an gani ba, abin nufi babu tabbas a faruwarsu. Alal misali, jamiyyar NPC ta ce jam’iyyar NEPU jam’iyyar kafirai ce, don ɗabi’unsu irin na Kirista ne. Dubi abin da suka ce:

 tsakanin ‘yan NPC da na NEPU waɗanne ne ɗabi’arsu irin ta Kirista ce? Har wasu daga cikinsu sukan ce ba sa bin addinin Musulunci?

(Nadabo, 1960).

Duk da cewa tambaya ce aka yi, amma dai ta sigar yarfe ce aka yi ta domin dai amsar a ƙarshe za ta faɗa kan NEPU ne, domin kuwa ‘yan NPC ne suke tambayar, kuma a jaridar gwamnati wadda ba a sanya bayanan ‘yan hamayya a cikinta, balle kuma abin da ya shafi yarfe. Idan aka duba a cikin wannan misali za a ga cewa an yi wa ‘yan hamayya ne yarfe cewa ɗabi’unsu irin na Kiristoci ne, wanda an san dai cewa kaso mafi tsoka na al’ummar ƙasar Hausa Musulmi ne, kuma addinin Kirista yana takin saƙa ne da na Musulunci. Wannan ya sa ‘yan jam’iyyar NPC suke ganin idan suka jefi NEPU da mummunar kalma irin wannan zai haifar masu da koma-baya. Haka kuma ba wai ɗabi’unsu ne kaɗai irin nan Kirista ba, domin ana iya samun wani Musulmi mai yin wasu ɗabi’u irin na Kirista, sai suka ƙara masu da cewa ai wasu ma daga cikin ‘yan hamayya sukan ce su ba Musulmi ba ne, wato dai sun ma yi ridda, sun bar addinin Musulunci ke nan. Idan aka duba za a ga cewa wannan ba ƙaramar magana ba ce, domin kuwa jifar ‘yan jam’iyya da kafirci ba ƙaramin illata jam’iyyar zai yi ba don al’ummar ƙasar Hausa akasarinta Musulmi ne.

Kasancewar al’ummar Hausawa suna girmama shugabanninsu matuƙa, wannan bai sa sun girmama wani sha’ani na siyasa fiye da addini ba. Tarihi ya nuna cewa abokan hamayyar siyasa, musamman na jam’iyyar hamayya ta NEPU suka riƙa amfani da wannan wajen yi wa magoya bayan NPC yarfe ta hanyar nuna cewa ai sun fi girmama Sardauna da shugabanninsu na siyasa fiye da Ubangiji. Sun nuna cewa yadda suke tsoron Sardauna ba su jin tsoron Allah haka. Dubi dai abin da suka ce a cikin jaridar Daily Comet:

Kai wawa, jahili, daƙiƙi, sususu, bari in gaya maka duk cikin Shari’ar Islama ba inda aka ce a nuna bambanci, ba inda aka ce a bada kuɗi don neman galaba, ba inda aka ce a girmama Sardauna a wulaƙanta gyartai. In kuwa akwai, ka gaya mani ayar da ta ce a yi kukan masallaci na ƙarya don jin daɗin Sardauna da jam’iyyarsa

(Addinin Musulunci a Mazahabar Maliki”, 1960).

Idan aka dubi wannan misalin da yake sama za a fahimci cewa, mayar da martani ne aka yi ga kalaman abokin hamayya. A cikin wannan martanin an yi wa shugabannin jam’iyyar NPC yarfe ta hanyar ƙaga masu wasu batutuwa munana da kuma danganta su da su ba tare da ƙwaƙƙwarar hujja ba. A cikin misalin an nuna cewa ‘yan NPC suna aikata wasu abubuwa na addini ne domin ganin idon Sardauna ko don su faranta masa. Misali, ɗaukaka Sardauna saboda samun duniya da wulaƙanta talaka. Haka kuma an nuna cewa suna yin kuka a masallaci ne ba don tsoron Allah da ya cika zuciyarsu ba, sai don Sardauna da jam’iyyarsa su ji daɗi.

Kamar yadda ‘yan NPC suka riƙa nuna cewa, jam’iyyar NEPU jam’iyya ce ta kafirai maƙiya addini, su ma NEPU sun yi amfani da wannan yarfen ta hanyar nuna cewa shiga jam’iyyar NPC ko AG tamkar shiga kafirci ne, kamar dai yadda wannan misalin ya nuna:

 domin ni har abada ba zani shiga AG ko NPC ko wata jam’iyya ba illa NEPU wadda na dade kuma nake ciki a yanzu. Domin shiga NPC ko AG shiga uku ne, saboda haka Allah ya tsari Musulmi da shiga waɗannan jam’iyyu

(Alasan, 1961).

Wannan misalin ya nuna cewa duk jam’iyyar da ba NEPU ba to shigar ta tamkar shiga uku ne. Idan aka ce mutum ya shiga uku kuwa ana nufin ya shiga masifa da bala’i ke nan. Babu kuwa wata masifar da ta kai kafirci, wannan ya sa a cikin misalin da yake sama aka ƙarasa da addu’ar neman tsarin duk wani Musulmi da shiga Jam’iyyar NPC da AG, wato duk Musulmi bai kamata ya shiga jam’iyyun ba, to wanda ya shiga fa? Ke nan, ba Musulmi ne shi ba.

A siyasance, idan aka lura cewa mutum yana da muhimmanci a cikin tafiyar wata jam’iyya to za a yi duk yadda za a yi domin karkato hankalinsa don ya bi wata jam’iyyar da ba ita ba, kuma kowace jam’iyya za ta so ya kasance a cikinta domin irin amfanin da zai jawo mata. Idan aka bi duk hanyar da za a bi domin raba shi da jam’iyyar da yake ba a yi nasara ba, sai kuma a nemi hanyar da za a ɓata shi don dai a yi irin abin nan da ake cewa a fasa kowa ya rasa, wato a bi shi da yarfe don a karya lagon siyasarsa. Irin wannan ne ya faru da Hassan a cikin littafin Tura Ta Kai Bango, inda abokan hamayya na jam’iyyar hamayya suka yi masa yarfe cewa ya shiga jam’iyyar kafirai. Dubi misalin da yake a ƙasa:

Eh to lafiya, amma ba lau ba. Hassan ne na ga yana neman ya shiga hanya ta Allah wadai, wadda sharrinta ba shi kaɗai zai shafa ba, har da danginsa da mutanen gari. A taƙaice dai yana neman kawo jam’iyyar siyasa ce ta kahurai a nan garin.’

‘Kahurai ɗan nan?’

‘Kahurai Inna! Mu kuma muna ganin yadda mai gidan nan ya nuna masa hanyar makaranta bai kamata ba a ce karatun da ya yi ya zo ya tafi a banza ke nan.

(Katsina, 1983: 43-44)

A wannan misalin idan aka duba za a ga cewa, magoya bayan jam’iyyar Riƙau ne suka tafi suka samu mahaifiyar Hassan suka ce ai jam’iyyar da su Hassan ɗin suke son kawowa garinsu jam’iyya ce ta kafirai, kuma yana neman shiga. Wannan ya sa hankalin mahaifiyarsa ya tashi don ta ji zancen cewa ɗanta zai shiga mummunar hanyar da ba shi kaɗai sharrinta zai shafa ba har da danginsa da sauran mutanen gari. Domin Hassan ɗan gidan malamai ne, kuma ya samu tarbiyya irin ta malanta bai kamata a ji shi ya shiga irin wannan hanya ba. Idan aka duba za a ga cewa yarfe ne aka yi wa Hassan na addini, inda aka danganta jam’iyyarsa da ta kafirai don kawai a ɓata shi a wajen mahaifiyarsa don ta hana shi bin jam’iyyarsa ta Sauyi.

Idan aka dubi waɗannan bayanan da misalan da aka kawo za a fahimci cewa, ‘yan siyasa suna amfani da addini wajen yi wa abokan hamayya yarfe domin nuna wa al’umma cewa ba su cancanci a bi su ba.

4.10.2 Yarfe Na Ƙima/Halaye

Ƙima yana nufin hali na ban girma (CNHN, 2006:244). A siyasa ana la’akari da halaye da ɗabi’un ‘yan siyasa wanda dole ne a zahiri su kasance na ƙwarai domin magoya bayansu samu dalili da ƙwarin guiwar goya masu baya da kuma tallata su domin zaɓensu. Samun ‘yan siyasa da wasu munanan ɗabi’u ko wasu miyagun halaye ko tarihin wani abin kunya yakan sa a yi wa jam’iyyarsu suka da mummunar shaida ta hanyar danganta su da wannan halin wanda zai iya raunana farin jinin jam’iyyar ga magoya bayanta.

A cikin tarihin siyasar Jam’iyyu an sha zargin ‘yan NEPU da tsaurin ido ga mahukunta, kasancewar sun yi imani cewa mahukunta suna danne masu haƙƙoƙinsu. Wannan ya sa duk yadda suka juya ko suka furta wani abu ‘yan NPC sukan ɗauke shi a matsayin tsageranci ne maimakon neman haƙƙi. A wata wasiƙa da aka samu a jaridar Sodangi an nuna yadda ‘yan jam’iyyar NPC suke jingina wa ‘yan NEPU rashin tarbiyya, inda har a cikin wasiƙar ya kira ‘yan NEPU da cewa sun raina iyayensu. Dubi wannan misalin:

Ina so Edita ka ban ɗan fili don in bayyana rashin tarbiyyar NEPU. Abin mamaki, don wanda ya ce mahaifinsa ma ba kowa ba ne, ina ga wani? Kwanan baya ne can, ranar da suka yi lacca a Tudun Wada, sun taso suna komowa gida suna ta ƙetare babban titi babu tunanin komai, sai ga wata mota ta ɓillo daga Airport. A nan suka dinga yi wa mai motar tsawa tun yana nesa, wai ya tsaya sai Firimiya ya wuce wato Malam Aminu Kano bayan wucewar wannan direba sai wasu jakan ‘yan NEPU suka bi shi da zagi. Wannan kuwa rashin tarbiyya a fili ke nan.

(Lallai Babu Tarbiyya”, 1957).

A cikin wannan misalin, an nuna yarfe ne inda aka bayyana cewa ‘yan NEPU ba su da tarbiyya. An sani cewa tarbiyya muhimmin abu ne a rayuwar Hausawa, kuma duk wanda ya rasa ta ana yi masa masa kallon mutumin banza maras ƙima da daraja a idon mutane. Haka kuma duk wanda ya rasa tarbiyya ana kallon sa a matsayin wanda ba ya ganin mutuncin kowa. Wannan ya sa a cikin misalin bayan marasa tarbiyya da aka kira su, sai kuma aka ce sun raina iyayensu, in kuwa hakan ta kasance to ke nan babu wani mai sauran mutunci a idonsu. Da wannan ‘yan NPC suka riƙa nuna wa al’umma cewa magoya bayan NEPU tsageru ne marasa kunya da mutunci, don haka kada a bi su ko kuma a goya masu baya.

Da aka ci gaba da tafiya lamarin yarfe ma ya ci gaba, domin a wuraren shekarar 1959 an samu wani bayani da ya nuna ‘yan siyasa sun ci gaba da yi wa abokan hamayyarsu yarfe, don nuna cewa ba su da halin kirki, ko kuma ba za a samu wani abin kirki da al’umma za ta amfana ba in aka zaɓe su. Alal misali, a cikin jaridar Sodangi an ga inda aka yi wa jam’iyyar NEPU yarfe da cewa cuta take yaɗa wa magoya bayanta kamar haka:

 amma NEPU ta zama tunku da ƙararrawa mai jawowa dangi cuta koyaushe, ita ko kujera ɗaya ba za ta samu ba, sai ta koma Kudu wajen Enugu ko ta lasa a can.

(A.G. Na Maganin Mutuwa a Arewa, 1959).

A nan ɗaya daga cikin magoya bayan NPC ne yake nuna cewa Jam’iyyar NEPU babu alheri tattare da ita, inda ya kwatanta jam’iyya da wani dabba mai suna tunku, wanda ya ce ba ya kawo wa ‘yan’uwansa alheri, kullum sai sharri. Don haka magoya bayan jam’iyyar ba za su samu wani alfanu daga gare ta ba sai dai cutuwa da za su yi. Ya nuna cewa ba za ta samu ko kujera ɗaya ba a Arewa idan aka yi zaɓe, sai dai ta koma Kudu ko za ta samu a can. Idan aka dubi yadda ya nuna cewa Jam’iyyar NEPU tana yaɗa wa ‘ya’yanta cuta za a fahimci cewa lallai yarfe ne ya yi wa jam’iyyar ta hanyar amfani da wani hali mummuna na yaɗa cuta, don dusashe haskenta ga mogoya bayanta. Duk da cewa babu wanda aka ji cewa jam’iyyar ta sa masa wata cuta ko kuma ta jawo masa wani sharri, illa dai ya ƙaga zancen ne don ya sanya wa jama’a shakku a kanta.

Yana daga cikin yarfen da aka samu a cikin tarihi tun a jamhuriya ta farko, jingina wa mutum wani mummunan aiki wanda bai aikata ba, ko kuma ya aikata sai a yi ƙoƙarin danganta mummunar aikinsa ga wasu don a nuna cewa duk haka suke ko kuma halinsu guda. Wannan ya yi daidai da wani misali da aka samu a cikin jaridar Sodangi wanda aka yanke wa wani ɓarawon agwagi shekara ɗaya a gidan yari. Dubi misalin:

Mai shari’a ya sami Gambo da laifin satar agwagi bayan an tambaye shi (Gambo) ya tabbatarwa da shari’a sai mai shari’a ya yanke masa hukunci da shekara ɗaya. Har wa yau dai ashe a jikin rigar mutumin nan a gaba da baya duk tauraro ne a jikinta To wannan abin kunya ko lallai ya kai a ce da mai shari’a an ji kunya ko ba ita a ce dai mai riga da tauraro ya sato agwagi

(Mohamed, 1960).

An tuhumi wani mai suna Gambo da satar agwagi, kuma an same shi da laifi. A matsayinsa na wanda aka samu da laifin sata, sai kawai aka yanke masa hukunci daidai da laifin da ya aikata. Bayan haka sai aka lura cewa, a jikin rigar ɓarawon akwai hoton tauraro wanda yake alama ce ta jam’iyyar NEPU, sai aka nuna cewa ai ɓarawon nan ɗan NEPU ne, don haka sai ‘yan NPC suka ce ‘yan NEPU su faɗa wa mai shari’a sun ji kunya. In kuwa ba su da kunya to su faɗi cewa an kama mai riga da alamar tauraro ya saci agwagi. Wannan shi ma zai iya kasancewa yarfe ne kawai irin na siyasa, domin kuwa da ganin tauraro a jikin rigar ɓarawo ba zai tabbatar cewa shi ɗan NEPU ne ba, don yana iya kasancewa ma rigar sato ta ya yi a wani wuri ya sanya ta ba tare da la’akari da alamar da take jikinta ko na wace jam’iyya ce ba. Don an kama wani ɗan jam’iyya da laifi ba shi yake nuna cewa duk ‘yan jam’iyyar ne suka yi laifin ba, hasali ma su laifin bai shafe su ba.

Wani misalin yarfe na halaye shi ne, yadda za ka ga wata jam’iyya tana faɗin miyagun maganganu a kan wata, inda za ta riƙa danganta ta da munanan halaye kamar su hassada da ƙarya da cin amana da dai sauransu. A wannan misalin da yake ƙasa an samu irin wannan:

 Ofishin ba da labarai na jam’iyyar NEPU ya Zargi Jam’iyyar NPC a kan sunan nan da ta yi na irin halin nan nata na hassada a kan maganar da awolowo ya yi cewa babu irin mulkin da ya fi dacewa da Nigeria illa na jamhuriya.

(Bai Kyautu NPC Ta Soki Maganar Da Awolowo Yayi Ba, 1961).

A cikin wannan Misalin NEPU ta siffanta jam’iyyar NPC da ɗabi’ar hassada, inda ta nuna cewa da ma halin jam’iyyar ne, domin a ganin NEPU shawarar da Awolowo ya bayar kan tsarin mulkin da ya kamata a bi shi ne daidai, kawai dai hassada ce ta sanya NPC sukar wannan batu. Idan aka duba za a ga cewa, hassada mummunan abu ne, kuma babu wanda zai so a danganta shi da shi, su kuwa a wurin ‘yan siyasa abu ne da suke amfani da shi don hana abokin hamayya motsi. Ya zama wani hali na ‘yan siyasa wanda da zarar an ga kuskuren ɗan siyasa aka nemi yi masa gyara sai a ce hassada ake yi masa. Wannan ya sa abokan hamayya da zarar sun yi magana sai a ce hassada ce suke yi wa jam’iyya ko ɗan siyasa ba da zuciya ɗaya suke yi ba.

Jam’iyyar NEPU ta kamanta jamiyyar NPC da jam’iyyar gumaka, inda ta yi kira da kada a zaɓe ta. Kalmar gunki dai an san wani abu ne da aka sassaƙa ko a ƙera ko a gina wanda yake da sifar mutum ko wani abu mai rai, wanda ba ya iya amfanar da kansa komai, kuma ba ya iya kare kansa daga cutarwa ko ya kare wani. Gunki ba ya magana ba ya motsi balle ya iya aiwatar da wani abu. Ga misalin kamar haka:

 ina jan hankalin mutane masu zaben NPC da su manta da ita domin jam’iyyar gumaka ce

(Gasakas,1961).

  A nan ‘yan jam’iyyar hamayya ne suke yi wa masu mulki yarfe da cewa jam’iyyarsu ta gumaka ce. A nan ɗayan uku ne, ko dai jam’iyyar ba ta iya tsinana wa al’umma komai kamar yadda gunki ba ya iya amfanar kansa balle waninsa, ko kuma manyan jam’iyyar NPC ne aka danganta su da gumaka domin ana yi masu biyayya tamkar yadda ake bauta wa gumaka, ko kuma su ‘yan jam’iyyar baki ɗaya daga shugabannin har mabiyan bautar gunki suke yi ba Allah suke bauta wa ba. Tun daga taken wasiƙar da jaridar ta buga za a fahimci cewa, mai wasiƙar yana nufin duk wanda ya bi jam’iyyar NPC ya ɓata kamar dai yadda mai bautar gumaka yake ɓatacce kamar yadda Musulunci ya nuna.

Daga cikin yarfe na ƙima wani lokaci akan danganta shi da wani makusancin ɗan jam’iyya, wanda ake ganin zai iya shafar su har ya yi tasiri a cikin siyasarsu. Alal misali, wani ɗan siyasa wanda yake tsohon shugaban ƙaramar hukuma ne, a lokacin da yake neman kujerar ƙaramar hukuma an yi masa yarfe da cewa mahifinsa ɓarawon keke ne lokacin yana matashi, don haka ba za a zaɓi wanda yake da gadon sata ba, bayan kuwa hakan bai taɓa faruwa ba.[15] Irin wannan yarfen ya yi kama da wanda aka nuna a cikin littafin Tura Ta kai Bango kamar haka:

Ni ai da ma na san wannan yaron bai gaji arziƙi ba. Ubansa fa Na-Torami har ya mutu itace yake sarowa yana sayarwa. Kwana bakwai ma kafin ya mutu, sai da na sa shi ya kawo min kai uku har gida Wani ya ce, Yo shi kansa Garban fa? Ubansa ba mahauci ba ne, karen lahira?

(Katsina, 1983: 21-22)

A cikin wannan misalin ana an yi wa ‘yan jam’iyyar Sauyi ne yarfe cewa talakawa ne ‘ya’yan matsiyata ba su da komai, duk da cewa suna da jama’a kuma sun zamar wa jam’iyyar Riƙau ƙadangaren bakin tulu. An nuna cewa ai Hassan mahaifinsa sana’ar saro itace yake zuwa ya yi, ya zo gari ya sayar. Shi kuwa Garba an ce wai mahaifinsa mahauci ne karen lahira. Irin waɗannan abubuwan akan samu duk yarfe ne don jama’a su ɗauka cewa ai ba wata ƙima suke da ita a cikin al’umma ba. Bayan kuwa babu ruwan shugabancin siyasa da arziƙinsu matuƙar dai sun cancanta, amma sai a yi amfani da ƙimarsu a yi masu yarfe da shi.

A wasu lokuta akan nemi abin da za a shafa wa ɗan siyasa domin ya zubar masa da mutunci a idon a jama’a, inda za ka ji an zargi wani ɗan takara da yi wa wata cikin shege, ko wani makamanci haka, a yaɗa don a sanya masa baƙin jini a cikin al’umma. A tarihin siyasar jam’iyyu an samu irin wannan yarfen wanda jaridar Gaskiya Ta fi Kwabo ta ruwaito, inda aka yi wa mataimakin shugaban ƙasa a jamhuriya ta biyu yarfe da cewa, ya yi lalata da wata mata har ta samu juna biyu. Ga misalin:

Wata mujallar kasar nan mai suna The Week ta taɓa buga wani labari, inda ta nuna cewa, wata matar aure ta shaida wa kotu cewa Alex Ekwueme ne ya yi mata ciki har Allah ya sa ta sami ƙaruwa Amma shi Ekwueme ya ce abin da Adeline ta fada karya ne kuma bata suna ne.

(“Ekwueme zai ba mu kunya”, 1999).

Alex Ekwueme shi ne mataimakin shugaban ƙasa a jamhuriya ta biya, kuma shi ne aka yi wa wannan yarfen a lokacin ana shirye-shiryen sake zaɓen su a karo na biyu a shekarar 1983. Wata matar aure ce mai suna Adeline ta yi iƙirarin cewa shi ne ya yi mata cikin shege har ta haifi ‘ya’ya biyu, inda shi kuma ya ƙaryata. Ya nuna cewa abin da ta faɗa ba shi da tushe, hasali ma yarfe ne kawai aka masa domin a ɓata masa suna.

Samun tababa a cikin nasabar mutum babban abu ne da kan sa mutum ya rasa ƙimarsa a idon mutane, wannan ya sa ‘yan siyasa kan riƙa yin yarfe a duk lokacin da aka samu wata ƙofa wadda ta ba su damar hakan. A baya an yi ta yaɗa maganganu na yarfe da suke nuna cewa wani mataimakin shugaban ƙasar Nijeriya tsintacce ko kuma ba a san iyayensa ba. ‘Yan hamayya sun yi ta amfani da wannan domin dasusashe haskensa. Irin wannan ya fito a ciki littafin Kowa Ya Bi inda aka nuna cewa gwamnan jihar bai san iyayensa ba. Ga misalin:

 to amma yadda za ku san batun ƙaryar shekarun da takardun da ma uwa uba rashin tabbacin iyayen gwamna don kowa ya san a gidan marayu ya girma. Sannan har yanzu gwamna ya kasa fitowa ƙarara ya ƙaryata zarge-zargen a idanun duniya. Sai kame-kame yake yi idan an tambaye shi. An ma taɓa tambayar mai ba shi shawara a kan batun shari’a sai ya ce wai a je gidan marayu za a ga tarihinsa a rubuce. To ya ‘yan’uwa mu da Allah (SWT) ya ba mu wannan babban gari mai tarihi ga manyan bayin Allah da waliyyai wai mun ba wa jikan Musailamatul-Kazzabi yana mulkarmu ku san ba zai yiwu ba.

(Gwammaja, 2007: 30)

Kamar yadda aka riƙa yada cewa wancan mataimakin shugaban ƙasar ba shi da iyaye, haka wannan misalin ya nuna cewa gwamnan bai san iyayen sa ba a gidan marayu ya tashi, kuma ‘yan hamayya ne suka sanya shi gaba suna yi masa yarfe da wannan. Ba sabon abu ba ne a siyasar Nijeriya a zargi mutum da rashin takardun karatu, wanda a lokuta mafi yawa akan samu yarfe ne kawai domin idan aka bincika akan tarar sun yi har ma da shaida. Akan yi wa mutum yarfe da cewa ba shi da iyaye ne don a rage ƙimarsa a idon duniya musamman idan an rasa da me za a ɓata sunansa da shi.

Irin wannan ya sake bayyana a cikin littafin Dambarwar Siyasa, inda aka so yarfa wa Farfesa don a ɓata masa suna da cewa ya yi wa wata yarinya fyaɗe kamar haka:

Ganin cewa haƙarsu ba ta cim ma ruwa ba sai suka ƙudurci ko ta wane fanni sai sun dakushe farin jinin Farfesa tare da zubar masa da mutunci a idon jama’a. Ranar wata Lahadi tarkonsu ya kama kurciya, domin a ranar ne suka samu nasarar shigar da wata yarinya ‘ya shekara goma sha biyu cikin gidan gonar Farfesan, a daidai lokacin da ya je duba wani aiki da aka gudanar. Bayan ‘yan iskan sun yi mata rubdugun fyaɗe, sai suka lallaɓa suka sulale ba tare da wani ya gan su ba, tare da yada ta a bakin hanyar shiga da fita ta gidan gonar. Tun daga nesa Farfesan ya hango ta a yashe, cikin hanzari ya yunƙura da niyyar kai mata agaji, tabbacin da ya samu tana da sauran numfashi a jikinta ya sa ya yunƙura tare da cicciɓar ta da niyyar sa ta a mota ya kai ta asibiti, a daidai wannan lokacin ‘yan sanda suna zuwa. Abin ka da ture, take suka zargi Farfesa da aikata wannan aika-aika.

(Aminiya-Trust, 2020: 41).

A cikin wannan misalin za a fahimci cewa yarfe ne aka shirya wa Farfesa a matsayinsa na mutum mai gaskiya da riƙon amana da kuma mutunci a cikin al’umma wanda gaskiya da mutunci suka sanya jama’a suke ƙaunarsa, kuma suka tsayar da shi takarar gwamna a wata jam’iyya, inda ‘yan hamayya suka lashi takobin ko ta halin ƙaƙa sai sun tabbatar bai kai labari ba. Bayan tsallake dukkan makirce-makircen da aka riƙa ƙulla masa ne aka yi tunanin a shirya masa yarfen da zai taɓa mutuncinsa ya sa al’umma su dawo daga rakiyarsa. Idan aka duba za a ga cewa, fyaɗe mummunan abu ne a cikin al’umma, wannan ya sa aka danganta ɗan takarar da shi ta hanyar jefar da yarinyar a bakin gidan gonarsa, kuma aka jira sai da ya zo inda take aka ce ana zargin shi ya yi mata.

Yarfen siyasa ya ci gaba da bayyana a cikin tahin siyasar jam’iyyu, domin bayan faɗuwar jam’iyyar PDP a babban zaɓen ƙasa a shekarar 2015, shugaba Muhammadu Buhari ne ya zama shugaban ƙasar Nijeriya a jam’iyyar APC. Bayan rantsar da shi ya yi fama da rashin lafiya, inda ya tafi jinya ƙasar Birtaniya. Bayan dawowarsa don ci gaba da gudanar da harkar mulki, sai aka yi ta raɗe-raɗin cewa ai ainihin Buhari ya mutu, an sauya shi ne da wani mai kama da shi mai suna Jibril daga Sudan. Wannan zance ya yi tashe a cikin al’umma kasancewar tun da ya dawo sai karsashinsa ya sauya ya ragu tamkar ba Buharin da aka zaɓa ba. Wannan ya sa wasu al’ummomi daga wasu ɓangarorin ƙasar suka riƙa kiransa da Jibril na Sudan. Shugaba Buharin ya nuna cewa shi ne da kansa ba a sauya shi da na bogi ba. Dubi wannan misalin:

A jiya Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa shi ba na bogi ba ne, ya bayyana hakan ne a ganawar da ya yi da al’ummar Najeriya mazauna kasar Poland a birnin Krakow a ziyarar da ya kai kasar domin halartar taron sauyin yanayi na Majalisar dinkin duniya. A yayin ganawar, wani dan Najeriya ne ya yi masa tambaya a kan cewa shin da gaske ne cewa shi ne Buhari da aka sani ko kuma wani ne ke kwaikwayon sa da ake kira Jibril daga Sudan. Shugaban ya yi Allah wadai masu yada wannan jita-jitar tare da cewa, ba su san ya kamata ba

(Adamu, 2018).

Shugaba Buhari ya fito ne ya tabbatar wa duniya cewa yarfen da ake yi masa cewa shi ba na bogi ne ba, shi ne dai gangariyarsa, ba wani ne yake kwaikwayonsa ba, kuma ya nuna rashin jin daɗinsa da wannan labarin da ake ta yaɗawa. Irin wannan yarfe ne na ƙima domin ana nuna cewa ba shi da nagarta kamar yadda aka san shi a farko kama mulkinsa a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasa.

A jamhuriya ta huɗu an samu wata hanya ta yarfe wadda za a samu wani ɗan bangar siyasa a biya shi, sai a kitsa masa abin da ake so ya fito ya faɗa a wata kafar watsa labarai, kuma in ma wani abu ya biyo baya iyayen gidansa na siyasa su ne za su tsaya masa don fitar da shi. Irin waɗannan mutane da akan ɗauka haya a siyasance ana kiran su da ‘sojojin baka’. Aikin irin waɗannan sojojin bakan shi ne su fito su ƙalubalanci ‘yan hamayya ta hanyar yarfe ko kuma su kare iyayen gidansu ta hanyar yi wa abokan hamayya yarfe. Irin wannan misalin na sojan baka ya bayyana a cikin littafin Da Bazarku inda aka bai wa wani sojan baka mai suna Auwalu wasu bayanai na yarfe a rubuce wanda aka yi wa Farfesa Auta. Ga misalin:

Wai yaro ƙarami kamar Auwalu wanda mahaifinsa ma almajirinka ne wai shi ne yau zai shiga gidan rediyo yana faɗar wai Farfesa ma da ake kiranka na je-ka-na-yi-ka ne… kuma wai kai ɗin nan Bafillatani ne, don haka idan aka yi kyakkyawan bincike wai kai ba ma mutumin ƙasar nan ba ne Farfesa Auta ya yi murmushi ya ce, na saurari duk abin da yaron nan ya faɗa, amma kai da ji ka san rubuta masa aka yi ya haddace domin haka ka rabu da su ko ba-daɗe ko ba-jima gaskiya dai ɗaya ce tal kuma siyasa ba da gaba muke yin ta ba.

(Surajo, 2006: 95).

A cikin misalin an nuna cewa Auwalu ya shiga gidan rediyo ya yi wa Farfesa Auta yarfe ta hanyar taɓa ƙimarsa da cewa wai shi ɗin Farfesan bogi ne, kuma wai in ma aka tsananta bincike a tarar cewa shi ba ɗan ƙasa ba ne don kawai shi Bafulatani ne. Don a nuna cewa sojan baka ne shi ɗaukar hayansa aka yi, sai Farfesa Auta ya ce, ai ko da jin yadda yake magana za a fahimci duk bayanan da yake faɗa rubuta masa aka yi ya haddace su, kuma in aka yi haƙuri gaskiya za ta bayyana.

Idan aka dubi dukkan bayanan da aka kawo a wannan ɓangaren za a fahimci cewa, wani nau’in yarfe ne da ake amfani da ƙima ko halaye wajen yin sa. Akan yi amfani da irin wannan yarfen ne don taɓa ƙimar wani ɗan siyasa ko jam’iyyarsa ko kuma nuna wani mummunan hali tare da danganta shi da shi.

4.10.3 Yarfe Na Tafiyar Da Shugabanci

Tafiyar da shugabanci wani nauyi ne na al’umma wanda akan ɗora wa shugabanni domin gudanar da al’amuran al’umma yadda ya dace bisa tsarin doka. Tsarin shugabanci na siyasa ya tanadi wasu tsare-tsare na dokoki waɗanda ake amfani da su wajen warwarewa da kuma daidaita abubuwan da suka shafi gudanar da al’amuran jama’a, ba tare da sanya son zuciya ko kuma bai wa wani ɓangare fifiko a kan wani ba. Bin ire-iren waɗannan dokoki sau da ƙafa galibi shi ne yake haifar da daidaito da adalci da kuma zaman lafiya. Sau da dama duk wanda ya bijirewa irin wannan tsarin doka akan kalle shi a matsayin mara gaskiya.

Duk da cewa bin waɗannan dokokin tsarin mulki shi ne daidai kuma abin da ya dace, amma wasu kan yi amfani da wannan don ganin wallen masu so su ɗabbaƙa su, har ma a wasu lokuta a zarge su da rashin yin abin da ya dace tun da ba su bar kowa ya yi yadda ya ga dama ba. A cikin siyasa akan yi wa ɗan siyasar da ya nuna cewa in ya hau mulki zai riƙe gaskiya da adalci ba tare da nuna sani ko sabo ba yarfe da cewa zai wulaƙanta manya ko zai ci mutuncin wasu. Alal misali, a lokacin da tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari yake gudanar da yaƙin neman zaɓe ya yi ta bayyana cewa zai hana cin hanci da rashawa da almundahana da dukiyar ƙasa, kuma duk wanda ya saci dukiyar ƙasa za a ƙwato, sai aka riƙa yi masa yarfe cewa yana da niyyar cin mutuncin manya ne. Wannan ya sa abokan hamayya suka dage don ganin bai kai labari ba. Irin wannan misali ne na yarfe na tafiyar da shugabanci, domin ana nuna cewa ga hanyar da zai bi ne wajen tafiyar da jama’a idan ya samu ya ɗare karagar mulki. Irin wannan misalin ya bayyana a cikin littafin Da Bazarku. Ga misalin:

 a cikin wannan jaridar tabbas na karanta wata hira da aka yi da Farfesa Auta a kan gyaran kundin tsarin mulkin ƙasar nan …Ya dai so ya yi taɓargaza ne, tun da cewa ya yi shi fa har yanzu bai iya faiyace takamaiman aikin da sarakuna suke yi ma talakawansu. Saboda haka wai shi yana ganin ya kamata a faiyace wannan lamari a cikin sabon kundin da ake shirin tsarawa Lauya ya ce, ‘to a nemo mana ita daga nan zuwa jibi ko gata, mu kuwa za mu yi farfaganda mu birkita abin da ya faɗa a ciki, shafa masa kashin kaji a idanun talakawa da sarakuna. Kai kuwa tauraruwarka ta haskaka hasken da ba wanda ya isa ya dusashe ta.

(Surajo, 2006: 50-51).

A cikin wannan misalin an nuna yadda ɗan takarar shugabancin ƙasa Farfesa Auta ya yi hira da ‘yan jarida ne kan batun yi wa kundin tsarin mulki gyaran fuska, inda ya nuna cewa ya kamata a fayyace aikin sarakuna a cikin kundin tsarin mulki. Wannan ya sa aka shirya nemo jaridar a birkita zancen a shigar da abin da za a yi masa yarfe da shi don a shafa masa kashin kaji. Idan aka duba wannan yarfe ne na tafiyar da shugabanci, domin ya nuna idan ya samu dama zai yi gyara ga kundin tsarin mulki ta hanyar bayyana irin aikin da ya kamata sarakuna su riƙa yi wa talakawa, amma sai aka nuna za a shafa masa kashin kaji da wannan don al’umma su dawo daga rakiyarsa, kuma tauraron abokin takararsa ya haskaka.

A jamhuriya ta huɗu zamanin mulkin Muhammadu Buhari an yi amfani da wani nau’in yarfe da ya dusashe hasken ‘yan siyasa da dama. A lokacin mulkin na Buhari musamman daga 2015 zuwa 2019, an ɗauka cewa duk wanda ba ya tare da shi to kamar mutum ne da bai yi imani ba, domin ana ganin kauce wa tsarin tafiyar Buhariyya kamar kafirci ne a siyasance. Wannan yana daga cikin dalilan da suka sanya da yawan ‘yan siyasa suka bi ɗariƙar Buhariyya ba don suna so ba, sai don su tsira da imaninsu a siyasance a fuskar mabiyansu. In ba haka ba za a bi su da yarfe cewa suna hamayya da Buhari ko tafarkinsa. Dubi wani misali mai kama da wannan a ƙasa:

Saboda mutane sun dauki Shugaba Muhammadu Buhari tamkar mahadi da saba masa tamkar saba wa Allah ne, sai wasu ’yan siyasa suke amfani da wannan dama wajen bata abokan siyasarsu don su lalata su. Duk wanda yake son lalata maka siyasa sai ya ce kana fada da Buhari.

(Mustapha, 2015).

Akwai waɗanda aka gurgunta tafiyar siyasarsu sanadin yarfen da aka yi masu da cewa suna faɗa da Buhari, domin a lokacin mutane suna yi wa Shugaba Buharin kallon wani waliyyi a siyasance wanda saɓa masa tamkar saɓa wa Allah ne, shi ya sa idan ana so a ɓata siyasar wani sai a yi masa yarfe da cewa yana yi wa Buhari zagon ƙasa ko yana faɗa da shi. Irin wannan ya karya alkadarin ‘yan siyasa da dama a zamaninsa.

Wani lokaci idan ana so a yi wa ɗan siyasa yarfe sai a yi masa riga-malam-masallaci ta hanyar aikata wani abu don nuna cewa shi ya kasa, ko kuma a yi kira gare shi ko jam’iyyarsa kan aikata wani abin da ya dace ba don ana son a aikata ɗin ba, sai don al’umma su yarda cewa jam’iyyar hamayya ba ta kan tsarin da ya dace ko ba ta bin doka da oda. Alal misali, jaridar Leadership Hausa ta buga wani labari wanda ta ce jam’iyyar hamayya ta PDP ta yi kira ga gwamnan jihar Kebbi da ya miƙa ragamar mulki a hannun mataimakinsa bayan bayyana cewa gwamnan yana shirin tafiya aikin Hajji. Ga misalin:

Mataimakin gwamnan jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Tafida, ya nesanta kansa da sanarwar da jam’iyyar hamayya ta PDP ta fitar na neman a miƙa ragamar mulkin jihar biyo bayan gwamnan jihar na shirin tafiya aikin Hajji 2024.

Tun da farko dai jam’iyyar PDP ce ta fitar da sanarwa a ranar Laraba 5 ga watan Yuni a Birnin Kebbi inda ta buƙaci Gwamnan Jihar da ya miƙa ragamar mulki ga mataimakinsa tun da yana shirin tafiya Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin bana.

(Birnin-Kebbi, 2023).

Idan aka duba za a ga cewa a doka idan gwamna zai yi tafiya irin wannan zai bar ragamar tafiyar da al’umma a hannun mataimakinsa ne, amma sai aka jiyo jam’iyyar hamayya tana yin kira ga gwamnan jihar da ya yi hakan. Wannan idan aka kula za a ga cewa yarfe ne na tafiyar da shugabanci, domin yana nuna cewa kamar gwamnan ba ya bin tsarin doka na tafiyar da mulkin jihar ne, kuma wannan zai iya yin tasiri ga al’umma wajen ganin wallen gwamnan. Hakan ne ya sa mataimakin gwamnan jihar ya fito ya mayar masu da martani cewa, ko da yaushe gwamnan jihar yana miƙa mulki ga mataimakin nasa ko da tafiyar yini ɗaya ya yi na barin ya jihar. Dubi abin da ya ce:

A cewar Sanata Umar, “Mun yi mamakin da’awar da ƴan hamayya ke yi na cewa a miƙa min ragamar mulki, domin ko da rana ɗaya Gwamna Nasir bai taɓa hanani yin aiki ba.

(Birnin-Kebbi, 2023).

Idan aka duba za a fahimci cewa wannan yarfe ne aka yi wa jam’iyya mai mulki ta hanyar nuna cewa ba su iya tafiyar da shugabanci ba, ko kuma ba su bin doka a tsarin shugabancinsu.

Idan aka dubi waɗannan bayanai da suka shafi yarfen siyasa, za a fahimci inda aka fito a tarihin ginuwar siyasar jam’iyyu a ƙasar Hausa, wanda wannan shi ne ya share hanya zuwa sauran jamhuriyoyin da aka samu bayan ta farko. Irin waɗannan sun ci gaba da faruwa a cikin siyasar ƙasar Hausa, kuma an ci gaba da amfani da su a matsayin hanyoyin samun magoya baya da kore wa abokan hamayyar siyasa mabiya.

4.11 Naɗewa

A wannan babi an kawo bayanai kan abin ya shafi ginuwar siyasar jam’iyyu tun daga samuwar ta, da kuma irin yadda jam’iyyun suka riƙa gwagwarmaya don neman mabiya ta kowane hali. Tun da farko an kawo ma’anar siyasa da nau’o’inta, sannan an kawo ma’anar adabin siyasa da kuma bayani kan wasu dalilan da ake ganin sun taimaka wajen haifar da ƙamfar ayyukan adabin siyasa. Daga nan kuma sai aka ci gaba da nazarin ginuwar siyasar ƙasar Hausa, inda kawo bayanai kan yadda aƙidu suka taka rawa wajen ginuwar siyasa a ƙasar Hausa, inda aka nuna irin gudummawar da ɗariƙun Tijjaniyya da Ƙadiriyya suka bayar wajen ci gaban siyasa da kuma ƙoƙarin neman mabiya. A cikin wannan babin an kawo yadda ‘yan siyasa suka riƙa amfani da matsayi da dangantakarsu da manyan Shehunnan ɗariƙu da sauran aƙidu da kuma manyan ‘yan siyasa wajen samun karɓuwa a siyasance. Daga nan kuma an dubi matsayin mata a siyasar ƙasar Hausa da irin gwagwarmayar da aka yi wajen ba su ‘yancin neman ilimi da shiga siyasa a dama da su. A ƙarshe, babin ya dubi yadda ‘yan hamayya suka riƙa shan matsi daga masu mulki da irin kai-ruwa-ranar da aka riƙa yi tsakaninsu, wanda ya haifar da siyasar yarfe a tarihin ginuwar siyasar ƙasar Hausa.



[1] Dubi https://www.inecnigeria.org/wp-content//uploads/2019/02/ANNEURE-1.pdf

[2] Dubi https://govote.ng/political-parties/

[3] Waɗannan wasannin duk ba a wallafa su ba kamar yadda Umar, A. U. (2022: 78-79) ya bayyana.

[4] Tattaunawa da Dr.Kabir Sufi Sa’id, masanin harkokin siyasa kuma mai sharhi a kan al’amuran yau da kullum, sannan Malami a kwalejin CAS da ke Kano, ranar 27 ga watan Janairu, 2024 da misalin ƙarfe 5:20 na yamma, ta wayar tarho.

[5] Hira da Farfesa Atiku Ahmad Dunfawa a ofishinsa da ke sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato. Ranar 15/7/24 da misalin ƙarfe 2:15.

[6] Dubi lamba ta 4

A duba Paden, J. (1973) Religion and Political Culture in Kano. Shafi na 69 da shafi na 182.

[7] Dubi Paden (1973) Religion and Politcal Culture in Kano, shafi na 312.

[8] Dubi Alƙasum Abba (2000) The Politics of Principles in Nigeria: The Example of NEPU. Shafi na 73.

[9] Hira da Dr. Isah Abdullahi Muhammad malami a sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato. Ranar 15/7/2024 a ofishinsa.

[10] Hira da Dr. Rabiu Bashir, ɗan siyasa kuma malami a ofishinsa da ke sashen Koyar da Harsunan Nijejiya  da Kimiyyar Harshe, jami’ar Jihar Kaduna, ranar 16 ga watan Mayu, 2024.

[11] Dubi lamba ta 10.

[12] Dubi lamba ta 5

[13] Dubi Paden, J. (1973:122) Religion And Political Culture in Kano.

Dubi Scott, P. H. G. (1952:2) A survey of Islam in Northern Nigeria.

[14] Dubi lamba ta 8

[15] Hira da Uwargidan Alhaji Ibrahim Lazuru, tsohon shugaban ƙaramar hukumar Lere, jihar Kaduna a gidansa da ke Sabon Kawo Kaduna. Ranar 22 ga Maris, 2021.

Post a Comment

0 Comments