Yusuf, J. (2025). Tarihin Ganuwar Wasu Al'amuran Siyasar Jam'iyyu a Cikin Rubutun Zuben Hausa Daga 1950-2023 (Ph.D. Thesis) Department of Nigerian Languages, Usmanu Danfodiyo, Sokoto.
TARIHIN GINUWAR WASU AL’AMURAN SIYASAR
JAM’IYYU A CIKIN RUBUTUN ZUBEN HAUSA DAGA 1950-2023
Na
Jibril Yusuf
Email: yusuf.jibril@kasu.edu.ng
Phone: +2347030399995
*** ***
Na sadaukar da wannan aiki ga mahaifana Malam Yusuf
Nadabo Musa da Marigayiya Malama Bilkisu Adamu. Allah ya ji ƙanta, ya yafe mata kuraranta, ya sa Aljanna
Firdausi ta zama makoma a gare su da mu baki ɗaya, amin.
GODIYA
Dukkan yabo da godiya, sun tabbata ga Allah Maɗaukakin
Sarki, Mahaliccin kowa da komai, mai yawan kyauta da baiwa, mai bai wa kowa komai,
ba shi buƙatar komai a wurin kowa, kowa ne yake da buƙatar komai a wurinsa, wanda
ya raya mu, ya nufe mu da kawowa wannan lokaci. Tsira da aminci su ƙara tabbata
ga fiyayyen halitta, farin jakada, cikamakin Annabawa, shugabanmu, Annabi Muhammadu
(S.A.W) da iyalan gidansa da sahabbansa. Ina ƙara godiya ga Allah (S.W.T) da ya
ba ni ikon kammala wannan aiki cikin nasara.
Ina miƙa godiya ta musamman ga jagororin wannan aiki,
Farfesa Umar Aliyu Bunza, wanda ya jagoranci duba wannan aikin bincike da Farfesa
Abdulbasir Ahmad Atuwo, mai duba aikin na biyu da kuma Farfesa Abubakar Abdullahi
na Sashen Kimiyyar Siyasa na Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato, mai duba aiki na
uku, waɗanda suka sadaukar da lokacinsu wajen dubawa, da daidaita aikin bisa turbar
da ta dace, ta hanyar ba da shawarwari har zuwa kammaluwar wannan bincike. Allah
ya saka musu da mafificin sakamako.
Ina godiya maras iyaka ga dukkan malamaina na Sashen
Nazarin Harsunan Nijeriya a Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato. Babu shakka, na
amfana da koyarwarsu a fannoni daban-daban da kuma taimakonsu wanda shi ya ƙara
ba ni ƙarfin guiwa na kai wannan mataki na fagen ilmi. Daga cikin su akwai, Shugaban
Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya Farfesa Bello Bala Usman da Farfesa Haruna Abdullahi
Birniwa da Farfesa Aliyu Muhammadu Bunza da Farfesa Salisu Ahmed Yakasai da Farfesa
Atiku Ahmad Dunfawa da Farfesa Abdulhamid Ɗantumbishi da Farfesa Ibrahim Abdullahi
Sarkin Sudan da Farfesa Yakubu Aliyu Gobir da Dokta Abdullahi S. Gulbi da kuma Dokta
Nasiru Aminu da Dokta Yahaya Idris da Dokta Dano Balarabe Bunza da Dokta Isah Muhammad
da Dokta Nazir Ibrahim Abbas da Dokta Muhammad Mustapha Umar da Dokta Musa Shehu
da Dokta Rabi’u Aliyu Rambo da Malam Sama’ila Umar da Malam Jamilu Ibrahim Mukoshy
da dukkan ma’aikatan Sashe.
Ina kuma miƙa godiya ga dukkan malamaina na Sashen
Nazarin Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna, musamman Farfesa
Ibrahim Malumfashi wanda ya taimaka mani ta fuskoki da dama domin ganin wannan aikin
bincike bai samu tangarɗa ba. Haƙiƙa na fa’idantu da dukkan shawarwari da kuma taimakon
da ya ba ni, ba ma ga wannan binciken kaɗai ba, har ma da dukkan rayuwata ta ɗalibta.
Na gode.
Dole ne in gode wa Jami’ar Jihar Kaduna bisa damar
da ta ba ni in yi wannan karatun tare da ɗaukar nauyinsa. Na gode, Allah ya ƙara
ɗaukaka jami’ar Jihar Kaduna. Ƙarfafa gwiwa da goyon bayan da na samu daga abokan
aikina na Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe ba kaɗan ne ba. Ina
miƙa godiyata ga Dokta Alamuna Nuhu da Dokta Rabiu Bashir da Dokta Usman Aliyu da
Dokta Aliyu Isah Sulaiman da Dokta Ibrahim Shehu Liman da Dokta Sama’ila Mijinyawa
da Malam Abdullahi Mujaheed da Malam Musa Muhammad Sani da sauran su. Allah ya saka
masu da alheri, amin!
Ina miƙa godiyata ga mahaifana Malam Yusuf Nadabo Musa
da Marigayiya Malama Bilkisu Adamu kan raino da tarbiyya da haƙurin da suka yi ta
yi da ni tun daga haihuwata zuwa yau. Na gode.
Ba zan taɓa mantawa da yayana Hamisu Yusuf ba, wanda
ya tsaya a matsayin ubana, ya kuma ɗauki ɗawainiyar magance duk wata matsalar da
ta tinkaro ni a harkar karatuna. Haƙiƙa ya taka muhimmiyar rawa a rayuwata ta ɗalibta
wanda ba zai yiwu in manta ba. Allah ya saka masa da mafificin sakamako, ya kuma
albarkaci zuriyarsa. Wata godiyar zuwa ga yayana Sadisu Yusuf Nadabo, sauran ‘yan
uwana, yayye da ƙanne da iyaye waɗanda suka taimaka da shawarwari da addu’o’insu,
ina godiya, Allah ya bar zumunci.
Ba zan taɓa yin tuya in manta da albasa ba. Wajibi
ne in miƙa ɗimbin godiyata zuwa ga aminina, Buhari Salisu (Coach), wanda ya taimaka
ƙwarai da gaske wajen ganin ya share mani hawaye a duk lokacin da wata matsala ta taso min musamman a gida. Na gode,
Allah ya bar zumunci.
Har abada ba zan manta da abokan karatuna da muka faro
wannan gwagwarmaya a jami’ar Umaru Musa Yar’adua ba, wato Abdullahi Mujaheed da
Abdurrahman Aliyu, mun faro tafiyar tare Allah bai ƙaddara za mu kammala tare ba.
Allah ya sa mu gudu tare, mu tsira tare, mu shiga aljanna
tare. Allah ya saka da alheri ya kuma cika mana burinmu.
Dokta Muhammad Abdullahi Maigari (Al-nassarawy) na
Jami’ar Al-Qalam, Katsina, shi ma ba ƙashin yarwa ba ne, kasancewar ya nuna kulawarsa
ta hanyar yawaita tuntuɓa ta kan ina aka kwana? Jinjina a gare ka bisa godiya da
kulawa. Allah ya bar mu tare, ya kuma bar zumunci ya cika mana burin da muka sanya
a gaba, amin. Abokin karatuna Shamsuddeen Isma’il ya taimaka min ta fuskoki da dama
a tsawon zamana a jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato. Allah ya saka masa da alheri
ya raya zuri’arsa.
Ina miƙa wata dunƙulalliyar godiya ga mai ɗakina Safiya
Hamisu (Maman Malam) bisa haƙuri da juriyar rashin zamana a gida da ta yi a dalilin
wannan bincike. Alal haƙiƙa ba don haɗin kai da ƙoƙarin kula da gida da yara da
ƙarin ƙarfin gwiwar da ta yi ta ba ni ba, wanda hakan ya samar mani da natsuwa,
da aikin zai iya samun cikas a kan hanya. Na gode, Allah ya ƙara mana danƙon soyayya
ya bar mu tare, ya kuma raya mana zuri’armu bisa kyakkyawar tafarki. ‘Ya’yana, Ibrahim
(Malam) da Ruƙayya, sun nuna juriya da haƙurin rashin ganina a gida a yayin gudanar
da wannan bincike. Na gode maku, Allah ya maku albarka, ya sa ku zama masu jin ƙai a gare mu da al’ummar Musulmi baki ɗaya.
A ƙarshe, ina rufewa da gode wa duk waɗanda suka taimaka
wajen ganin kammaluwar karatun nan ta kowace fuska, walau da kuɗinsu ko tunaninsu
ko iliminsu ko ƙarfinsu ko addu’o’insu, waɗanda na ambata da ma waɗanda ban iya
ambaton su ba, hakan ba yana nuna cewa na manta da su ne ba. Na gode, Allah ya saka
wa kowa da alheri, amin.
TITLE PAGE i
SADAUKARWA ii
CERTIFICATION iii
GODIYA iv
ƘUNSHIYA viii
ABSTRACT xiii
TSAKURE xiv
BABI
NA ƊAYA 1
GABATARWA 1
1.0
Shimfiɗa
1
1.1
Dalilin Bincike 3
1.2
Manufar
Bincike 3
1.3
Muhimmancin Bincike 4
1.4
Farfajiyar Bincike 5
1.5
Tambayoyin Bincike 5
1.6
Naɗewa 6
BABI NA BIYU 7
BITAR AYYUKAN DA SUKA GABATA 7
2.0
Shimfiɗa
7
2.1
Kundayen Bincike 7
2.1.1
Kundayen Digiri Na Uku 7
2.1.2
Kundayen Binciken Digiri Na Biyu 11
2.1.3
Kundayen Binciken Digiri Na Ɗaya 19
2.2
Maƙalu
21
2.2.1 Bugaggun Maƙalu 21
2.2.2 Maƙalu Da Ba A Buga
Ba 27
2.3
Bugaggun
Littattafai 31
2.4 Bayanan Intanet 36
2.5
Hujjar Ci Gaba Da Bincike 38
2.6
Naɗewa 39
BABI NA UKU 40
HANYOYIN GUDANAR DA BINCIKE 40
3.0 Shimfiɗa
40
3.1 Hanyoyin Tattara Bayanai 40
3.2 Manyan Hanyoyin Tattara Bayanai 40
3.2.1 Bibiyar Tarihi Da Karance-Karance
Kan Abubuwan Da Suka Shafi Zube 40
3.2.2 Hira Da Masana Da ‘Yan Siyasa 41
3.3 Ƙananan Hanyoyin Tattara Bayanai 41
3.3.1 Ziyara Zuwa Ɗakunan Ajiyar Littattafai
Domin Nazari 41
3.3.2 Amfani Da Na’urorin Zamani 42
3.4 Ra’in Bincike 42
3.5 Naɗewa 46
BABI NA HUƊU 47
SIYASA A RUBUTACCEN ADABIN HAUSA 47
4.0 Shimfiɗa 47
4.1 Ma’anar siyasa 47
4.2 Samuwar Siyasar Zamani ga Hausawa 51
4.2.1 Siyasar Addini 51
4.2.2 Siyasar Jam’iyya 53
4.3 Ma’ana da samuwar Rubutaccen
Adabi Hausa 65
4.4 Ma’ana da Samuwar Rubutaccen Adabin Siyasa 66
4.4.1
Rubutattun Waƙoƙin Siyasa 67
4.4.2 Rubutaccen Zube na Siyasa 69
4.4.3 Rubutaccen Wasan Kwaikwayo na Siyasa 74
4.5 Dalilan da suka Haifar da Ƙamfar wasu Ɓangarori na Rubutaccen Adabin Siyasa 75
4.5.1 Tasirin Ilimin Addinin Musulunci 76
4.5.2 Mulkin Soja 77
4.5.3 Ɓullowar Finafinan Ƙasashen Waje 79
4.5.4 Tasirin Soyayya 80
4.5.5 Ƙarancin Ilimin Siyasa Ga Matasa 81
4.6 Dangantakar Siyasar Addini da Siyasar Jam’iyya 82
4.6.1 Muhimmancin
Ilimi a cikin Siyasar Jam’iyyu 89
4.6.2 Aƙidu Da Matsayinsu A Fagen Siyasar Jam’iyyu 85
4.6.3 Danganta ‘Yan Siyasa Da Masu Mulki da
Manyan Madogaran Addinin Musulunci 97
4.6.4 Amfani da Daraja ko Matsayi wajen
Tallata Ɗan Takara 106
4.7 Tallata ‘Yan Siyasa Da Ɗaukaka Ko Martabar
Shugabannin Siyasa 112
4.8 Matsayin Mata a Cikin Siyasar
Jam’iyyu 117
4.9 Takura wa Abokan Hamayya 129
4.10 Yarfe ga Abokan Hamayyar Siyasa 144
4.10.1 Yarfe na Addini 148
4.10.2 Yarfe na Ƙima/Halaye
154
4.10.3 Yarfe na Tafiyar da Shugabanci 163
4.11 Naɗewa 167
BABI NA BIYAR 169
SIYASAR
Jam’iyyu DA CIGABAN AL’UMMA DAGA CIKIN RUBUTACCEN ADABIN HAUSA 169
5.0 Shimfiɗa 169
5.1Manufar Siyasar Jam’iyyu 169
5.1.1 Samar da Walwala ga ‘Yan Ƙasa 175
5.1.2 Wadata ‘Yan Ƙasa 181
5.1.3 Sama wa Ƙasa da ‘Yan Ƙasa ‘Yanci 183
5.1.4 Samar da Tsaro 190
5.2 Gwagwarmayar Samun Cigaban Al’umma
a Siyasance 193
5.2.1 Kafuwar Jam’iyyu 194
5.2.2 Tallata Jam’iyyu 196
5.2.3 Tallata ‘Yan Takara 201
5.2.4 Yaƙin Neman Zaɓe 210
5.2.5 Rarrashin Jama’a 217
5.2.6 Sauya Sheƙa 220
5.2.7 Haɗakar jam’iyyu 231
5.2.8 A-Kasa-A-Tsare 237
5.3 Abubuwan da suke kawo Cikas ga Samun
Cigaba 243
5.3.1 Alƙawarin Ƙarya 244
5.3.2 Maguɗin Zaɓe 250
5.3.3 Sayen Ƙuri’a 264
5.3.4 Angulu da Kan Zabo 269
5.3.5 Bangar Siyasa 272
5.3.6 Zuba Jari a Siyasa 282
5.3.7 Siyasar Ubangida 287
5.3.8 Amfani da Kuɗi 293
5.3.9 Amfani da Malaman Addini 299
5.3.10 Barazana ga Ma’aikatan Gwamnati 307
5.3.11 Fankama 311
5.4 Dangantaka Tsakanin Masu Mulki da Waɗanda
ake Mulka 317
5.4.1 Yadda Talakawa suke kallon ‘Yan
Siyasa 318
5.4.1.1 Maƙaryata 319
5.4.1.2 Mayaudara 321
5.4.1.3 Azzalumai 327
5.4.1.4 Maciya Amana 330
5.4.2 Yadda Masu Mulki da ‘Yan Siyasa suke
Kallon Talakawa 333
5.4.2.1 Makwaɗaita 333
5.4.2.2 Matalauta 337
5.4.2.3 Wawaye 339
5.4.2.4 Cima-zaune 342
5.5 Naɗewa
344
BABI NA
SHIDA 346
KAMMALAWA 346
6.0 Shimfiɗa 346
6.1 Taƙaitawa 346
6.2 Sakamakon Bincike 350
6.3 Shawarwari 351
6.4 Naɗewa 352
MANAZARTA… 353
HIRA DA TATTAUNAWA 367
RATAYE NA 1 368
RATAYE NA 2 368
ABSTRACT
This
research, titled “Historical Development Of Party
Politics From Hausa Written Prose, 1950 – 2023”, is an effort to study the historical development
of party politics in Northern Nigeria. The study examines how various political
developments have evolved historically, from 1950 to 2023, as reflected in Hausa
written prose. The motivation for conducting this research arose from observing
the different political eras that authors of prose have documented, which highlight
the dynamics of party politics. This prompted a review of works such as newspaper
articles, letters, political speeches, and fictional narratives to uncover themes
related to the history of political parties. The aim of the research is to understand how party politics
developed over time and the role that literary works have played in preserving the
history of politics while contributing to national and societal progress. To enrich
the research, consultations were made with experts and politicians. However, the
data obtained from them was insufficient, necessitating visits to libraries, research
institutions, and internet sources for further information. The research employs the Historicism Theory framework,
ultimately uncovering that many contemporary political events in Northern Nigeria
have their roots in the early days of party politics. However, some changes have
occurred over time due to evolving circumstances. Additionally, the study identifies
certain political approaches that promote societal progress and others that hinder
it. The research provides insights into how past political events have shaped the
current state of politics and societal development in Northern Nigeria.
TSAKURE
Wannan bincike mai taken, “Tarihin Ginuwar Wasu Al’amuran Siyasar Jam’iyyu A Cikin Rubutun Zuben Hausa Daga 1950-2023” wani yunƙuri ne na nazarin tarihin ginuwar siyasar jam’iyyu a Arewacin Nijeriya. A wannan binciken an yi nazarin yadda wasu al’amuran siyasa suka ginu a cikin tarihi, tun daga shekarar 1950 zuwa 2023 daga cikin rubutaccen zuben Hausa. Tunanin gudanar da wannan bincike ya taso ne duba da yadda aka ratsa wasu zamunnan siyasa mabambanta, waɗanda marubutan zube suka samar da rubuce-rubuce da suke ɗauke da hoton siyasar jam’iyyu a cikinsu. Wannan ya sa aka ga dacewar lalubo ire-iren waɗannan ayyukan da suka shafi jaridu da wasiƙu da jawaban siyasa da ƙagaggun labarai domin fito da wasu batutuwan tarihin siyasar jam’iyyu. Manufar binciken ita ce ƙoƙarin gano yadda siyasar jam’iyyu ta ginu a cikin tarihi, da kuma irin gudummuwar da ayyukan adabi suka bayar wajen adana tarihin siyasar da cigaban ƙasa da kuma al’umma. Domin inganta binciken an tuntuɓi masana da ‘yan siyasa, bayanan da aka samu a daga gare su ba su wadatar ba sai da aka ziyarci ɗakunan karatu da cibiyoyin bincike da shafukan intanet domin neman ƙarin bayanai. Ra’in Tarihanci (Historicism Theory) ne aka gudanar aikin a kansa, wanda daga ƙarshe binciken ya gano wasu abubuwan da suke faruwa cikin al’amuran siyasar Arewacin Nijeriya a yau, sun samo asali ne tun daga farkon siyasar jam’iyyu, sai dai ‘yan sauye-sauye da aka riƙa samu saboda sauyawar zamani. Haka kuma binciken ya gano waɗansu hanyoyi da ake bi a siyasance domin samar da ci gaban al’umma da kuma abubuwan da suke sawa a rasa wannan cigaban a cikin siyasa. Binciken ya ba da damar sanin me jiya ta haifar da halin da ake ciki a yau a fagen siyasa da cigaban al’ummar Arewacin Nijeriya

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.