𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam Shin ya halatta a yi sallar nafila bayan sallar asuba da kuma sallah bayan sallar la'asar?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumusalam
warahmatallahi wabarakatuh
Bai halatta yin sallar
nafila bayan sallar asuba.
Saboda hadisai
ingantattu wanda bukhari da muslim suka ruwaito, daka Annabi sallallahu Alaihi
wasallam Ya ce: ( Babu sallah bayan asuba harsai rana ta fito) awata ruwayar
kuma ( harsai rana ta daga, babu sallah bayan la'asar harsai rana
tafadi).wadannan sune lokutan da'aka hana yin sallah a cikinsu. Bai halatta
mutum yayi sallar nafila a cikinsu, saidai sallar datake da sababi, kamar
sallah jana'iza ko sallar gaisuwar masallaci, ko kuma sallar farillah data
kubucewa mutum baiyiba saboda mantuwa ko bacci, saboda fadin Annabi sallallahu
Alaihi wasallam ( Wanda yai bacci baiyi sallah ba ko ya mantata baiyiba, to ya
sallaceta lokacin daya tuna ko ya farka daka bacci, bata dawata kaffara sai
wannan).
Idan yamanta baiyi wata
sallah ba ko bacci yadaukeshi, zaiyita koda bayan sallar asuba ne ko bayan
sallar la'asar, haka idan rana ta kisfe bayan sallar la'asar za ai sallar
kisfewarta awannan lokacin. Haka sallar gawa bayan sallar asuba ko bayan sallar
la'asar duk hanin bai shafi irin wadannan salloli masu sababi ba.
Amma wanda raka'a biyu
da'akeyi kafin sallar asuba ta kubuce masa baiyi ba, ya halatta yayita bayan
asuba ɗin, abunda yafi yabari sai bayan rana ta fito yaramata,
domin Annabi sallallahu Alaihi wasallam yai umarni dahaka.
Idan yasallaceta bayan
Asuba tayi saboda Annabi sallallahu Alaihi wasallam yaga wani mutum yana sallah
bayan sallar asuba saiya ce dashi ( Zakai sallar asuba raka'a huɗu ne) saiya ce: ya manzan Allah Sallallahu Alaihi
Wasallam raka'atanul fajrice banyiba kafin sallah, sai Annabi sallallahu Alaihi
wsallam yai masa shiru baice masa komai ba, Wannan saiya nuna babu laifi
ramata, amma sallar nafila haka kawai taneman lada haramunne yinta bayan sallar
asuba harsai rana tafito sosai, haka haramunne yinta bayan sallar la''asar
harsai rana ta fadi.
WALLAHU A'ALAMU.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.