Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Yin Sallah Nafila Bayan Sallah Asuba Da La'asar

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum malam Shin ya halatta a yi sallar nafila bayan sallar asuba da kuma sallah bayan sallar la'asar?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumusalam warahmatallahi wabarakatuh

Bai halatta yin sallar nafila bayan sallar asuba.

Saboda hadisai ingantattu wanda bukhari da muslim suka ruwaito, daka Annabi sallallahu Alaihi wasallam Ya ce: ( Babu sallah bayan asuba harsai rana ta fito) awata ruwayar kuma ( harsai rana ta daga, babu sallah bayan la'asar harsai rana tafadi).wadannan sune lokutan da'aka hana yin sallah a cikinsu. Bai halatta mutum yayi sallar nafila a cikinsu, saidai sallar datake da sababi, kamar sallah jana'iza ko sallar gaisuwar masallaci, ko kuma sallar farillah data kubucewa mutum baiyiba saboda mantuwa ko bacci, saboda fadin Annabi sallallahu Alaihi wasallam ( Wanda yai bacci baiyi sallah ba ko ya mantata baiyiba, to ya sallaceta lokacin daya tuna ko ya farka daka bacci, bata dawata kaffara sai wannan).

Idan yamanta baiyi wata sallah ba ko bacci yadaukeshi, zaiyita koda bayan sallar asuba ne ko bayan sallar la'asar, haka idan rana ta kisfe bayan sallar la'asar za ai sallar kisfewarta awannan lokacin. Haka sallar gawa bayan sallar asuba ko bayan sallar la'asar duk hanin bai shafi irin wadannan salloli masu sababi ba.

Amma wanda raka'a biyu da'akeyi kafin sallar asuba ta kubuce masa baiyi ba, ya halatta yayita bayan asuba ɗin, abunda yafi yabari sai bayan rana ta fito yaramata, domin Annabi sallallahu Alaihi wasallam yai umarni dahaka.

Idan yasallaceta bayan Asuba tayi saboda Annabi sallallahu Alaihi wasallam yaga wani mutum yana sallah bayan sallar asuba saiya ce dashi ( Zakai sallar asuba raka'a huɗu ne) saiya ce: ya manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam raka'atanul fajrice banyiba kafin sallah, sai Annabi sallallahu Alaihi wsallam yai masa shiru baice masa komai ba, Wannan saiya nuna babu laifi ramata, amma sallar nafila haka kawai taneman lada haramunne yinta bayan sallar asuba harsai rana tafito sosai, haka haramunne yinta bayan sallar la''asar harsai rana ta fadi.

WALLAHU A'ALAMU.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments