𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum warahmatullah Malan. An yini Lafiya ya koqari Dakuma karatu Allah ya taimaka Kuma Muna godiya Sosai. na ce Malan Dan Allah a daure aqara mana karatu Dakuma dogon bayani kan azumin tasu'ah Dakuma ashura Dan wasu Suna Ganin Kamar ranar da zai fada ranar yin azumin tasu'ah Dakuma ashura Kamar Wai ba ranakun da'ake son yin azumin ba ne to shi ne nake so Malan yaqara wayar mana dakai.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis salaam wa
rahmatullahi wa Barkatuhu, Ameen Ya Yayyu Ya Qayyum 🤲🏽.
Toh 'Yar uwa ai hadisi
ya zo daga Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam cewa, "Kada ku yi
azumi ranar asabar sai abin da aka farlanta muku Shi". (Abu-dawud hadisi
mai lamba ta :2423).
Sai dai malamai sun yi
saɓani akan ingancin wannan hadisin, akwai malaman da suka
tafi akan cewa hadisin karya ne, Abu-dawud ya hakaito hakan daga Imamu Malik.
Akwai waɗanda suka inganta shi, akwai kuma malaman da suka ce
hadisin akwai kuskure a ciki, saboda ya Saɓawa hadisin da ya fi shi inganci, inda Annabi Sallallahu
Alaihi Wasallam yake cewa; "kada ɗayan ku ya
azumci ranar juma'a, sai in ya azumci yinin da yake gabanin ta, ko kuma wanda
yake bayan ta". (Bukhari a hadisi mai lamba ta 1884,). wannan hadisin yana
nuna halaccin azumtar asabar ga wanda ya azumci juma'a.
Akwai malaman da suka
tafi akan cewa wannan hadisin an goge shi da wasu hadisan, saboda yadda aka
rawaito cewa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yana azumtar mafi yawan kwanaki
a cikin watan Sha'aban, wannan sai ya nuna cewa dole asabar ma za ta fado a
cikin azumin sa, ga shi kuma Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam. Ya
halatta yin irin azumin Annabi Dawud, wanda za ka yi azumi yau ka sha gobe, ke
nan babu yadda za a yi mutum yayi azumin Annabi Dawud ba tare da Asabar ko
Juma'a ta fado a cikin Azumin sa ba.
Zancen miliyoyin malamai
shi ne ya halatta ayi azumi ranar asabar ga wanda yayi Azumi ranar juma'a. Don
neman karin bayani duba: Tahzibu sunani Abidawud 1\469
Sa'annan Azumin indai
sun fado a ranar Juma'a ko Ranar za a yi su wadda su waɗannan Azumin hanin da ake Faɗi akan sa babu shi dole ne idan Azumi ya Fado a ranar
Juma'a, ko Asabar ko Lahadi toh mutum zai yi Azumin sa, kamar misalin Azumin
Arfa.
Azumin Arfa sai ya Faɗo a ranar asabar ne, ko Juma'a ko Lahadi duk za a yi
domin babu wannan hanin a kansa, Ku Dena Amfani da maganar jahilai cewa wai bai
halatta ayi ba, Karfi da yaji a Haramta Muku samun wnnan ladan ku, Akan Cewa
Wai ba a yin Azumi ranar Ranar asabar ko Azumin Ranar Juma'a. Shakka babu
Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya hana Musulmai yin Azumi a ranar Juma'a kaɗai da asabar, _Ma'ana ki ware ranar Juma'a ko asabar kaɗai, ki ce a wannan ranar ne zakiyi Azumin ki ko Azumin
Ramako ko wani Azumin da kike so ki samu Ladan ki, ko Kuma ki ce sai Ranar
lahadi kaɗai, duk Annabi
Sallallahu Alaihi Wasallam ya Hana yin Azumi a Irin Waɗannan ranakun. Toh amma Wannan Azumin da Za a Yi a Ranar
Juma'a da asabar Bai shafi hanin da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yake nufi
ba, domin Azumi ne na Nafila Kuma Azumi ne wadda yake da sababi irin wancan ba
ne.
Sabida haka Azumin ARFA,
Azumin ASHURA da TASU'A, duk Wannan idan sun Faɗo a irin waɗannan ranar Za a
iya yin Azumin nan babu Wannan hanin. Sabida haka a ji tsoron Allah a bar
mutane su yi Ƙayan su idan ke
ba zakiyi ba toh kada ki cewa wasu kada su yi. Idan Kai ba zakayi ba toh Bai
kamata ka Haramtawa Bayin Allah yin Azumin su ba. Idan har Nafila na Zama Mai
sababi ce, toh ana iya yin sa ko da a lokacin Hani ne domin Halin Bai shafe shi
ba, balle ma ai wannan Azumin ya zo daidai da abun da Annabi Sallallahu Alaihi
Wasallam ya ce Idan za a yi asabar toh dole ne a fara shi daga Juma'a. Kuma ai
wannan Azumin ya fara daga Juma'a ne zuwa Asabar kin ga ke nan daidai ne, ko
kuma idan ba ki samu yin Juma'a ba toh sai kiyi Asabar naki da Lahadi duk ya
halatta.
Cewa akayi, ayi Azumin
ranar Tasu'a Da Ashura ne, ai bawai kaine ka kayyade wannan ranar cewa dole
zakayi Azumin a wannan ranar ba, Allah da iKon sa ne ya sa Azumin zai faɗa a ranar Juma'a da asabar, ke nan babu wani hani a
kansa, sai dai idan kaine za ka Hana kanka. (Bukhari 1985, MUSLIM 1144).
Malamai Sun yi magana akan ba za a yi Azumi a ranar Juma'a ko asabar kaɗai ba, (Tirmizy 744 da abu-dawud 2421, Bnu majah 1726).
duk Suna magana Akan ba a yin Azumin ranar asabar ko Juma'a kaɗai sai wadda Allah ya farhanta muku shi.
Sabida Haka wannan
Azumin Mai sababi ne Bai dace ace ana ta yada abun da Bai dace ba ko ba a San
hukuncin abun ba, a Hana mutane yin Aikin Ladan su, kowa sai ya amsa tambaya a
ranar Alkiyama. Allah ya tsare. ana ta yadawa status ne a ko Ina a social media
ai Bai halatta ayi Azumin ba tunda ranar Juma'a da asabar ba, waye gaya ma? a
Rika fahimtar Hadisan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam dakyau don Allah.
Allah ya shirya.
Sa'annan ko ana bin ki
Bashin Azumin watan Ramadan kina iya yin wannan Azumin Tasu'a Da Ashura ɗin ki daga baya kiyi niyyar Rama Azumin Farillah naki shike
nan, sa'annan ko kin makara kina iya wucewa da wannan Azumin matukar za ki iya,
sai dai Sharadin ya kasance cewa tun daga lokacin da kika farka har zuwa safiya
ba ki ci komai ba, toh sai ki wuce da Azumin ki, idan kuma kin ci wani abun toh
shike nan ba za kiyi Azumin wannan Yinin ba, shi Azumin Nafila ko mutum bai
kwana da Niyya ba zai iya kulla niyyar sa da Safe indai bai ci komai ba, domin
haka inda Hadisan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam suka nuna Hakan cewa
Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yana zuwa gidan sa ya ce akwai Karin Kumallo?
Idan an ce eh! Sai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya karɓa Abincin ya ci, idan an ce babu sai Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce toh ya wuce da Azumi, sabida haka za ki iya
yin haka kema indai za ki iya yin sa.
Baya ga Hakan idan ba ki
samu damar yin Azumin Tasu'a ba toh sai kiyi na Ashura sai ki haɗa shi da ranar Lahadi, Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam
ya Sanya yin Azumin Tasu'a ne a dalilin cewa a Saɓawa Yahudawa da Nasara, sabida haka idan ba ki samu yin
na ranar Juma'a ba toh sai kiyi Asabar da kuma Lahadi yayi. Allah ya amsa mana
ya bamu Ladan sa Ameen Ya Yayyu Ya Qayyum 🤲🏽.
Wallahu A'alamu.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.