HADIN KAN MUSULMI A WAJEN AIKIN HAJJI
Kusan duk shekara ana samun karin kusantar juna tsakanin Malamai Ahlus Sunna da Malaman bidia a wajen Aikin Hajji, la'alla da nufin neman hadin kan al'ummar Musulmi.
To, lallai Hadin kan Musulmai lamari ne mai girma,
mai muhimmanci. Abu ne da Allah ya wajabta shi, kuma ya fadi yadda ake yinsa.
To a yau gama garin mutane, da 'yan siyasa, da
shugabannin gomnati, da 'yan boko jahilai suna so Musulmai su hada kai. To amma
su irin wadannan mutane da yake mafi yawansu sun jahilci iyakokin abin da Allah
ya saukar wa Annabinsa (saw), irin hadin kan da suke so a yi ba irinsa Allah ya
ce a yi ba. Kuma ba irinsa ne hadin kai mai haifar da d'a mai ido ba.
Asali hadin kan da Allah ya yi umurni da shi, shi
ne haduwa a kan riko da igiyar Allah, bin Alkur'ani da Sunna, haduwa a kan
Musluncin da Sahabbai da Tabi'ai suka rayu a kai. Idan kowa ya bar bidi'arsa,
dan Darika ya bar Sufancinsa, dan Shi'a ya bar Rafidhancinsa, dan Kala-kato ya
bar Qur'aniyancinsa, ya zo aka hadu a kan Alkur'ani da Sunnar Annabi (saw),
bisa tafarkin Musulman farko to shi ne an yi hadin kai na gaskiya, za a dena
fada da juna. A nan ne za a samu hadin kan Musulmi mai dorewa.
Amma saboda jahilci ko maslaha sai wadancan mutane
suke zaton za a iya hadin kai ba tare da kowa ya bar bidi'arsa ba. To alal
hakika wannan ba zai samu ba, sai dai idan wanda yake kan tafarkin Sunna ya
fifita maslahar samun abin duniya, na dukiya da daukaka, ya koma girmama
Malaman bidi'a, yana kambama su. Duk don a nuna neman hadin kai, da nuna
sassaucin ra'ayi, da nuna cewa Ahlus Sunna ba sa yin abin da ake zarginsu da
shi na kafirta 'yan Darika da bin tsattsauran ra'ayi, da makamancin haka.
Lallai yanzu muna zamani ne na fitina, an kakaba
mana talauci, da yawa cikin masu wa'azi suna ra'buwa da 'yan siyasa, don samun
abin duniya, da daukaka da shahara. Don haka malami ya tsare Addininsa a wannan
yanayi yana da wahala, kuma kokarin hakan yana cikin Jihadi. Don kawai biyan
muradun gomnati da bukatun 'yan siyasa kada ka yi sakaci da Manhajinka na
tafarkin Sunna.
Allah ya kare mana Addininmu, ya ba mu wadatar
zuci, ya tabbatar da mu a kan tafarkin gaskiya.
Dr.
Aliyu Muh'd Sani
18
June, 2024
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.