BANBANCIN SUFAYE A YAƘIN IRAN DA IZRA'ILA
Duk da munin Aƙidun Sufaye, amma ban san suna da tarihin
ta'addanci a kan al'ummar Muaulmi ba.
A wannan zamani, za a iya cewa: ƙasar Moroco ita ce ƙasar da ta yi fice wajen tsayawa a matsayin gomnati mai bin tafarkin Sufanci, amma ban san tana da manufa ta mamaya, ko manufa ta zubar da jini da ta'addanci a kan sashen al'ummar Musulmi ba, ko abokan saɓaninsu.
Wannan ya sa idan Izra'ila za ta yaƙi Moroco, ko wata ƙasa da za a iya cewa ta
Sufaye ce, to za mu goyi bayanta, saboda ba mu san Sufaye da zalunci da
ta'addanci, da mungun nufi a kan al'ummar Musulmi ba.
Saɓanin Rafidha ƴan Shi'a masu mummunan
shiri na mamayar ƙasashen Musulmai, tun daga ƙasashen Larabawa, har ƙasashen Afirka, da manufar ɗaukar fansar
jinin Sayyidina Hussain (ra) a kan Nawasib, wato Ahlus Sunna (Sunny), waɗanda suke ɗauka a matsayin
maƙiya Ahlul Baiti, jikanun
Yazidu, mashaya jinin Hussaini (rs). A kullum suna shelanta sai sun ɗau fansa.
Wannan ya sa Gomnatin Rafidha ƴan Shi'a ta
"Wilayatul Faƙeeh" (ولاية الفقيه), mai mulki a Iran, take da
mungun nufi a kan Ahlus Sunna da ma'anarsa ta babban zaure (Sunny). Wato waɗanda suke kira "Nasibawa". Suka yi wani tsari
(Plan) na shekara hamsin (الخطة الخمسينية), don
mamaye ƙasashen Musulmi, har
Makka da Madina, da gasa musu aya a hanu. Sun yi aiki da wannan tsari a ƙasashen Larabawa;
gabashin Saudiyya, Bahrain, Kuwait, da kuma Yamen, Iraq da Syria da Labanon da
sauransu. Hatta ƙasashen Afirka ba su tsira daga tsarin ba, ta hanyar abin da suka kira da
cigaban mamayar Iran "تصدير الثورة"
(Export of revolution). Tare da ɗaukar nauyin ƙungiyoyin ta'addanci
masu zubar da jinane, da ɓarna a bayan ƙasa.
A taƙaice, duk wanda ya san shirin Iran, da mugun nufinta a kan al'ummar
Musulmi, ya san cewa; idan sharrin Iran bai fi sharrin Izra'ila ba, to za su yi
kunnen doki. Ka tambayi tarihi a kusan nan, ka ji irin ta'addancin da Iran ta
yi a Iraq, Syria, da Yamen, dss, da muzgunawar da take yi wa Ahlus Sunna ƴan ƙasar ta Iran. Wanda hatta Masallaci ba su da ikon
mallaka.
A taƙaice, wannan faɗa da ake yi na
Iran da Izra'ila, sauran Musulmai ba ruwansu da shi. Saboda ba faɗa ba ne na Addini. Azzalumai ne biyu suke faɗa da juna, saboda maslahohinsu na mamayar ƙasashen Musulmai.
Don haka idan Izra'ila ta ba da kashi wa Iran, sai
mu taya ƴan Syria da Iraq dss
murna. Haka idan Iran ta lallasa Izra'ila, sai mu yi murna, mu taya Falasɗinawa murna.
Sabda haka Rafidha azzalumai ne masu mungun nufi a
kan Musulmai, kamar yadda Yahudawa ma haka, saɓanin Sufaye, su ba mu sansu da haka ba.
Ya Allah ka sa su ruguza junansu, ka dirkake su
gaba ɗaya.
~
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.