𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum malam Ina fatan kana lafiya. Malam Ina da tambaya, idan mutum ya samu sallahr juma'a Amma bai samu Khuduba ba (ya zo an tada ikama) mene ne hukuncinsa? Inason ayi mana bayani akan falalar zuwa masallacin juma‘a da wuri
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus salam
Warahmatallahi Wabarkatahu
Da yawa mukan shagalta
da wasu al‘amura na rayuwar duniya har mu kwashe lokaci mai tsawo ba tare da
mun damu ba, amma cikakkun awowi biyu (2hrs) ba zamu iyayi a wurin bautar Allah
cikin nishad‘i ba. A ranar Juma‘a ana son zuwa Masallaci da wuri domin samun
babbar rabo!
An karɓo Hadithi daga: Abu Hurairah (RA) ya ce: Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: ((Duk wanda yayi wanka, sannan ya tafi
Masallacin Juma‘a (da wuri), yayi Sallah (ta nafila) gwargwadon abinda ya samu,
sannan ya saurara, har Liman ya fito domin yin Khudubah, ya saurari Khudubah
aka yi Sallah tare da shi: to, an gafarta masa abinda ke tsakanin Juma‘ar da
kuma wata Juma‘a mai zuwa, tare kuma da bashi falala ta kwanaki uku)) [MUSLIM]
Zuwa Masallacin Juma'a
da Wuri Yanada Tarin Lada Mai Yawa. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam
yana Cewa: (Wanda Yayi Wanka a Ranar Juma'a, Sannan ya Tafi Zuwa Masallaci a
Farkon Lokaci, Yanada Lada kamar Yayi Sadaka da Rakumi. Idan Yaje a Sa'a ta Biyu
kamar yàyi Sadaka ne da Saniya. Idan Yaje a Sa'a ta Uku kamar Yayi Sadaka ne da
Rago. Idan Yaje a Sa'a ta Huɗu kamar Yayi
Sadakane da Kaza. Idan Yaje a Sa'a ta Biyar kamar yayi Sadakane da Dabino. Idan
Liman Yazo Ya Hau kan Mimbari Sai Mala'ikun su Rufe Takardunsu su tsaya Suna
Sauraran Khuduba).
Wanda ya tafi a kasa
zuwa Sallar Juma'a Yana Samun Ladar Azumin Shekara Guda da tsayuwar dare na
Shekara Guda ga Kowane taku. Daga Ausi bn Ausi (ra) Daga Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce: (Dukkan Wanda Yayi Wanka a Ranar Juma'a
(Wankan Juma'a) Yayi Sammako Yaje da Wuri, ya Zauna ya Saurari khuduba yayi
shiru beyi Magana ba, Ya kasance yana da Lada ga Kowane Taku da Yayi Zuwa
Masallaci, Yanada Ladar Azumin Shekara Guda da tsayuwar dare na Shekara Guda).
Saboda haka ‘Yan‘uwa mu
dinga zuwa Masallaci da wuri. Allah ya bamu ikon gyarawa.
WALLAHU A'ALAMU
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.