𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum ina fatan malam nacikin koshin lfy mlm matsalan dake damuna achan da ina yin istimna,i amma yanzu cikin ikon Allah nadaina saboda ina biye da shafin zauren fiqhu a facebook. mlm don Allah ina son ataimakamani saboda kusan kullum inafamada mafarkin inasaduwa da mace amma yanzu nadaina sai dai yanzu ina fama da bugawar kirji faduwan gaba mlm don Allah ina neman taimako albarkancin Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallam. kahuta lfy daga Ibrahim sokoto
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.
Istimna'i wanda a turance ake kiransa
'Masturbation' wani abu ne da wasu samari har 'yan mata ke yi ta hanyat taɓa al'aurorinsu domin biya wa kansu bukata.
Yana haifar da matsaloli da yawa ga lafiyar mutum
har addininsa ma. Daga cikin matsalolin akwai samun shafar aljanu ta sanadiyyar
wannan dalilin. Sai kuma raunin idanu, raunin al'aura, rikicewar tunani,
dakushewar kwakwalwa (wato toshewar basira) faduwar gaba Da sauransu.
Kamar yadda kayi bayani, gaskiya duk waɗannan abubuwan da kakeji suna daga illolin da istimna'in
yake haifarwa. Don haka shawarar da zan baka anan ita ce ka yawaita tuba da
kuma gyara ayyukanka na addini, sannan ka yawaita zikirin Allah da karatun
Alqur'ani da nafilfili.
Ka kiyayi leka shafukan yanar gizo wadanda ke ɗauke da hotuna ko labarai na batsa. Ka kiyayi duk abinda
zai janyo maka motsawar sha'awar aikata zina. In kana da halin yin aure ma ya
kamata kayi domin tsare mutuncinka.
Matayen Aljanu sukan shiga jikin namiji saurayi
alokacin da ya keɓance kansa yana
aikata istimna'i ko a toilet ko dakinsa. Shi yasa mafiya yawan masu aikatawa
zaka samu suna da shafar aljanu ajikinsu. Haka ma mace budurwa idan ta keɓance kanta tana aikata wani abu irin wannan, to yakan
kasance mazajen aljanu su shiga jikinta.
Don haka Ka rika tofa waɗannan ayoyi da surori acikin ruwa kana sha kana shafe
jikinka dashi kullim kafin ka kwanta barci :
1. Fariha 7.
2. Ayatul Kursiyyi 41.
3. Suratu Yaseen 1.
4. Suratul ikhlas 11.
5. Suratul falaq 11.
6. Suratun Nas 11.
In shaAllahu zaka samu lafiya. Idan kuma ka gwada
waɗannan amma abun bai ta fi gaba daya ba, ka tuntubi ZAUREN
FIQHU ta kan wannan lambar kamar haka :07064213990.
WALLAHU A'ALAM.
DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.