๐๐๐๐๐๐๐❓
Assalamu alaikum Malam Shin zan iya ษaukan azumi na kwana uku Domin fatan Allah ya karษi addu'a na ya biya min wasu bukatuna?.
๐๐๐๐❗️
Wa alaikis salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.
Eh kwarai kuwa ya halatta Musulmi ya ษauki wata nau'in ibada wacce ake neman kusanci ga Allah
da ita, ya yita musamman domin neman biyan wata bukatarsa awajen Allah
Subhanahu wa Ta'ala.
Misali kamar sallolin nafila, azumin nafila,
karanta wasu surori na Alqur'ani, taimakon marayu, ciyarwa, tona rijiyoyi, Gina
makarantu ko asibitoci ko masallatai, da sauransu. Duk wanda mutum yayi tare da
kyakkyawar niyyah Allah zai karษa masa ya biya
masa bukatarsa. Idan kuma wata musiba ce yake neman yayewarta awajen Allah, zai
samu abinda ya nufa.
Hujjah kamar yadda yazo cikin hadisin Sahihu
Muslim : "Ku riskar da bakin cikinku da damuwarku ta hanyar yin sadakoki.
Allah zai yaye muku chutarku kuma ya taimakeku akan makiyanku".
Amma dai abinda akafi so ga Mumini shi ne yayi
ayyukan ibadarsa domin neman yardar Allah kaษai ba tare da neman wata amfanuwa irin ta duniya ba. Idan
kuma Allah ya dubeshi da rahamarsa ya biya masa wata bukatar duniya to
shikenan. Amma dai ba ita kaษai aka nufa ba.
Dagewa da nau'o'in ibadu musamman domin neman
yardar Allah da kusanci gareshi, sunnah ce ta salihan bayin Allah daga
magabata. Musamman idan muka kalli rayuwar mutanen kirki irin su : Fudhayl bn
'Iyadh, Imam Hasanul Basariy, Rabi'atul Adawiyyah, Nafisatul Hashimiyyah,
Hasanatul Abidah da sauransu.
Waษannan duk
Salihan bayin Allah ne da suka rayu cikin rashin wadatar abun duniya amma suna
yin ibadah dare da rana tare da yin azumin nafilah kullum don neman yardar
Allah kaษai ba tare da neman wata bukata ta duniya ba.
Idan muka duba cikin Alqur'ani zamu ga yadda Allah
yake bada labarin Annabawansa irin su Annabi Zakariyya wanda yakan tashi yayi
sallolin dare ko azumi kuma harma yayi addu'ar neman haihuwa, kuma Allah ya
biya masa bukatarsa.
Ibnu Jareer Attabariy (rahimahulLah) acikin
tafsirinsa (juzu'i na 12 shafi na 347) ya ce : "Wanda duk ya aikata wani
aikin alkhairi don neman amfanuwar duniya kaษai, kamar azumi ko sallah ko tsaiwar dare, to Allah ya ce
zai biya masa bukatar tasa ta duniya ษin, amma aranar
lahira aikin nasa zai lalace ba zai samu komai awajen Allah ba.".
A takaice dai Malamai sun raba abun kashi-kashi
kamar haka :
1. Idan mutum ya nufi lahira kaษai, Allah zai karษa ya tabbatar
masa da ladansa. Koda wasu bukatunsa sun samu tabbatuwa anan duniya, wannan ba
zai rage masa ladansa awajen Allah ba.
2. Idan mutum ya raba niyyarsa biyu, yana son
bukatar duniya, kuma yana neman lada awajen Allah, to Malamai sun yi saษani. Amma dai ra'ayi mafi karfi shi ne, Allah zai
kyaleshi da aikinsa ne. "Domin Allah ba ya karษar wani aiki sai wanda akayi dominsa kaษai" - inji Shugaba Sallallahu Alaihi Wasallam.
3. Idan kuma zallar bukatar duniyar ce kaษai agabansa, to Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya
ce : "Wanda hijirarsa ta zamto domin duniya ne ko wata mace da yake so zai
aura, to ladan hijirarsa yana cikin abinda yayi hijirar dominsa.
WALLAHU A'ALAM.
DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
๏บณُ๏บ๏บคَ๏บ๏ปงَ๏ปَ ๏บ๏ป๏ป َّ๏ปฌُ๏ปขَّ ๏ปญَ๏บِ๏บคَ๏ปคْ๏บชِ๏ปَ ๏บ๏บทْ๏ปฌَ๏บชُ ๏บ๏ปฅ ๏ปَ๏บ ๏บِ๏ปَ๏ปชَ ๏บِ๏ปปَّ ๏บ๏ปงْ๏บَ ๏บ๏บณْ๏บَ๏ปْ๏ปِ๏บฎُ๏ปَ ๏ปญ๏บَ๏บُ๏ปฎ๏บُ ๏บِ๏ปَ๏ปดْ๏ป
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
๐๐๐๐๐๐๐๐๐
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
๐
๐๐๐๐๐๐๐๐
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ษaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan ฦur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waษanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ฦarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ฦasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ษorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ฦoฦari da muke yi na tattaro muku ษimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.