SHIN MUTUM ZAI IYA YI WA KANSA ƘARIN KARATU?
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Malam Dan Allah inada tambaya Amma dai Dan Allah kada a gaji dani kada tambayoyina su fara yawa. Malam na kasance a lokacin da na taso ina yarinta karatun da nayi na islamiya ba wani sosai bane saboda na sanya wasa a lamarin Amma kuma gaskiya ko malamanmu sun sani a lokacin ina da saurin ɗaukar karatun cikin kaina sai dai kuma yanzu ina son karatun gashi kuma a inda Nike kasuwanci wlh babu islamiyya kwata kwata Amma ina ta qoqarin yiwa kaina qari da sauraron karatun sudais da na sauran maluma to sune dayake na iya tada baqi sai in ɗauko Alkur'ani ina yiwa kaina qari shin malam tambayana anan yana da kyau mutum ya dinga yiwa kansa qari?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.
A'a yadda kakeyi ɗin babu laifi saboda larurar da kake ciki. Maimakon zama
haka baka yin komai, yana da kyau ka rika karanta Alqur'anin kamar yadda na
baka shawara achan baya.
Amma kasan shi ilimi nakaltarsa akeyi daga bakunan
Malamai, babu damar mutum ya ɗauki littafi ya
karanta da kansa ba tare da samun jagoranci daga wani Malami masanin wannan
fannin ba, to hakanan shima karatun Alqur'ani fanni ne na musamman wanda yana
da Maliman dake karantar dashi bisa Qa'idodin yadda ake karantashi bisa duk
riwayar da mutum ya zaba. Amma in dai ɗauka zakayi da
kanka ka karantashi ba tare da naqaltarsa daga bakin wani malami masani akan
fannin ba, to za'a samu ta'adi da ɓarna acikin
karatun naka kuwa.
Matsalar zata zamto mai sauki gareka idan ya zamto
daman ka riga ka koyi ilimin tajweedi kuma ka kware, kasan nau'in maddodi da
Qalqala da hukunce-hukuncen harrufa da siffofinsu da makharij da sauransu.
Shawarar da zan baka ita ce idan kasan kana da
ilimin tajweedi, kaci gaba da yin yadda kakeyi ɗin nan amma tare da bin shawarwarin wani Malami masanin
abin, koda ta hanyar yin waya dashi ne, kana tambayarsa abinda baka fahimta ba.
Idan kuma babu ilimin wannan fannin tare dakai, zaifi kyau ka hakura kaci gaba
da maimaita wuraren da ka karanta agaban Malamai, ka jira duk sanda ka dawo
gida Arewa ka koma wajen malamanka kaci gaba da dora karatun.
Allah shi Qara maka kokari da jajircewa, ya
sanyamu dukkanmu cikin ceton Alqur'ani mai girma.
WALLAHU A'ALAM.
DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.