HAƊA GWIWA WURIN LAYYA:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Hadisin Abu-Ayyub Al-Ansaariy (Radiyal Laahu Anhu) wanda An-Nasaa’iy da At-Tirmiziy da Ibn Maajah suka riwaito shi kuma Al-Albaaniy ya inganta shi cewa: A zamanin Annabi (Sallal Laahu Alalihi Wa Alihi Wa Sallam) mutum ɗaya yana yin layya da rago guda ɗaya ga kansa da iyalin gidansa. Da kuma wani audio clip na As-Shaikh Albaaniy Zaria (Rahimahul Laah) wanda yanzu yake yawo a cikin social media cewa: ‘Idan mutum ya ƙuduri aniyyar yanka wata dabba don yin layya shi da iyalinsa, to hukuncin layya ya hau kansa shi da iyalinsa. Tun daga farkon watan nan ba za su yi aski ko yanke ƙumba ba.’ Tambayata a nan ita ce: Hukuncin ya keɓanci rago ɗaya ko akuya ɗaya ce, ban da shanu ko raƙuma? Ko mutane biyu za su iya yin layyar da rago ko akuya ɗaya?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa
Barakaatuh.
Hadisin Sahabi Abu-Ayyuub shi ne wanda Al-Imaam
At-Tirmiziy (1587) ya riwaito da isnadinsa cewa: Ataa’u Bn Yasaar ya tambayi
Abu-Ayyuub Al-Ansaariy (Radiyal Laahu Anhu) ya ce: Yaya ya kasance ake yin
layya a zamanin Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)? Sai ya ce:
كَانَ الرَّجُلُ يُضَحِّى
بِالشَّاةِ عَنْهُ وَعَنْ أَهْلِ بَيْتِهِ فَيَأْكُلُونَ وَيُطْعِمُونَ حَتَّى تَبَاهَى
النَّاسُ فَصَارَتْ كَمَا تَرَى
Maigida ya kasance yana yin layya da rago ko
tunkiya guda ga kansa da iyalin gidansa, sai su ci kuma su ciyar da waɗansu, har ya kai mutane suna yin alfahari. Sai abin ya
koma kamar yadda kake gani.
At-Tirmiziy ya ce: ‘Wannan hadisin kyakkyawa ne
ingantacce… Waɗansu daga cikin malamai
sun yi aiki da wannan hadisin, shi ne maganar Ahmad da Is’haaq… Waɗansu malaman kuma cewa suka yi: Rago guda ba ya isuwa sai
dai ga mutum guda kaɗai. Wannan kuma
ita ce maganar Abdullaah Bn Al-Mubaarak da waninsa daga cikin malamai masana
ilimi.’
Daga wannan hadisi sahihi ana iya fahimtar cewa:
1. Rago guda ɗaya ya ishi maigida da iyalinsa a wurin layya. Haka ma raƙumi ko sa guda, idan
akwai wadata.
2. In akwai wadata mutum guda na iya yin layya da
raguna biyu ko sama da haka, kamar yadda yake iya yanka wa kowane daga cikin
iyalansa ragonsa na musamman.
3. Mutane biyu ko fiye ba su iya yin layya da rago
guda ɗaya, tun da ga shi har wasu malamai ma suna ganin rago ɗayan ba ya isuwa sai dai ga mutum guda kaɗai.
Sannan kuma Al-Imaam Muslim (1318) ya riwaito daga
Sahabi Jaabir Bn Abdillaah (Radiyal Laahu Anhumaa) ya ce:
« أَمَرَنَا رَسُولُ اللَّهِ
- صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَآلِهِ وَسَلَّمَ - أَنْ نَشْتَرِكَ فِى الإِبِلِ وَالْبَقَرِ
كُلُّ سَبْعَةٍ مِنَّا فِى بَدَنَةٍ »
Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa
Sallam) ya umurce mu da mu haɗa mutane bakwai
a cikin raƙumi guda ko
saniya guda.
Wannan ya nuna:
1. Kodayake wannan hadisi a kan hadaya ne ya zo
amma hukuncin ya shafi layya ma, tun da malamai sun yarda cewa babu bambancin
hukunci game da dabbobin da ake yankawa a cikinsu.
2. Mutane bakwai - tare da iyalansu - suna iya haɗa gwiwa a wurin layya da bijimin sa ko raƙumi guda ɗaya, ta yadda kowannensu zai tashi da subu’in (1/7)
naman.
3. Mutane ƙasa da bakwai - kamar biyar ko uku - suna iya haɗuwa su ma a cikin layya da raƙumi guda ɗaya ko sa guda ɗaya, tun da dai a asali ya halatta mutum guda mai hali ya
yi layya da sa ko raƙumi guda ɗaya.
Haka kuma hadisin Ummul-Mu’mineen Ummu-Salamah
(Radiyal Laahu Anhaa) da Al-Imaam Muslim (1977) ya riwaito cewa Annabi (Sallal
Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
« مَنْ كَانَ لَهُ ذِبْحٌ
يَذْبَحُهُ فَإِذَا أُهِلَّ هِلاَلُ ذِى الْحِجَّةِ فَلاَ يَأْخُذَنَّ مِنْ شَعْرِهِ
وَلاَ مِنْ أَظْفَارِهِ شَيْئًا حَتَّى يُضَحِّىَ »
Duk wanda yake da abin yankawa da zai yanka a
lokacin layya, to idan jinjirin watan Zul-Hijjah ya tsaya kar ya yanke wani abu
na gashin jikinsa ko ƙumbarsa har sai ya yi layyar.
Daga wannan hadisin da makamantansa ne malamai
suka gano cewa:
1. Wajibi ne ga duk wanda ke son yin layya ya rabu
da yanke wani abu da gashinsa ko ƙumbarsa tun daga ɗaya ga watan
Zul-Hijjah.
2. Idan mai layya bai ɗaura niyyar yin layyar ba sai a bayan watan ya shiga da
kwanaki, to hukuncin barin aski da yanke ƙumba gare shi yana farawa ne daga lokacin da ya ɗaura niyyar.
3. Idan ƙumbarsa ta karye ko kuma wani gashi ya tsiro masa a cikin ido wanda yake
cutuwa da shi, to ya halatta ya kawar da su, domin wannan a babin gusar da cuta
ne.
4. Idan wani mutum ya wuce iyakar shari’a, ya je
ya yanke waɗannan abubuwan da aka
hana, to ya yi zunubi kuma babu wata fidiya da zai yi, kuma wannan bai shafi
sahihancin layyarsa ba, idan dai an cika sharuɗɗanta.
5. Idan maigida zai shigar da iyalinsa a cikin
layyarsa, to ko dokar hana yanke gashi da ƙumba ya shafe su su ma? Malamai sun sha bamban: Waɗansu sun ce: E, domin su ma suna da hukuncin masu layyar
ce. Waɗansu kuma sun ce: A’a, domin hadisin bai ambace su ba.
Wal Laahu A’lam.
Sheikh Tambayad Abdullaah Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.