𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum dafatan malam yana cikin koshin lafiy Amin. malam ni tambayata ita ce yin sallah tahajjud a gida da yinta a masallaci wanne yafi falala?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
Salam Warahmatullahi Wabarkatuhu.
Acikin
Hadisin Abdullahi bn Sa'ad Ya ce “Na tambayi Manzon Allah Sallallahu alaihi
Wasallam akan sallar mutum tahajjud a gidansa da yinta a masallaci wanne yafi?
sai Annabi Sallallahu alaihi Wasallam yace “shin baka ganin gidana ba wanda
yafi shi kusa da masallaci, amma na yi sallah a gidana (tahajjud) ya fi na yi sallah
amasallaci sai dai sallar farilla” (Dubi Ibn Majah 1\39).
An karɓo daga Zaidu bn
Sabit (RA) daga Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam yana cewa “Sallar mutum
agidansa tafi sallarsa a masallacina. (wato masallacin Annabi). sai dai sallar
farilla”(Dubi Abu Dawud 1\9, taglikutta aliq 1/ 239 Nailal Audar 3\5 ko Ash shama,il
150).
Annabi
Sallallahu alaihi Wasallam Ya ce: “Mafificiyar sallarku (tahajjud) wacce kuka
yita a gidane sai dai sallar farilla kawai ”(Dubi Tirmizi Bisharhil Ahuz 2\00).
An ruwaito
acikin Bukhari mafificiyin sallar mutum a gidansane sai dai sallar Farilla
kawai.
(Dubi Fathul
Bary 3\0 ko Umdatul Qary.
Don haka yin
nafilar (tahajjud) a gida yafi yinta akowani masallaci falala. tunda Annabi
Sallallahu alaihi Wasallam yafifita nafila a gidaje a bisa masallacinsa.
Ananne
Hafizu bn hajar yake cewa: yin tahajjud agida lallai shi yafi falala ga al’umma
gaba ɗaya, domin shi ne
amsar da Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya baiwa mai tambaya, fatahul bary
juzu’I na 3 shafi na 25\6 Abu daud juzu’I na1 shafi na 69 Tajujjami’u juzu’I na
1 shafi na 332 Nailul Audhar juzu’Ina 3 shafi na 95 Tagliqutta’aliq juzu’I na 1
shafi 239 Ashshama’il shafi na 157
Amma duk da
haka rafkanannu acikin garuruwan kasannan (Nigeria) suna karfafa mata akan
fitowa masallaci da tsakar dare domin yin sallar Tahajjud. Alhali Annabi
Sallallahu alaihi Wasallam yace da ummu Humaidu Allah ya yarda da ita, yayin da
tazo gurin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam tace “ Ya Rasulullahi inaso
na yi sallah tare da kai” sai yace “Na sani kinaso kiyi sallah tare dani, amma
kiyi sallah a’yar kurin ɗakinki yafi kiyi sallah a falonki, kiyi sallah a tsakar
gidanki yafi kiyi sallah a masallacin mutanenki, kuma kiyi sallah a masallacin
mutanenki yafi kiyi sallah a masallacina wannan”.(Ahmad ne ya ruwaito 6\71 da
Ibn Khuzaima acikin sahihinsa 3\5 da Ibn Abdul Barri acikin Tamhid 23\98).
Wannan yana
nuna sallar mace ta farillah a cikin gidanta yafi ta yi a masallaci to yaya
kuma Nafila. Donhaka yin tahajjud a gida yafi yinta a masallaci a wajen mace ko
namiji.
WALLAHU
A'ALAM
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.